< Sunglatnah 2 >

1 Te vaengah Levi imkhui lamkah tongpa pakhat te cet tih Levi nu te a loh.
Ana nan, sai wani Balawe ya auri wata Balawiya,
2 A yuu te vawn tih capa a cun hatah anih tea then la a sawt tih hla thum a thuh.
ta kuwa yi ciki, ta haifi ɗa. Sa’ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har watanni uku.
3 Anih te koep thuh ham a coeng pawt vaengah tah anih ham talik lawng a loh pah tih lungpaat kunhnai neh a hluk. Te phoeiah a khuiah camoe te a khueh tih sokko tuikaeng kah carhaek ding ah a khueh.
Amma da ba tă iya ɓoye shi kuma ba, sai ta yi kwandon kyauro ta shafa masa kwalta. Bayan haka sai ta sa jaririn a cikin kwandon, ta je ta ajiye kwandon tare da jaririn a cikin kyauro, a bakin kogin.
4 Anih taengah metla a om khaw ming hamla a ngannu loh a hla lamkah a pai thil.
’Yar’uwarsa ta tsaya da ɗan rata tana lura da abin da zai faru da shi.
5 Te vaengah Pharaoh canu te tui hlu la sokko ah cet tih a hula puei neh sokko lihmoi ah pongpa uh. Tedae carhaek ding kah lawng te a hmuh vaengah a salnu te a tueih tih a loh pah.
Sai’yar Fir’auna ta gangara zuwa kogi domin tă yi wanka, bayinta kuwa suna tafiya a bakin kogi. Sai ta ga kwandon a ciyawa, ta aiki ɗaya daga cikin masu hidimarta tă ɗauko mata.
6 A ong vaengah camoe te a hmuh tih camoe khaw tarha ana rhap. Te dongah anih ham a thinphat tih, “Hebrew camoe la he,” a ti.
Da ta buɗe kwandon, sai ta ga yaro yana kuka, ta kuwa ji tausayinsa. Ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin jariran Ibraniyawa ne.”
7 Te vaengah a ngannu loh Pharaoh canu te, “Ka cet vetih nang ham Hebrew nu te, cakhoem la ka khue eh. Te daengah ni nang ham camoe hang khoem eh?,” a ti nah.
Sai’yar’uwarsa ta tambayi’yar Fir’auna, ta ce, “In tafi in samo ɗaya daga cikin matan Ibraniyawa tă yi miki renon yaron?”
8 Anih te Pharaoh canu loh, “Cet saw,” a ti nah dongah hula te cet tih camoe manu te a khue pah.
Sai ta amsa ta ce, “I, tafi.” Sai yarinyar ta tafi ta kawo mahaifiyar yaron.
9 Pharaoh canu loh anih te, “Camoe he caeh puei lamtah kai ham han cun, kamah loh na thapang kam paek bitni,” a ti nah. Te dongah manu loh camoe te a khuen tih a cun.
Diyar Fir’auna ta ce mata, “Ɗauki jaririn, ki yi mini renonsa, zan kuwa biya ki.” Saboda haka ta ɗauki yaron, ta yi renonsa.
10 Camoe te a pantai phoeiah Pharaoh canu taengla a khuen. Te vaengah a capa la om tih a ming te Moses a sui tih, “Anih he tui dong lamlong ni ka doek,” a ti.
Sa’ad da ya yi girma, sai ta kawo shi wajen’yar Fir’auna, ya kuwa zama ɗanta, ta kuma ba shi suna Musa, tana cewa, “Na tsamo shi daga ruwa.”
11 A khohnin loh a pha tih Moses khaw pantai coeng. Te dongah a manuca rhoek taengla pawk tih amih kah bitloh te a hmuh. Te vaengah a manuca Hebrew hlang mai Egypt hlang loh a ngawn pah te a hmuh.
Wata rana, bayan Musa ya yi girma, sai ya haura, ya tafi inda mutanensa suke, ya kuma ga yadda suke shan wahala da aiki. Ya ga wani mutumin Masar yana dūkan mutumin Ibraniyawa, ɗaya daga cikin mutanensa.
12 Tedae heben hebang la a mael akhaw hlang te hmu pawh. Te dongah Egypt te a ngawn tih laivin khuiah a up.
Da ya leƙa nan da can bai kuwa ga kowa ba, sai ya kashe mutumin Masar, ya ɓoye shi a yashi.
13 A hnin bae dongkah a mop vaengah tah Hebrew hlang rhoi te tarha ana hnuei uh rhoi. Te dongah aka halang te, “Balae tih na hui na ngawn?” a ti nah.
Kashegari ya fita, sai ya ga Ibraniyawa biyu suna faɗa. Ya tambayi mai laifin ya ce, “Don me kake bugun ɗan’uwanka, mutumin Ibraniyawa?”
14 Te vaengah, “Hlang khaw, Kaimih sokah mangpa neh laitloek la ulong nang ng'khueh, Egypt na ngawn bangla kai ngawn ham na cai nama?” a ti nah. Te dongah Moses loh a rhih coeng tih, “Dumlai khaw phoe taktak coeng,” a ti.
Mutumin ya ce masa, “Wa ya mai da kai mai mulki da mai hukunci a kanmu? Kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan?” Sai Musa ya tsorata, ya yi tunani ya ce, “To, fa, abin nan da na yi, ya zama sananne.”
15 Te ol te Pharaoh loh a yaak vaengah Moses te ngawn ham a mae. Tedae Moses tah Pharaoh mikhmuh lamloh yong tih Midian khohmuen ah kho a sak. Te vaengah tuito ah ngol hatah,
Da Fir’auna ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă kashe Musa, amma Musa ya gudu daga wajen Fir’auna, ya tafi ƙasar Midiyan inda ya zauna kusa da wata rijiya.
16 Midian khosoih kah a canu parhih te ha pawk uh tih tui a dueh uh. Te phoeiah a napa kah boiva te tul ham tuisoi dongah a loei uh.
To, fa, akwai wani firist na Midiyan, yana da’ya’ya mata bakwai, suka zo su shayar da dabbobin mahaifinsu.
17 Te vaengah boiva aka dawn rhoek te ha pawk uh tih huta rhoek te a haek uh. Tedae Moses te thoo tih huta rhoek a rhun tih a boiva te tui a tul pah.
Sai waɗansu makiyaya suka zo suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su ya shayar da dabbobinsu.
18 A napa Reuel taengla a pawk uh vaengah, “Tihnin ah tah balae tih yue na pawk uh,” a ti nah.
Da’yan matan suka komo wurin Reyuwel mahaifinsu, sai ya tambaye su ya ce, “Yaya kuka dawo da wuri yau?”
19 Te vaengah, “Egypt hlang loh kaimih he boiva aka dawn rhoek kut lamloh n'huul. Te phoeiah tui pataeng kaimih ham han dueh han dueh tih boiva te a tul,” a ti nauh.
Suka amsa suka ce, “Wani mutumin Masar ne ya taimake mu daga hannun waɗansu makiyaya. Har ma ya ɗebo ruwa ya shayar da dabbobin.”
20 Te dongah a ca rhoek te, “Melae anih? Balae tih hlang te na hnoo uh? Anih te khue uh lamtah buh ca dae saeh,” a ti nah.
Ya tambayi’yan matansa, “To ina yake? Don me kuka bar shi a can? A gayyace shi, yă zo, yă ci wani abu.”
21 Hlang neh khosak ham khaw Moses loh a ueh van coeng dongah a canu Zipporah te Moses taengah a paek.
Musa ya yarda yă zauna da mutumin wanda ya ba da’yarsa Ziffora aure da Musa.
22 Te vaengah capa a cun pah hatah kholong kho ah yinlai la ka om a ti tih a ming te Gershom a sui.
Ziffora ta haifi wa Musa ɗa, ya kuma raɗa masa suna Gershom cewa, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa.”
23 A tue muep a khum phoeiah tah Egypt manghai khaw duek. Te vaengah Israel ca rhoek te thohtatnah khui lamloh huei uh tih pang uh. Thohtatnah lamloh a pang uh te Pathen taengla cet.
Ana nan dai, a kwana a tashi, sai sarkin Masar ya mutu. Isra’ilawa suka yi kuka mai zafi saboda bautarsu mai wuya, sai kukar neman taimakonsu saboda bauta, ya kai wurin Allah.
24 Tedae Pathen loh amih kah nguekcoinah te a yaak tih Abraham taengkah, Isaak taengkah, Jakob taengkah a paipi te Pathen loh a poek.
Allah kuwa ya ji kukansu sai ya tuna da alkawarinsa da Ibrahim da Ishaku da Yaƙub.
25 Te dongah Pathen loh Israel ca rhoek te a hmuh tih amih te Pathen loh a ming.
Sai Allah ya dubi Isra’ilawa, ya kuma damu da su.

< Sunglatnah 2 >