< 1 Samuel 17 >

1 Filistinnaw ni taran tuk hane ransanaw a pâkhueng teh Judah ram Sokoh kho dawk a kamkhueng awh teh Sokoh hoi Azekah a rahak Ephesdammin hmuen koe a tungpup awh.
To, fa, Filistiyawa suka tattara mayaƙansu suka haɗu a Soko cikin Yahuda domin yaƙi. Suka yi sansani a Efes-Dammim, tsakanin Soko da Azeka.
2 Sawl hoi Isarelnaw hmuen buet touh koe a kamkhueng awh teh Elah yawn dawk a tungpup awh teh, Filistinnaw tuk hanelah a kâcai awh.
Shawulu da Isra’ilawa suka taru suka yi sansani a Kwarin Ela suka ja dāgā don su yi yaƙi da Filistiyawa.
3 Filistinnaw teh avanglae mon dawk a kangdue awh teh, Isarelnaw teh avanglae mon dawk a kangdue awh, rahak dawkvah a yawn pui ao.
Filistiyawa suka zauna a tudu guda, Isra’ilawa kuma suka zauna a ɗaya tudun. Kwari yana a tsakaninsu.
4 Filistin ransa thung dawk hoi, Gath kho e Goliath a min kâphung e a tâco, a rasang e dong taruk touh hoi khap touh a pha.
Wani jarumin da ake kira Goliyat wanda ya fito daga Gat, ya fita daga sansanin Filistiyawa. Tsawonsa ya fi ƙafa tara.
5 Rahumluhuem a kâmuk teh Bahling angki a kho, hote angki teh rahum shekel 5000 tabang a ri.
Ya sa hular kwanon da aka yi da tagulla, da rigar ƙarfe mai sulke, nauyin rigar ya kai shekel dubu biyar.
6 A khokrangan dawk rahum a pada teh a loung hoi a loung rahak rahum tahroe a ka va.
A ƙafafunsa kuwa ya sa ƙarafar tagulla, rataye a bayansa kuma māshi ne na tagulla.
7 A tahroecung teh hni kawng kalawng e patetlah. Tahroe hmo teh shekel 600 tabang a ri teh, bahling ka sin e hah a hmalah a cei.
Ƙotar kibiyarsa kuwa kamar sandar saƙar igiya take, ƙarfen kibiyar kuma nauyinsa ya kai shekel ɗari shida. Mai riƙe masa garkuwa yana tafe a gabansa.
8 A kangdue teh Isarelnaw a hram sin. Bangdawkmaw taran hanelah, na tâco awh. Kai teh Filistin tami buet touh lah ka o. Nangmanaw teh Sawl e a san nahoehmaw, tami buet touh roi awh nateh kai koe tho sak awh.
Goliyat ya tsaya ya tā da murya wa hafsoshin Isra’ila ya ce, “Me ya sa kuka fito kuna layi don yaƙi? Ni ba Bafilistin ba ne? Ku kuma ba bayin Shawulu ba ne? Ku zaɓi waninku yă zo nan.
9 Ahni ni kai na tâ pawiteh nangmouh koe san lah ka o awh han. Ahni hah kai ni ka tâ lah ka thet pawiteh, ka san lah na o awh vaiteh kaimae thaw na tawk awh han telah atipouh.
In zai iya yin faɗa har yă kashe ni, to, za mu zama bayinku. Amma in na fi ƙarfinsa na kashe shi, to, sai ku zama bayinmu, ku kuma yi mana bauta.”
10 Filistin tami kai ni sahnin Isarel ransanaw na savek awh. Kai koe tami buet touh patoun awh. Kai hoi kâhmo roi han telah a ti.
Sai Bafilistin ya ce, “A wannan rana, na kalubalanci sojojin Isra’ila, ku ba ni mutum ɗaya mu yi faɗa.”
11 Sawl hoi Isarelnaw ni hote lawk a thai awh navah, pueng hoi a taki teh a pâyaw awh.
Da jin maganganun Bafilistin, sai Shawulu da dukan Isra’ila suka damu suka kuma ji tsoro.
12 Devit teh Judah ram, Bethlehem kho Jesi e capa doeh. Jesi ni capa a tawn e ataroe e doeh. Ahni teh a matawng poung toe.
To, Dawuda dai ɗan wani mutumin Efratawa ne mai suna Yesse, shi mutumin Betlehem ne a cikin Yahudiya. Yesse yana da yara maza takwas, a zamanin Shawulu kuwa, Yesse ya riga ya tsufa.
13 Jesi e a ca kacuenaw kathum touh teh Sawl e hnuk a kâbang awh. A capa kathum touh taran tuknae koe ka cet e a minnaw teh, kacuepoung e Eliab, apâhni e Abinadab, hoi apâthum e Shammah tinaw doeh.
Manyan’ya’yansa maza uku, sun bi Shawulu wajen yaƙi. Ɗansa na fari shi ne Eliyab, na biyu shi ne Abinadab, na uku kuwa shi ne Shamma.
14 Devit teh cahnoung poung e capa doeh. A capa kacue e kathum touh ni Sawl koe a kâbang awh ei,
Dawuda shi ne ɗan autansu. Manyan’yan mazan nan uku suka bi Shawulu.
15 Devit hateh Sawl koehoi Bethlehem kho koe lah a na pa e tu khoumnae koe atu hoi tu a cei.
Amma Dawuda yakan tafi sansanin Shawulu lokaci-lokaci yă kuma koma Betlehem don yă yi kiwon tumakin mahaifinsa.
16 Filistin tami ni amom tangmin ahnimouh koe a hnai pouh teh hnin 40 touh a kamnue pouh.
Kwana arba’in cif, Bafilistin nan ya yi ta fitowa kowane safe da kuma kowace yamma.
17 Jesi ni a capa Devit koevah atu na hmaunaw hanlah cai ephah buet touh, hete vaiyei 10 touh lat nateh na hmaunaw aonae koe lah karanglah cet haw.
Yesse ya ce wa ɗansa Dawuda, “Ka ɗauki wannan gasasshen hatsi da waɗannan curin burodi goma, ka kai wa’yan’uwanka a sansani da sauri.
18 Maito sanu kamkak e tueng 10 touh hai ransa 1, 000 kaukkung hanlah sin pouh. Na hmaunaw a dam hoi dam hoeh e na khet hnukkhu, ahnimouh koehoi hno buet buet touh sin la atipouh.
Ka haɗa da waɗannan cuku guda goma, ka kai wa komandan rundunarsu. Ka ga lafiyar’yan’uwanka, ka kawo mini labari daga wurinsu.
19 Sawl hoi Isarelnaw teh Elah yawn vah ao awh telah a ti.
Suna tare da Shawulu da kuma dukan mutanen Isra’ila a Kwarin Ela, suna can suna yaƙi da Filistiyawa.”
20 Devit amom a thaw teh, tunaw ka khoum hane tami buet touh koe a ceitakhai teh, Jesi ni kâ a poe e patetlah rawca a sin teh a cei. Isarel ransanaw taran tuk han a hramki awh lahun nah tungpup im koe a pha.
Kashegari da sassafe, Dawuda ya tashi ya bar tumakinsa wa wani yă lura da su, sai ya ɗauki kayansa, ya kama hanya kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya isa sansanin daidai sa’ad da rundunar tana fitowa zuwa bakin dāgā, suna kirarin yaƙi.
21 Isarel ransanaw hoi Filistin ransanaw teh a kâtuk awh hanelah rek a kâhnai awh.
Isra’ila da Filistiyawa suka ja dāgā suna fuskantar junansu.
22 Devit ni hno ka khen hane koe a kut dawk a poe teh ransa aonae koe lah a yawng teh, a hmaunaw hah kut a man.
Dawuda ya bar kayansa a wajen wani mai lura da kaya, sai ya ruga zuwa bakin dāgā yă gai da’yan’uwansa.
23 Ahnimouh hoi lawk a kâdei lahun nah Gath kho e Filistin tami Goliath teh Filistin ransanaw e hmalah hoi a tâco teh ouk a dei e patetlah lawk bout a dei e Devit ni a thai.
Da yana magana da su sai Goliyat, jarumin nan Bafilistin daga Gat ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya tā da murya kamar yadda ya saba. Dawuda kuwa ya ji shi.
24 Isarel ransanaw ni a hmu awh navah, a takipoung awh. Ahnie a hmalah hoi a yawng awh.
Da Isra’ilawa suka ga mutumin, sai dukansu suka gudu saboda tsananin tsoro.
25 Isarelnaw ni ka tâcawt e tami na hmu awh ou, Isarelnaw a savek hanelah a tho toe. Ahni ka thet e teh, siangpahrang ni moikapap e poehno hoi a bawi sak han. Hothloilah, a canu hai a poe han. Ahnie imthungnaw hai a ngai patetlah ao sak han.
Isra’ilawa suka yi ta cewa, “Kun ga yadda wannan mutum yana ta fitowa? Yana fitowa ne don yă kalubalanci Isra’ila. Sarki zai sāka wa mutumin da ya kashe wannan da dukiya mai yawa. Zai kuma ba shi’yarsa yă aura, yă cire suna mahaifinsa daga biyan kuɗin haraji cikin Isra’ila.”
26 Devit ni ateng kangdoutnaw koe, hete Filistin tami ka thet niteh, Isarelnaw min mathoenae kahawi sak e tami teh bangtelamaw sak hanelah ao han. Vuensom ka a hoeh e Filistin tami heh bangpatet e tami na maw, ka hring Cathut e ransa ka savek e tami nahoehmaw atipouh.
Dawuda ya tambayi mutanen da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilistin nan, ya kuma cire wannan kunya daga Isra’ila? Wane ne wannan bafilistin marar kaciya da yake kalubalantar rundunar yaƙi na Allah mai rai?”
27 Tami pueng ni, hete tami ka thet e teh ka dei awh e patetlah sak pouh han telah atipouh awh.
Sai suka sāke gaya masa abin da suka faɗa cewa, “Ga abin da zai faru da wanda ya kashe shi.”
28 Ahnimouh hoi Devit lawk a kâdei e hah kacuepoung e Eliab ni a thai nah, Devit koe a lung hmatara a khuek. Kahrawng e tu hah apimaw na khoum sak. Na kâoupnae na lung poannae na lungthin ka panue. Kâtuknae khet hane doeh na tho tie ka panue telah a ti.
Da wansa Eliyab, ya ji yana magana da mutanen, sai ransa ya ɓace ƙwarai saboda fushi, sai ya ce wa Dawuda, “Me ka zo yi a nan? Wa kuma ka bar wa’yan tumakin a jeji? Na san ka da taurinkai, da kuma mugun hali. Ka zo nan ne don ka yi kallon yaƙi kawai.”
29 Devit ni atu bangmaw ka sak, a lamthung kaawm nahoehmaw telah a ti.
Dawuda ya ce, “To, yanzu me na yi? Ba zan ma yi magana ba?”
30 Ahni koehoi alouklah a kangvawi takhai teh, ouk a dei patetlah bout a dei pouh.
Sai ya juya wajen wani kuma ya sāke kawo zancen, mutanen kuwa suka amsa masa kamar dā.
31 Devit ni a dei e lawk a thai awh teh, Sawl e hmalah a dei pouh awh nah, Devit hah a kaw.
Aka ji abin da Dawuda ya ce, aka kuwa gaya wa Shawulu, Shawulu kuma ya aika a kawo shi.
32 Devit ni Sawl koe ahni kecu dawk buet touh hai na lungpout sak hanh awh. Na san kai ni ka cei vaiteh hote Filistin tami ka tuk han telah a dei pouh.
Da Shawulu ya tambayi Dawuda, sai Dawuda ya ce masa, “Kada kowa yă damu saboda wannan Bafilistin. Bawanka zai je yă yi faɗa da shi.”
33 Sawl ni hote Filistin tami na tuk thai hane kawi lah awm hoeh. Nang teh na naw rah, ahni teh a nawca hoi tarantuk ka thoum e doeh telah Devit koe a dei pouh navah,
Shawulu ya ce, “Ba za ka iya yin faɗa da wannan Bafilistin ba, ya daɗe yana yaƙi, ya yi yaƙi tun yana saurayi. Ga shi kuwa kai ɗan yaro ne kawai.”
34 Devit ni Sawl koe tunaw na san kai ni ka khoum nah, sendek thoseh, tavom thoseh, a tho navah, tuhu dawk e tu a la navah,
Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Bawanka yana kiwon tumakin mahaifinsa. Sa’ad da zaki ko beyar ta zo ta kama tunkiya, ta tafi da ita.
35 Ka pâlei teh a pahni dawk e ka lawp, hahoi na cusin navah, a pâkhamuen dawk ka man pouh teh ka thei.
Nakan bi ta a baya in buga ta in kuma ƙwato tunkiyar daga bakinta. In kuma ta taso mini, nakan cafke ta a gashinta in buga ta in kashe.
36 Sendek hoi Tavom na san kai ni ka thei na maw, Cathut e ransanaw ka savek vuensom ka a hoeh e Filistin tami hai hote buet buet touh e patetlah han doeh atipouh.
Bawanka ya kashe zaki da beyar, wannan Bafilistin marar kaciya zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, domin ya rena rundunar Allah mai rai.
37 Sendek kut hoi tavom kut dawk hoi thoseh, kai na ka rungngang e BAWIPA ni hote Filistin kut dawk hoi hai na rungngang han doeh telah Devit ni bout a dei navah cet leih, Cathut teh nang hoi rei awm naseh telah Devit koe atipouh.
Ubangiji wanda ya cece ni daga kumbar zaki da kuma kumbar beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafilistin.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Je ka, Ubangiji yă kasance tare da kai.”
38 Sawl ni amae a puengcang a kho sak teh, a lû dawk rahumluhuem a kâmuk hnukkhu saiphei a kho sak.
Sai Shawulu ya kawo kayan yaƙinsa ya sa wa Dawuda. Ya sa masa hular kwanon da aka yi da tagulla a kansa, ya kuma sa masa rigar ƙarfensa.
39 Devit ni a angki van Sawl e tahloi a kava teh a cei bo teh, ouk a khohna boihoeh dawkvah, Sawl koe Devit ni ka cet thai mahoeh telah atipouh. Devit ni hot naw be a rading pouh.
Dawuda ya ɗaura māshin Shawulu a sulken, ya yi ƙoƙari yă zaga, sai ya ji ba zai iya ba saboda bai saba ba. Ya cewa Shawulu, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, domin ban saba ba.” Don haka ya tuɓe su.
40 Amae sonron hah a kut hoi a sin teh palang dawk e talung kâpica e 5 touh a rawi. Tu khoumnae koe a sin e yawngya dawk a pâseng. A kut dawk tâyai hoi Filistin tami teh a pâtam.
Sai ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya sa su a’yar jakarsa ta makiyaya; ya kuma ɗauki majajjawarsa, ya tafi, yă fuskanci Bafilistin.
41 Filistin tami ni a tho teh Devit koe lah rek a hnai. Ahnie hmalah bahling ka sin e hai ao.
Ana ciki haka, sai Bafilistin nan shi ma ya fita yana gusowa zuwa wurin Dawuda. Mai riƙe masa garkuwar yaƙi kuwa yana tafe a gabansa.
42 Filistin tami ni a khet navah, Devit a hmu teh sam palingvuek, a mei a hawi teh khet ahawi, camo lah ao dawk banglahai noutna hoeh.
Bafilistin ya dubi Dawuda daga sama har ƙasa, ya gan dai ɗan yaro ne kawai, kyakkyawa kuma mai ƙoshin lafiya, sai ya rena shi.
43 Hote Filistin tami ni, Devit koe kai ui lah maw ka tho teh, bongpai hoi khuet na tho sin vaw atipouh teh, Filistin tami ni a cathut noe lahoi Devit thoe a bo.
Ya ce masa, “Kana tsammani ni kare ne da za ka zo mini da sanda?” Sai ya la’anci Dawuda da sunayen allolin Filistiyawa.
44 Devit koevah kai koe tho haw, na moi hah kalvan e tava hoi kahrawng sarangnaw koe ka poe han telah bout a ti.
Ya ce, “Zo nan, ni kuwa zan ba da naman jikinka ga tsuntsayen sama da namun jeji su ci.”
45 Devit ni Filistin tami hanelah, kai koevah tahloi, tahroeca, tahroepui, hoi na tho, kai teh nang ni na savek e Isarel ransabawi Cathut, ransabawi Jehovah min hoi doeh nang koe ka tho.
Dawuda ya ce wa Bafilistin, “Kana zuwa ka yaƙe ni da māshi da takobi da kere, amma ni ina zuwa in yaƙe ka a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki, Allah na rundunar Isra’ila, wanda ka rena.
46 Cathut ni sahnin nang hah teh kaie kut dawk na poe e lah ao vaiteh, nang hah kai ni na thei hnukkhu na lû tâtueng han. Hahoi Filistin ransanaw e ro hah kalvan e tava hoi talai dawk e moithangnaw ka poe han. Isarelnaw koe Cathut ao tie talai van pueng ka panue sak han.
Yau nan, Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan kuwa kashe ka, in datse kanka. Yau, zan ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namun jeji, da haka duniya za tă sani lalle akwai Allah a cikin Isra’ila.
47 Hete tamihunaw ni hai BAWIPA ni tahloi hoi tahroe hoi na rungngang hoeh tie a panue awh han. Bangkongtetpawiteh, tarantuknae teh BAWIPA e doeh. Ama ni nangmanaw teh kaimae kut dawk na poe han telah a ti.
Duk waɗanda suka taru a nan za su san cewa ba da māshi ko takobi ne Ubangiji yake ceto ba, gama yaƙin nan na Ubangiji ne, shi kuwa zai bashe ku duka a hannuwanmu.”
48 Filistin tami teh a tho teh, Devit kâhmo hane rek a hnai nah, Devit ni Filistin tami kâhmo hane karanglah a yawng.
Yayinda Bafilistin yana matsowa kusa domin yă fāɗa wa Dawuda, sai Dawuda ya ruga a guje zuwa bakin dāgā don yă same shi.
49 Devit ni a yawngya thung a tapu teh, athung e talung buet touh a rasa hnukkhu tâyai hoi a yai teh, Filistin tami e tampa dawk a yai pouh. A tampa hlut ati teh talai dawk pakhup lah rawk a tabo.
Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
50 Hottelah, Devit ni tâyai hoi talung buet touh hoi hote Filistin tami a tâ teh a thei, a kut dawk tahloi sin hoeh.
Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara a kan Bafilistin. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba.
51 Devit ni a yawng sin teh, Filistin tami van a kangdue teh, ahnie tahloi tabu dawk e tahloi a rayu teh, a lahuen mon a tâtueng pouh. Filistinnaw ni a thakaawmpounge a due e a hmu awh torei teh, koung a yawng awh.
Dawuda ya ruga ya tsaya a bisan Bafilistin, ya zare takobin Bafilistin daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka juya suka gudu.
52 Isarel hoi Judah ransanaw a thaw awh teh, hram laihoi ayawn apout ditouh thoseh, Ekron longkha totouh thoseh, a pâlei awh. Hahoi Filistin tami thung dawk e a hmâ kacatnaw teh Shaaraim lam koehoi Gath hoi Ekron totouh a kamlei awh.
Mutanen Isra’ila da na Yahuda suka rugo gaba da babbar murya, suka fafari Filistiyawa har zuwa mashigin Gat da kuma ƙofofin Ekron. Gawawwakin Filistiyawa suka bazu a hanyar Sha’arayim zuwa Gat da kuma Ekron.
53 Isarelnaw teh Filistinnaw pâleinae koehoi bout a ban awh teh, ahnimae pupimnaw be a raphoe pouh awh.
Da Isra’ilawa suka komo daga bin Filistiyawa sai suka washe sansanin Filistiyawa.
54 Devit ni Filistin tami e a lû hah a la teh, Jerusalem kho totouh a sin. A puengcangnaw teh a rim dawk a hruek pouh.
Dawuda ya ɗauki kan Bafilistin zuwa Urushalima. Sai Dawuda ya ajiye kayan yaƙin Bafilistin a tentinsa.
55 Sawl ni Filistin tami tuk hanelah Devit a cei e a hmu navah, ransanaw kaukkung Abner koe, Abner hete nawsai heh apie capa maw telah a pacei. Abner ni oe siangpahrang na hring e patetlah kai ni ka panuek hoeh telah a ti.
Yayinda Shawulu yake kallon Dawuda sa’ad da za shi yă yaƙi Bafilistin, sai ya tambayi Abner, komandan rundunarsa ya ce, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya ce ran sarki yă daɗe, “Ban sani ba.”
56 Hottelah Siangpahrang ni hete camo heh api capa maw pacei haw, telah atipouh.
Sarki ya ce, “Ka tambaya mini ko yaron wane ne wannan saurayi.”
57 Hote Filistin tami a theinae koehoi Devit a tho nah Abner ni ahni hah a kaw teh, Sawl koe a ceikhai. Filistin tami e a lû a kut dawk a sin.
Dawuda yana dawowa daga karkashe Filistiyawa ke nan, sai Abner ya kai shi gaban Shawulu, riƙe da kan Bafilistin.
58 Sawl ni ahni koe thoundoun nang apie capa maw telah a pacei. Devit ni Bethlehem kho e na san Jesi capa telah a ti.
Sai Shawulu ya ce, “Kai ɗan wane ne, saurayi?” Dawuda ya ce, “Ni ɗan bawanka Yesse ne, na Betlehem.”

< 1 Samuel 17 >