< Suencuek 39 >
1 Joseph te Egypt la a suntlak puei ngawn dae, anih aka suntlak puei Ishmael kut lamkah te Egypt hlang, imtawt mangpa, Pharaoh imkhoem, Potiphar loh pahoi a lai.
To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
2 Tedae BOEIPA te Joseph taengah a om dongah hlang thaihtak la coeng tih a boei Egypt hoel kah im ah om.
Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
3 A boei long khaw, BOEIPA te Joseph taengah tih a saii boeih te a kut dongah BOEIPA loh a thaihtak sak tila a hmuh.
Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
4 Joseph te a mikhmuh ah mikdaithen la a hmuh tih a taengah thotat. Te vaengah Potiphar loh a im te Joseph pum dongah a hlah pah. Te phoeiah a koe boeih te a kut ah a tloeng pah.
sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
5 Tedae a im neh a koe boeih te a hlah pah vaeng lamloh om tih, Joseph kong ah Egypt cako te BOEIPA loh yoethen a paek. BOEIPA kah yoethennah te a koe neh im, lo boeih dongla cet.
Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
6 A koe boeih te Joseph kut ah a hnoo pah van neh Egypt hoel loh buh caak bueng te a ming tih ba khaw amah loh ming pawh. Joseph ngawn tah a suisak sakthen tih mueimae sakthen la om.
Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
7 Tedae hekah olka he a om phoeiah a boei kah a yuu loh a dan vaengah Joseph te a mik neh a nai tih, “Kai taengah yalh mai,” a ti nah.
bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
8 Tedae a boei yuu te a aal tih, “Ka boeipa loh im kah aka om te kai taengah ngaiyak mueh la a khuehtawn boeih te ka kut ah a tloeng coeng.
Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
9 Hekah im ah kai lakah aka len a om moenih. Tedae nang tah a yuu la na om dongah nang mueh atah ba khaw kai ham a hloh moenih. Te dongah metlam lae boethae aka len he ka saii vetih Pathen taengah ka tholh sui dae,” a ti nah.
Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
10 Joseph taengah, khohnin khohnin a thui pah van dae a taengah yalh ham neh om hmaih ham te Joseph lohngaiyaknah pawh.
Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
11 Tedae hnin at ah Joseph te amah kah bi saii ham im khuila a caeh van hatah, tekah im ah im om hlang te khat khaw om pawh.
Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
12 Te dongah Potiphar yuu loh Joseph te a himbai ah a tuuk tih, “Kai taengah yalh mai,” a ti nah. Tedae Joseph loh a himbai te anih kut ah a caehtak phoeiah rhaelrham tih poeng la cet.
Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
13 Tedae a kut dongah a himbai a caehtak pa tih poeng la a rhaelrham vaengah te boeinu loh a hmu.
Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
14 Te dongah a im kah tongpa rhoek te a khue tih, “So uh lah, mamih aka lawn la Hebrew hlang te mamih taengla han khuen. Kai taengah yalh ham kamah taengla m'paan dongah ol ue neh ka pang.
sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
15 Tedae ka ol ka huel tih ka pang te a yaak hatah kai taegah a himbai a caehtak phoeiah rhaelrham tih poeng la cet,” a ti nah tih a thui pah.
Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
16 Te phoeiah a boei loh a im a paan duela a kah himbai te amah taengah a khoem.
Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
17 A taengah hekah olka bangla a thui pah tih, “Kai aka lawn ham ning taengah na det Hebrew sal loh ka taengah m'paan.
Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
18 Te dongah ka ol ka huel tih ka pang hatah a himbai te kai taengah a hnoo tih poeng la rhaelrham,” a ti nah.
Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
19 “Na sal loh kai hekah hno he a saii,” a ti nah tih a taengah a thui a yuu kah olka te a boei loh a yaak vaengah ngawn tah a thintoek ah pahoi sai.
Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
20 Te dongah Joseph te a boei loh a khuen tih manghai loh a khoh thongtla rhoek kah a hmuen, thong im ah a khueh dongah thong im ah pahoi om.
Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
21 Tedae BOEIPA loh Joseph a om puei tih sitlohnah a tueng sak dongah thong im kah mangpa mikhmuh ah anih te mikdaithen la a khueh.
Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
22 Te dongah thong im kah mangpa loh thong im kah thongtla boeih te Joseph kut ah a paek tih saii ham koi boeih te aka saii la Joseph khaw pahoi om.
Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
23 BOEIPA tah anih taengah om tih a saii te BOEIPA loh a thaihtak sak. Te dongah thong im mangpa a om pawt akhaw a kut hmuikah tah pakhat hilah boeih a sawt.
Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.