< Isaiah 49 >
1 Sanglak rhoek loh kamah taengkah he hnatun uh saeh lamtah khohla lamkah namtu rhoek loh hnatung uh saeh. BOEIPA loh kai he bungko khuiah ng'khue coeng tih a nu bung khuiah ni ka ming a sum coeng.
Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
2 Ka ka he cunghang haat bangla a khueh tih a kut dongkah hlipkhup ah kai n'thuh. Kai he thaltang la n'khueh tih amah kah liva dongah a meet tangtae la kai n'thuh.
Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
3 Kai taengah tah, “Kamah kah sal tah Israel nang, namah dongah ni ka ko ka hang eh.
Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
4 Tedae kai loh a poeyoek la ka ti coeng. A hinghong la ka kohnue tih ka thadueng khaw a honghi coeng. Ka tiktamnah he BOEIPA taengah, ka thaphu te ka Pathen taengah ka bawt.
Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
5 Bungko khui lamloh amah kah sal la kai aka hlinsai BOEIPA loh Jakob te amah taengla mael sak ham neh Israel te amah taengla coi ham te a thui coeng. Te dongah BOEIPA mikhmuh ah ka thangpom uh tih ka Pathen tah ka sarhi la om.
Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
6 Jakob koca te thoh ham neh Israel a kueinah tih mael puei ham khaw kamah kah sal la na om te rhaemaih. Nang tah diklai khobawt duela kamah kah khangnah a om sak ham neh namtom rhoek kah vangnah la kang khueh ni,” a ti.
ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
7 Israel aka tlan tih anih kah a cim Yahovah loh hinglu kah a hnaep taengah, namtom kah a tuei taengah, aka taemrhai rhoek kah sal taengah, “Manghai rhoek loh a hmuh uh vaengah mangpa rhoek khaw thoo uh vetih a bawk uh bitni. Israel kah a cim BOEIPA tah a uepom dongah ni nang n'coelh.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
8 BOEIPA loh, “Kolonah tue vaengah nang kan doo tih khangnah khohnin ah nang kan bom. Nang te kang kueinah vetih aka pong tangtae khohmuen aka thoh ham neh rho aka pang pilnam patai la nang te kang khueh ni.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
9 Amih hmaisuep ah a khih rhoek te, 'Ha pawk uh lamtah ha mop uh,’ ti nah. Longpuei ah luem uh vetih caphoei cuk boeih te amih kah rhamtlim la poeh ni.
don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
10 Lamlum uh pawt vetih halthi uh mahpawh. Amih te unghae neh khomik loh do mahpawh. Amih aka haidam loh amih te a hmaithawn vetih tuisih tui taengla a khool ni.
Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
11 Kamah kah tlang boeih te long la ka khueh vetih ka longpuei te ka pomsang ni.
Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
12 Khohla lamkah rhoek te ha pawk uh ni ke. Tlangpuei lamkah rhoek neh tuitun lamkah ke khaw, Sinim kho lamkah rhoek khaw.
Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
13 Vaan rhoek loh tamhoe uh lamtah diklai khaw omngaih saeh. Tlang rhoek khaw tamlung neh rhong la rhong uh saeh. BOEIPA loh a pilnam te a hloep tih mangdaeng rhoek te a haidam coeng.
Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
14 Zion loh, “Yahovah loh kai n'hnoo tih ka Boeipa loh kai n'hnilh coeng,” a ti.
Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
15 Huta loh a ca cahni te a hnilh a? A bungko khuikah a ca te a haidam ta. Te rhoek loh hnilh uh mai cakhaw kai long he nang kan hnilh mahpawh.
“Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
16 Kutpha dongah nang kan tarhit coeng tih na vongtung khaw kamah hmaiah om yoeyah coeng he.
Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
17 Na ca rhoek loh namah n'koengloeng uh paitok tih namah lamkah aka thoeng rhoek loh nang n'khah uh.
’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
18 Na mik te huel kilkoel lamtah hmu van lah. Amih te boeih coi uh thae tih nang taengla ha pawk uh coeng. Kai, hingnah BOEIPA kah olphong ni. Amih boeih te kamrhui bangla na vah vetih na langa bangla na hlaengtang ni.
Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
19 Namah kah imrhong neh na ponah kho na pong sak. Khosa taeng lamloh n'daengdaeh pawn vetih nang aka yoop rhoek khaw lakhla uh bitni.
“Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
20 Nang hlangmoeng ca rhoek na hna khuiah, “Kai ham a hmuen caek coeng tih kamah ham han thoeih lamtah kho ka sa eh?,” a ti uh ni.
’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
21 Te vaengah na thinko nen tah, “Kai aka cun te unim? Kai dueidah laemhong neh pumhong he a hliphen tih n'rhoe sut. Te dongah te rhoek aka puel sak te unim? Kai kamah bueng ka sueng vaengah melae amih eh?,” na ti ni.
Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
22 Ka Boeipa Yahovah loh he ni a thui. Namtom taengah ka kut ka thueng vetih pilnam hamla ka rholik ka thoh pah ni. Te vaengah tah na ca rhoek te poehla neh ham pawk puei uh vetih na tanu rhoek te laengpang dongah a poeh uh ni.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
23 Manghai rhoek te nang aka kaem la, a boeinu rhoek khaw nang aka khut la om uh ni. Nang taengah a talung neh diklai la bakop uh vetih na kho dongkah laipi a laem uh ni. Te vaengah kai Yahovah neh kai aka lamtawn rhoek loh yah a poh pawt te na ming uh ni.
Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
24 Hlangrhalh kah hnorhawt te a loh vetih aka dueng kah tamna te a loeih khaming a?
Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
25 Tedae BOEIPA loh, “Hlangrhalh tamna khaw a loh pah vetih hlanghaeng a dang khaw a khong pah ni. Na lungawn taengah kai loh kang rhoe vetih na ca rhoek te kamah loh ka khang ni.
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
26 Nang aka vuelvaek rhoek te a saa ka cah vetih a thii te thingtui bangla rhuihmil uh ni. Te vaengah pumsa boeih loh kai tah nang kah khangkung Yahovah neh nang aka tlan Jakob kah samrhang la a ming uh ni.
Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”