< Joba 38 >
1 BOEIPA loh Job te hlipuei khui lamloh a doo tih,
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2 Mingnah aka tal olthui neh cilsuep aka hmuep sak te unim?
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3 Hlang bangla na pumpu yen lamtah nang kan dawt bangla kai he n'tueng laeh.
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4 Diklai ka suen vaengah melam na om? Yakmingnah na ming atah thui lah.
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5 U loh a khodang a khueh khaw na ming van nim? A soah rhilam aka yueng khaw unim?
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6 A buenhol te me dongah nim a buen tih, a bangkil lung te unim aka thuinuet?
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7 Mincang aisi rhoek rhenten tamhoe uh tih Pathen ca rhoek boeih yuhui uh.
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8 Tuitunli te a bung lamloh a poh tih a coe vaengah thohkhaih neh a tlaeng.
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9 Kai loh cingmai kah a pueinak neh anih kah yinnah hni khaw ka khueh pah.
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10 Ka oltlueh he anih ham ka tlueh pah tih thohkalh neh thohkhaih khaw ka khueh pah.
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11 He hil ka ti vaengah ha mop lamtah koei boeh. Na hoemdamnah tuiphu te he ah he khueh laeh.
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
12 Namah tue vaengah mincang ke na uen a? Khothaih ke na ming tih amah hmuen ah khothaih a om khaw na ming.
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13 Te lamkah halang rhoek khoek ham neh diklai hmoi a tuuk sak ham khaw.
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14 Dikpo kutbuen bangla poehlip tih pueinak bangla pai.
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15 Halang rhoek te amamih kah vangnah a hloh pah tih ban a thueng khaw a tlawt sak.
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
16 Tuitunli kah tuiput la na pawk tih tuidung kah khenah dongah na pongpa vai a?
“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
17 Nang taengah dueknah vongka rhoek ah uh tih dueknah hlipkhup vongka te na hmuh a?
Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
18 Diklai hmuenka duela na yakming nim? A cungkuem la na ming atah thui lah.
Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
19 Vangnah aka om longpuei he menim? Hmaisuep kah a hmuen he melae?
“Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
20 Te te amah khorhi la na thak van tih a im kah a hawn khaw na yakming van nim?
Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
21 Nang n'sak tih na khohnin kah a tarhing a puh daengah ni na ming pueng.
Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
22 Vuelsong thakvoh khuila na kun tih rhaelnu thakvoh na hmuh a?
“Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
23 Te te rhal tue vaengkah ham khaw, caemrhal neh caemtloek tue vaengkah ham khaw ka tuem pueng.
waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
24 Diklai ah kanghawn loh a taekyak tih, vangnah loh a tael longpuei te menim?
Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
25 Tuilong lungpook ham neh rhaek ol ham longpuei aka tael te unim?
Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
26 A khuiah tongpa aka om pawh khosoek neh hlang aka tal khohmuen ah khaw rhotui aka tlan sak la,
don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
27 khohli rhamrhael neh imrhong aka hah sak la, toitlim annoe aka poe sak la om coeng.
don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
28 Khotlan te a napa om a? Buemtui tuicip te ulong a sak?
Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
29 Rhaelnu he u kah bungko lamkah nim a thoeng tih, vaan vueltling te ulong a sak?
Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
30 Tui khaw lungto bangla thuh uh tih tuidung hman ah khal.
lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
31 Airhitbom kah omngaih omloe te na hlaengtang tih buhol phueihrhui khaw na hlawt thai aya?
“Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
32 Mazzaroth aisi te amah tue vaengah na thoeng sak tih Ayish aisi te a ca rhoek neh na mawt a?
Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
33 Vaan kah khosing te na ming atah amah kah laithuithainah te diklai ah na khueh a?
Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
34 Na ol te khomai dongla na huel thai tih tuili tui te na khuk thai a?
“Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
35 Rhaek na tueih vaengah cet uh tih nang taengah, “Kaimih la he,” a ti uh a?
Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
36 Kodang khuila cueihnah aka khueh te unim? Kopoek khuiah yakmingnah aka pae te unim?
Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
37 Cueihnah neh khomong aka tae te unim? Vaan tuitang aka thael te unim?
Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
38 Me vaengah lae Laipi a hlawn la a hlom tih dikmuh a man sak?
sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
39 sathuengnu hamla maeh na mae pah tih sathuengca kah hingnah na tom pah a?
“Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
40 Me vaengah lae a khuisaek ah a ngam uh tih thingpuep khui ah a kol uh?
Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
41 A sakah te vangak ham aka tawn pah te unim? A camoe, a camoe uh vaengah tah Pathen taengah bomnah a bih uh dae caak mueh la kho a hmang uh.
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?