< Jeremiah 32 >
1 Judah manghai Zedekiah kah a kum, kum rha dongah BOEIPA taeng lamkah ol te Jeremiah taengla ha pawk. Te vaengah Nebukhanezar kah a kum tah kum hlai rhet lo coeng.
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
2 Te vaengah Babylon manghai tatthai rhoek loh Jerusalem te a dum uh coeng. Tonghma Jeremiah khaw Judah manghai im kah vongup thongim ah a khoh tih om coeng.
Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
3 Judah manghai Zedekiah loh, “'BOEIPA loh he khopuei he Babylon manghai kut ah ka paek coeng tih a tuuk pawn ni.
Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
4 Tedae Judah manghai Zedekiah he Khalden kut lamloh poenghal mahpawh. Babylon manghai kut ah a paek rhoe a paek rhoe ni. Te vaengah a ka neh a ka voek uh rhoi vetih a mik rhoi khaw a mik, mik ah so uh rhoi bitni.
Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
5 Zedekiah te Babylon loh a khuen vetih kai n'hip hlan duela pahoi om ni. He tah BOEIPA kah olphong ni. Khalden te na vathoh thil akhaw na thaihtak mahpawh,’ a ti,” tila thui ham nim na tonghma?” a ti nah tih a khoh.
Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
6 Te vaengah Jeremiah loh, “BOEIPA ol kai taengla ha pawk tih,
Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
7 “Na panoe Shallum capa Hanamel te na taengla ha pawk coeng te. Anathoth kah kai khohmuen te namah ham lai laeh. Lai ham tlannah khaw namah kah hamsum ni, ' a ti ni,” a ti.
Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
8 BOEIPA ol bangla ka panoe capa Hanamel te kai taengah thongim vongup la ha pawk. Te phoeiah kamah te, “Benjamin khohmuen, Anathoth kah kai khohmuen te lai laeh. Rho kah hamsum khaw namah coeng tih tlannah khaw namah kah ni, namah ham lai laeh. Te dongah he tah BOEIPA ol ni tila ka ming,” a ti.
“Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
9 Te dongah ka panoe capa Hanamel taeng lamkah khohmuen Anathoth kah te ka lai pah. Anih ham tangka la ngun te shekel hlai rhih ka thuek pah.
saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
10 Cabu dongah khaw ka daek tih kutnoek ka daeng. Laipai te ka laipai sak phoeiah ni tangka te cooi dongah ka khiing pah.
Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
11 Olpaek neh oltlueh a daeng thil tih a rha, lainah cabu te ka loh.
Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
12 Te phoeiah lainah cabu te ka panoe capa Hanamel mikhmuh neh lainah cabu dongah aka daek laipai kah mikhmuh neh, thongim vongup kah aka ngol Judah pum kah mikhmuh ah Maaseiah koca Neriah capa Barukh taengah ka paek.
na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
13 Barukh te amih mikhmuh ah ka uen tih,
“A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
14 “He tah Israel Pathen caempuei BOEIPA long ni a thui. He cabu he lainah cabu la khuen laeh. Kutnoek a daeng neh a rha cabu te khaw lai am khuiah khueh. Te daengah ni kum a sen a kuei eh.
‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
15 He tah Israel Pathen caempuei BOEIPA long ni a thui. He diklai kah im khaw, khohmuen khaw, misur khaw koep a lai uh ni,” ka ti nah.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
16 Te phoeiah BOEIPA taengla ka thangthui tih lainah cabu te Neriah capa Barukh taengah ka paek.
“Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
17 Te vaengah, “Ya-oe ka Boeipa Yahovah, namah loh vaan neh diklai he na saii ne. Na thadueng tanglue neh na ban na lam tih namah ham tah ol boeih he khobaerhambae voel moenih.
“A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
18 A thawng thawng taengah sitlohnah na saii dae pa rhoek kathaesainah te amih hnukah a ca rhoek rhang dongah khaw a thuung. Tanglue neh hlangrhalh Pathen tah a ming caempuei Yahweh ni.
Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
19 cilsuep khaw tanglue tih na bibi khaw cungkuem pai. Na mik loh hlang ca rhoe kah longpuei boeih te a sawt tih hlang boeih te a longpuei tarhing neh a khoboe kah a thaih tarhing ah na paek.
manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
20 Egypt kho ah miknoek neh kopoekrhai khaw na khueh. Te khohnin kah te Israel khui neh hlang taengah khaw tahae khohnin kah bangla namah ming ham ni na saii.
Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
21 Na pilnam Israel te Egypt kho lamloh miknoek neh, kopoekrhai neh, tlungluen kut neh na khuen. Na ban nen khaw mueipuelnah la muep na thueng thil.
Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
22 Suktui neh khoitui aka pha khohmuen he amih taengah paek ham a napa rhoek taengah na toemngam bangla he khohmuen he amih taengah ni na paek.
Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
23 Ha pawk uh tih he he a pang uh vaengah na ol te hnatun uh pawh. Na olkhueng te khaw na olkhueng bangla vai uh pawt tih amih taengah saii ham na uen boeih te saii uh pawh. Te dongah ni he kah yoethae cungkuem he amih taengah na thoeng sak.
Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
24 Khopuei amah loh ham tanglung la ha pawk uh coeng ke. Te dongah khopuei he amah aka vathoh thil Khalden kut dongah a paek coeng. cunghang neh, khokha neh, duektahaw na thui te khaw thoeng tih na hmuh coeng he.
“Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
25 Boeipa Yahovah namah loh kai taengah, “Khopuei he Khalden kut ah pae mai cakhaw khohmuen he tangka neh namah ham lai lamtah laipai te laipai sak na ti,” a ti nah.
Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
26 Te vaengah BOEIPA ol te Jeremiah taengah ha pawk tih,
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
27 “Kai tah pumsa boeih kah BOEIPA Pathen ni he, hno boeih he kai ham khobaerhambae a?” a ti nah.
“Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
28 Te dongah BOEIPA loh he ni a thui. He khopuei he Khalden kut neh Babylon manghai Nebukhanezar kut ah ka tloeng coeng tih a khaih pawn ni he.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
29 He khopuei aka vathoh thil Khalden rhoek ha pawk uh vetih he khopuei he hmai neh a hlup ni. Te vaengah kai veet ham Baal taeng neh pathen taengah tuisi a bueih uh tih a imphu ah a phum te im neh a hoeh pah ni.
Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
30 Israel ca neh Judah ca khaw ana om van tih a camoe lamloh ka mikhmuh ah boethae ni a saii uh. Israel ca ngawn long khaw a kut dongkah bisai neh kai m'veet uh. He tah BOEIPA kah olphong ni.
“Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
31 He khopuei he ka thintoek ham neh ka khosi ham khaw ka taengah om ngawn coeng. A thoong uh khohnin lamloh tahae khohnin duela ka mikhmuh lamloh a khoe rhoe coeng.
Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
32 Israel ca rhoek neh Judah ca rhoek, amih kah a manghai rhoek neh a mangpa rhoek, a khosoih rhoek neh a tonghma, Judah hlang neh Jerusalem khosa loh boethae a saii boeih te kai ni m'veet uh.
Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
33 Kai taengla a rhawn a koh uh tih a maelhmai then pawh. Te vaengah amih tukkil ham he a thoh neh a tukkil akhaw thuituennah doe ham a hnatun uh moenih.
Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
34 Im ah a sarhingkoi te a khueh uh tih a poeih ham te kai ming a khue thiluh.
Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
35 A canu neh a capa te Molek taengah paan sak ham kolrhawk ah Baal hmuensang te a thoh uh. Te tueilaehkoi te saii ham amih ka uen pawt tih ka lungbuei khaw a paan moenih. Te dongah Judah he tholh rhoela tholh.
Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
36 Tedae he khopuei kawng tah Israel Pathen BOEIPA loh a thui tangloeng coeng he. Te ni nangmih khaw, 'Babylon manghai kut dongah cunghang neh, khokha neh, duektahaw neh a thak ni, ' a ti te.
“Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
37 Kai loh amih te diklai pum lamkah ka coi coeng he. Ka thintoek ah, ka kosi neh ka thinhul bat ah ni te lam te amih ka heh. Tedae amih te he hmuen la kam mael puei vetih ngaikhuek la kho ka sak sak ni.
tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
38 Kamah taengah pilnam la om uh vetih kai khaw amih taengah Pathen la ka om uh ni.
Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
39 Te vaengah amih te lungbuei pakhat neh longpuei pakhat ni ka paek eh. Te daengah ni hnin takuem ah kai he n'rhih uh vetih amamih ham neh amih hnukkah a ca rhoek ham khaw a then eh.
Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
40 Amih taengah kumhal kah paipi te ka saii vetih amih taengah ka voelphoen ham khaw amih taeng lamloh ka paa mahpawh. Kai hinyahnah te amih thinko ah ka khueh daengah kai taeng lamloh a nong uh pawt eh.
Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
41 Amih taengah voelphoeng ham te amih soah ka ngaingaih ni. Amih te he khohmuen ah ka lungbuei boeih, ka hinglu boeih neh oltak dongah ka phung ni.
Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
42 BOEIPA loh he ni a thui. He pilnam soah he yoethae tanglue a cungkuem ka thoeng sak bangla amih taengah hnothen a cungkuem la ka thui te amih taengah ka thoeng sak van.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
43 He kah kho ah khohmuen he koep a lai ni. Te ni nangmih loh, 'Hlang neh rhamsa aka om pawh khopong te Khalden kut dongah a paek,’ na ti uh.
Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
44 Khohmuen te tangka neh a lai uh vetih cabu dongah daek ham neh kutnoek daeng ham khaw Jerusalem kaepvai ah, Judah khopuei ah, tlang kah khopuei ah, kolrhawk khopuei ah, tuithim khopuei ah, Benjamin kho ah laipai te a a laipai sak ni. Amih khuikah thongtla te ka mael puei ni. He tah BOEIPA kah olphong ni.
Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”