< Mark 5 >

1 Chuti chun dil gal langkhat lama, Gerasene gam agalkai tauvin ahi.
Suka ƙetare tafkin suka je yankin Gerasenawa.
2 Konga pat Yeshua ahung potleh, lhan'a konin lhagaoboh vop khat'in ahung kimupin ahi.
Da Yesu ya sauka daga jirgin ruwa, sai wani mutum mai mugun ruhu ya fito daga kaburbura, ya tarye shi.
3 Ama chu lhanmol'a cheng ahin, koiman atuhtang joulou, thih khaova jong ahen joulou-u ahi.
Wannan mutumin ya mai da kaburbura gidansa. Kuma ba wanda ya iya daure shi, ko da sarƙa ma.
4 Bul atuhsah uva thih khaova jong ahen ji vang un thih khao chu asattan jin, bul chu atumkeh jin, koima chan abolngoi jou louhel ahitai.
Gama an sha daure shi hannu da ƙafa da sarƙa, amma yakan tsintsinke sarƙar, yă kuma karye ƙarafan da suke ƙafafunsa. Ba wanda yake da ƙarfin da zai iya yă riƙe shi.
5 Sunle jan in lhan mola chun aumin chule molchunga a-aole a-aolejin, songhem in ama aki-at chen jin ahi.
Dare da rana, sai yă dinga kuka yana ƙuƙƙuje jikinsa da duwatsu a cikin kaburbura da kan tuddai.
6 Gal a pat'in Yeshua ahin mun, ahung lhaijel in a-angah abohkhup in ahi.
Da ya hangi Yesu daga nesa, sai ya ruga da gudu, ya zo ya durƙusa a gabansa.
7 “Pathen chungnungpen Chapa Yeshua, ipi dinga neihung suhboi got ham? Pathen min'a nahenga katao ahi, neibolgim hih-in,” tin apeng jeng tai.
Ya yi ihu da babbar murya ya ce, “Ina ruwanka da ni Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ka rantse da Allah cewa ba za ka ba ni azaba ba!”
8 Hichun Yeshuan ajah-a, “Mipa-a kon chun hung potdoh in, nang lhagao boh,” tin ano tai.
Gama Yesu ya riga ya ce masa, “Ka fita daga jikin mutumin nan, kai mugun ruhu!”
9 Chuin, “Namin ipiham?” tia adohleh, aman adonbut in, “Tamtah kahi jeh'un kamin Janel ahi,” ati.
Sai Yesu ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa ya ce, “Sunana Lejiyon, wato, ‘Tuli,’ domin muna da yawa.”
10 Chuin chuche gamkai sunga kon'a nodoh ahilouna ding un Yeshua henga hataovin ataotan ahi.
Sai ya yi ta roƙon Yesu, kada yă kore su daga wurin.
11 Hiche mun lhang pang khat'a chu voh hon tamtah kilha-a ahi.
A kan tudun da yake nan kusa kuwa, akwai wani babban garken aladu, suna kiwo.
12 Janelte chun, “Voh hon lah-a kaluttheina ding un neisol un,” tin athum tauve.
Sai aljanun suka roƙi Yesu, suka ce, “Tura mu cikin aladun nan, ka bari mu shiga cikinsu.”
13 Yeshuan jong aphalpeh tan, lhagaoboh ho chu ahung potdoh-un vohcha ho sunga chun alut tauvin, hichun vohcha sangni jen chu halhaiyin alhaiyun, kol ah alhai lhauvin dil ah alhalut'un, twi lah-a chun alhumgam tauvin ahi.
Ya kuwa yarda musu, sai mugayen ruhohin suka fita suka shiga cikin aladun. Garken kuwa, yana da kusan aladu dubu biyu, suka gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, suka nutse.
14 Chuin ganching ho chu ajam un, khopi sung le loujaovah athu chu aseile tauvin ahi. Mipi chun ipi tidan hitam tin ave dingin ahung lhaipheiyun ahi.
Masu kiwon aladun kuwa suka ruga da gudu zuwa cikin gari da ƙauyuka, suka ba da wannan labari. Sai mutanen suka fito, domin su ga abin da ya faru.
15 Chuin Yeshua kom ahung lhun un, thilha Janel voppa chun pon akisila chule lunglima anatou chu amuvin akicha lheh jeng uve.
Da suka kai wajen Yesu, sai suka ga mutumin da dā yake da tulin aljanun yana zaune a wurin, sanye da tufafi kuma cikin hankalinsa, sai suka ji tsoro.
16 Chuin thilha voppa leh vohcha ho umchan achen achaiya mua hetoh hon thil umje chu aseipeh tauve.
Waɗanda suka ga abin da ya faru, suka ba da labarin abin da ya faru da mai aljanun, da kuma aladun.
17 Hichun amahon Yeshua chu agamsung uva kon'a potdoh ding in ahenga atao uvin ahi.
Sai mutane suka fara roƙon Yesu yă bar yankinsu.
18 Chuin konga alut konin masanga thilha voppa chun ama toh kilhon khom dingin angeh tai.
Yesu yana kan shiga cikin jirgin ruwa ke nan, sai mutumin da dā yake da aljanun ya roƙa yă bi shi.
19 Ahivang in Yeshuan ajadan ajah a, “Na in a chen lang nain kote henga Pakaiyin itobang thil loupi nabolpeh a, iti nakhoto'em abonchan gaseitan,” atipeh tai.
Yesu bai yardar masa ba, amma ya ce, “Ka tafi gida wurin iyalinka, ka gaya musu babban alherin da Ubangiji ya yi maka, da yadda ya yi maka jinƙai.”
20 Chuin amapa chu akipatdoh in Decapolis (Khopi som) jousea Yeshuan thil lentah abolpeh chu lhangphong tah'in aseile pantai. Mijousen kidang asa lheh jeng un ahi.
Sai mutumin ya tafi, ya yi ta ba da labari a cikin Dekafolis a kan babban alherin da Yesu ya yi masa. Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
21 Chuin Yeshua konga akitol in agal langkhat alhung in, hiachun mi honpi tamtah ahenga ahung kikhom un ahi.
Da Yesu ya sāke ƙetarewa cikin jirgin ruwa zuwa ɗaya hayen tafkin, sai taro mai yawa ya taru kewaye da shi yayinda yake a bakin tafkin.
22 Hichun kikhopna in'a vaipo holah-a mi khat, amin Jairus chu ahung in, Yeshua amu phat in akengbulah abohkhup in,
Sai ɗaya a cikin masu mulkin majami’a, wanda ake kira Yayirus ya zo wurin. Da ganin Yesu, sai ya durƙusa a gabansa,
23 “Kachanu khangdongcha thiding dinmun'in aumtan, lungset in hung in lang achunga nakhut hung ngam in lang, ahinna ding in neijen dampeh-in,” tin ahung taove.
ya roƙe shi da gaske ya ce, “Ƙaramar diyata tana bakin mutuwa. In ka yarda, ka zo ka ɗibiya hannunka a kanta, domin ta warke, ta kuma rayu.”
24 Chuin Ama chutoh akilhon pheiyin, mi honpin jong ahin juiyun, atom lellul jeng un ahi.
Sai Yesu ya tafi tare da shi. Babban taron kuma ya bi shi, suna ta matsinsa a kowane gefe.
25 Hikahlah chun numei khat jong kumsom le kumni athi longa damlou aum in ahi.
A can kuwa akwai wata mace, wadda ta yi shekaru goma sha biyu tana zub da jini.
26 Louthem tamtah akivetsahna-a sum le pai anei jouse sumang jouva ahitan, imala phachom louvin khoh chehcheh a um ahi.
Ta kuma sha wahala ƙwarai a hannun likitoci da yawa, har ta kashe duk abin da take da shi, amma maimakon samun sauƙi, sai ciwon ya ƙara muni.
27 Amanu chun Yeshua thudol anajan, hijeh chun mi honpi lah achun ahung in Yeshua pon mong chu ahung tham tai.
Da ta ji labarin Yesu, sai ta zo ta bayansa, a cikin taron, ta taɓa rigarsa,
28 Amanu chu aki ngaiton, “Apon jengjong hi thamleng dam nange,” ti atahsan ahi.
domin ta yi tunani cewa, “Ko da rigunarsa ma na taɓa, zan warke.”
29 Chomloukah'in athiput chu akang in atang jeng tan, anat thoh lel a kon aol leh adamdoh dan chu atichunga akihettan ahi.
Nan da take, zub da jininta ya tsaya, sai ta ji a jikinta ta rabu da shan wahalarta.
30 Chutah chun Yeshuan atichunga kon'a amidamsahna tha apotdoh chu akihet in, hichun mipi lah-a chun akihei kimvelin, “Kapon thama chu koiham?” tin adongtai.
Nan da nan Yesu ya gane cewa, iko ya fita daga gare shi. Sai ya juya a cikin taron ya yi tambaya, “Wa ya taɓa rigata?”
31 Aseijuiten ajah-a, “Mipi hijat'in naneh le jeng uva, itidan'a, ‘Koiham eithama?’ tia dohna nabol ham?” atiuvin ahi.
Sai almajiransa suka ce, “Kana ganin mutane suna matsinka, duk da haka kana tambaya, ‘Wa ya taɓa ni?’”
32 Hinlah Aman chuche bol a chu mudohna dingin avelen ahi.
Amma Yesu ya ci gaba da dubawa don yă ga wa ya taɓa shi.
33 Amanu chun achunga thilsoh chu ahen, kicha sasan kihot pum in ahung in a-angah abohkhup in, ama ahi akiseidohtai.
Matar, da yake ta san abin da ya faru da ita, sai ta zo ta durƙusa a gabansa, da tsoro da rawan jiki, ta kuma gaya masa dukan abin da ya faru.
34 Chuin Yeshuan ajah a, “Boinu, natahsan in nadamsah ahitai. Lungmong in chetan. Na thohnatna chu kichai ahitai,” ati.
Sai ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya, kin kuma rabu da dukan wahalarki.”
35 Amanu koma thu asei jinglaiyin, thupole khat Jairus in'a konin ahung in, “Nachanu athitai. Houhil hi kisahboisah ngaitaponte,” tin Jairus komah ahung seiye.
Yayinda Yesu yana cikin magana, sai waɗansu mutane daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’a, suka zo suka ce, “Diyarka ta rasu. Kada ma ka wahal da Malam.”
36 Aki hounau chu Yeshuan ajatan, Jairus koma chun, “Kicha hih-in, tahsan poupoutan,” ati.
Yesu bai kula da abin da suka faɗa ba, sai ya ce wa mai mulkin majami’ar, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata kawai.”
37 Chuin Peter, James le John (James naopa), hicheng tailou midang koiman ajuiding ajadan akijuisah poi.
Bai bar kowa ya bi shi ba, sai Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub.
38 Kikhopna in vaihompa, Jairus in alhun'u chun, mihonpi chu anapoh cheichoi jeng un, kap le maova aum'u chu Yeshuan amun ahi.
Da suka iso gidan mai mulkin majami’ar, sai Yesu ya ga ana hayaniya, mutane suna kuka da kururuwa.
39 Chuin ama alut'in ajah uva, “Ibola hitia hi napo cheichoiyuva nakau ham? Chapangnu chu athi ahipoi, aihmu ahibouve,” ati.
Sai ya shiga ciki, ya ce musu, “Mene ne dalilin wannan hayaniya da kuka? Yarinyar ba mutuwa ne ta yi ba, barci take yi.”
40 Thi op mi honpi chun anuisat uve. Hichun aboncha uvin asoldohsoh in, chapangnu nu le pa toh chule ahin kilhonpi seijui thum ho chengsetoh chapangnu umna'a chun alut un ahi.
Sai suka yi masa dariya. Bayan ya fitar da su duk waje, sai ya ɗauki mahaifin da mahaifiyar yarinyar tare da almajiran da suke tare da shi, suka shiga inda yarinyar take.
41 Chuin chapangnu khut chu atuh in, “Talitha koum,” atin ahi. Hichu “Boinu, kithouvin!” tina ahi.
Sai ya kama hannunta ya ce mata, “Talita kum!” (Wato, “Ƙaramar yarinya, na ce miki, tashi!”).
42 Chupettah chun chapangnu chu ahung thouvin, ading in lam ajotpai jeng tai. Amanu chu kum som le ni bou ahina laiye. Chutah chun amaho chun kidang asa lheh jeng un.
Nan da nan, sai yarinyar ta tashi ta yi tafiya (shekarunta goma sha biyu ne). Saboda wannan, suka yi mamaki ƙwarai.
43 Hiche thuhi koima ahetsah louna diuvin Yeshuan akhamgah in, chule amanun aneh ding an apeh diuvin thu apen ahi.
Sai ya ba da umarni mai tsanani, kada kowa yă san kome game da wannan. Sai ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.

< Mark 5 >