< Joba 8 >

1 Shuhi Bildad loh a doo tih,
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 “He he me hil nim na thui ve? Na ka kah ol tah khohli bangla khuet coeng.
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Pathen loh tiktamnah he a khun sak tih Tlungthang loh duengnah te a khun sak mai a?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 Na ca rhoek te anih taengah a tholh vaengah amih te amamih kah boekoek kut dongla a tueih.
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 Namah loh Pathen te na toem tih Tlungthang te na hloep mak atah,
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 Na cil tih na thuem koinih nang yueng la haenghang vetih na duengnah rhamtlim te n'thuung pataeng pawn ni.
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 Na tongnah te a yiit om cakhaw na hmailong te muep rhoeng ni.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 Lamhma kah cadil taengah dawt laeh lamtah a napa rhoek khenah te soepsoei laeh.
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 Mamih loh n'hlaem paek kah long khaw m'ming uh moenih, mamih kah khohnin diklai dongkah mueihlip banghui ni.
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 Amih te na thuinuet pawt tih a, nang taengah a thui vetih amih kah lungbuei lamloh olthui te a khueh eh?
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 Nongtui pawt ah talik thawn tih tui om mueh ah capu rhoeng a?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 Te te a duei pueng ah a hlaek pawt akhaw sulrham boeih hmai ah rhae coeng.
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 Pathen aka hnilh boeih kah caehlong neh lailak kah ngaiuepnah tah bing tangloeng.
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 A uepnah neh a pangtungnah bumba im te khaw bawtboeng.
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 A im dongah hangdang dae pai thai pawh. Te te a kuel dae thoo pawh.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 Anih te khosae li ah thingsup tih a dum ah a dawn sai.
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 A yung loh lungkuk dongah a ven tih lungto im te a hmuh.
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 Te te a hmuen lamloh a phuk van vaengah, “Nang kam hmu moenih,” anih te a namnah.
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 He he a longpuei kah omthennah coeng koinih laipi tloe lamloh a poe uh khaming.
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 Pathen loh cuemthuek hnawt ngawn pawt tih thaehuet kut te a moem moenih.
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 Na ka dongah nueihbu neh na hmui dongah tamlung bae.
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 Na lunguet rhoek loh yahpohnah a bai uh vetih halang kah dap tah om mahpawh,” a ti.
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”

< Joba 8 >