< Caeltueih 8 >
1 Anih a ngawnnah te aka rhoih la Sual khaw om. Te vaeng tue ah a nah la hlangboel hnaemtaeknah te Jerusalem ah om. Te dongah caeltueih rhoek bueng pawt atah hlang boeih loh Judea neh Samaria paeng tom la palang uh.
Bulus ya amince da mutuwarsa. A wannan rana tsanani mai zafi ya fara tasowa akan Iklisiya da take a Urushalima, sai masu bangaskiya duka suka bazu ko ina a cikin garuruwan Yahudiya da Samariya, sai manzannin kadai aka bari.
2 Stephen te aka cuep hlang rhoek loh a up uh tih anih te rhangsaenah a saii uh.
Amintattun mutane suka bizne Istifanus suka yi babban makoki game da shi.
3 Tedae Saul tah im takuem la kun tih hlangboel te a phae. Huta tongpa te a mawt tih thongim ah a thak.
Amma Shawulu ya yi wa Iklisiya mugunta kwarai, ya dinga shiga gida gida yana jawo mutane maza da mata, kuma yana kulle su cikin kurkuku.
4 Te dongah aka palang rhoek long khaw caeh lam ah olthangthen a thui uh.
Duk da haka masu bangaskiyar nan da suka warwatsu suka tafi suka dinga yada wa'azin maganar.
5 Te vaengah Philip tah Samaria kho la cet tih amih taengah Khrih te a hoe.
Filibus ya tafi can Samariya ya yi shelar Almasihu.
6 Philip loh a thui te hlangping loh a hnatung tih huek a yaak uh vaengah miknoek a saii te a hmuh uh.
Da taron mutane suka ji kuma suka ga alamun da Filibus yake yi, sai suka mai da hankali dukansu domin su ji abinda yake fadi.
7 Rhalawt mueihla aka kaem rhoek te khaw ol ue la pang uh tih muep nong uh. Aka khawn neh aka khaem rhoek khaw muep hoeih uh.
Domin kazaman ruhohi sun fito daga cikin mutane da yawa da suka saurare shi suna kuka da kururuwa; nakasassun mutane dayawa da guragu suka warke.
8 Te dongah khopuei khuiah omngaihnah te muep om.
Kuma aka yi farin ciki mai girma a birnin.
9 Te vaengah kho khuikah aka om noek hlang pakhat, a ming ah Simon loh hlang a bi tih khat khat taengah amah te a len la om ham a ti dongah Samaria namtu te a limlum sak.
Amma akwai wani mutum a cikin birnin da ake kira Siman, wanda tun farko shi masafi ne da kuma dan dabo, yana yi wa mutanen Samariya abubuwan ban mamaki, yayin da yake kiran kansa wani mai muhimmanci.
10 Anih te a yit a len hlang boeih loh a hnatung uh tih, “A khuet la a khue Pathen kah a thaomnah ni he,” a ti uh.
Dukan Samariyawa, manya da yara, suna sauraronsa, su kan ce, ''Wannan mutum shine ikon Allahn nan wanda ake kira mai girma.''
11 Amih te kum te yet khuiah hlangbi neh a limlum sak dongah ni anih te a hnatung uh.
Suna sauraron sa, domin ya dade yana yi masu abubuwan mamaki da tsafe-tsafensa.
12 Tedae Philip loh a phong Pathen ram kawng neh Jesuh Khrih ming te a tangnah uh dongah huta tongpa a nuem.
Amma da suka yi bangaskiya da wa'azin bisharar da Filibus yake yi game da mulkin Allah da sunan Yesu Almasihu, sai aka yi masu Baftisma dukansu maza da mata.
13 Simon amah long khaw a tangnah dongah a nuem tih Philip taengah aka khuituk la coeng. Miknoek neh thaomnah tanglue a saii te a hmuh vaengah limlum.
Har shima Siman da kansa ya ba da gaskiya. Bayan an yi masa Baftisma ya cigaba da bin Filibus, da ya ga ana nuna alamu da manyan ayyuka, sai ya yi mamaki.
14 Samaria loh Pathen kah olka a doe te Jerusalem kah caeltueih rhoek loh a yaak uh vaengah amih taengla Peter neh Johan te a tueih uh.
Da manzannin da ke Urushalima suka ji labarin Samariya ta karbi maganar Allah, sai suka aika masu Bitrus da Yahaya.
15 A suntlak rhoi vaengah Mueihla Cim dang uh van saeh tila amih ham thangthui rhoi.
Da suka iso, suka yi masu addu'a, domin su karbi Ruhu Mai Tsarki.
16 Boeipa Jesuh ming neh nuem tangtae la om uh coeng dae, amih te Mueihla Cim loh pakhat khaw tlak thil la om hlan.
Domin har wannan lokaci, Ruhu Mai Tsarki bai sauko kan kowannensu ba; an dai yi masu baftisma ne kadai cikin sunan Ubangiji Yesu.
17 Te dongah amih te kut a tloeng thil rhoi tih Mueihla Cim a dang uh.
Sai Bitrus da Yahaya suka dora masu hannuwansu, sai suka karbi Ruhu Mai Tsarki.
18 Caeltueih rhoek kah kut a tloengnah lamloh Mueihla a paek te Simon loh a hmuh vaengah amih taengla tangka a khuen tih,
Sa'adda Siman yaga ana bayar da Ruhu Mai Tsarki ta wurin dorawar hannuwan manzanni, ya basu kudi.
19 “Tahae kah saithainah he kai khaw m'pae uh lamtah kut ka tloeng thil sarhui loh Mueihla Cim dang van saeh,” a ti nah.
Ya ce, “Ku bani wannan iko, ni ma, don duk wanda na dora wa hannu ya karbi Ruhu Mai Tsarki.''
20 Tedae Peter loh anih te, “Pathen kah kutdoe he tangka la kaelh ham na poek dongah, na tangka te namah taengah pocinah la om saeh.
Amma Bitrus yace masa, ''Azurfarka ta lalace tare da kai, saboda kana tunanin za ka malaki baiwar Ubangiji da kudi.
21 He olka dongah na hmulung neh khoyo a om moenih. Na thinko te Pathen hmaiah thaeng a om moenih.
Baka da wani rabo a wannan al'amari, domin zuciyarka ba daidai take da Allah ba.
22 Na phayoenah he yut lamtah Boeipa taengah thangthui. Na thinko kah mangtaengnah loh nang n'hlah vuek khaming.
Saboda haka ka tuba daga wannan muguntarka, ka kuma yi addu'a ga Ubangiji, domin mai yiwuwa ya gafarta maka game da manufar zuciyarka.
23 Olkhaa hmuet neh boethae kah pinyennah khuiah na om te ka hmuh,” a ti nah.
Domin na gane kana cikin bacin rai da kuma cikin daurin zunubi.''
24 Te dongah Simon loh a doo tih, “Boeipa taengah kai hamla nangmih loh thangtui uh lamtah na thui te kai soah ha thoeng boel saeh,” a ti nah.
Siman ya amsa ya ce, ''Kayi addu'a ga Ubangiji domina, kada wani daga cikin abubuwan nan da ka fada ya faru da ni.''
25 Te rhoek long te a uen uh tih Boeipa kah olka a thui pa uh phoeiah, Jerusalem la bal uh. Samaria kah kho te yet te khaw olthangthen phong pauh.
Sa'anda Bitrus da Yahaya suka bada shaida kuma suka fadi maganar Ubangiji, sun koma Urushalima; akan hanya, suka yi wa'azin bishara a kauyukan samariyawa da yawa.
26 Te vaengah Boeipa kah puencawn loh Philip te a voek tih, “Thoo, tuithim long ben la cet lamtah, Jerusalem lamloh Gaza la suntla thuk. Te ah te khosoek om lah ko,” a ti nah.
Yanzu kuwa Mala'ikan Ubangiji ya yi wa Filibus magana cewa, ''Tashi ka tafi ta kudu da hanyar da ta yi kasa daga Urushalima zuwa Gaza'' (wannan hanyar yana cikin hamada.)
27 Te dongah thoo tih a caeh vaengah Ethiopia manghai nu Kandaki kah hlueikhu mangpa Ethiopia hlang pakhat lawt humuh. Anih loh manghai nu kah khohrhang boeih a om thil. Te vaengah anih khaw bawk hamla Jerusalem ah ha lo.
Ya kuwa tashi ya tafi. Sai ga wani mutum daga Habasha, baba ne mai babban matsayi a karkashin Kandakatu, sarauniyar Habasha. Shine yake mulkin dukan dukiyarta. Ya zo Urushalima domin ya yi ibada.
28 Te tlam te om tih a bal vaengah amah kah leng khuiah ngol tih tonghma Isaiah te a tae.
Yana komawa zaune cikin karussarsa, kuma yana karanta Littafin annabi Ishaya.
29 Te vaengah Philip te Mueihla loh, “Leng ke paan lamtah ben lah,” a ti nah.
Ruhun ya ce wa Filibus, ''Ka je kusa da karussar nan.''
30 Puk a cuk vaengah tonghma Isaiah a tae te Philip loh a yaak tih, “Na tae te na yakming van nim te,” a ti nah.
Sai Filibus ya gudu ya same shi, kuma ya ji shi yana karanta littafin annabi Ishaya, sai ya ce, ''Ka fahimci abin da kake karantawa?''
31 Anih van long khaw, “Pakhat loh kai he long n'tueng pawt atah metlam ka coeng thai van eh?,” a ti nah. Te phoeiah amah taengla luei tih ngol hamla Philip te a cael.
Bahabashen ya ce. ''Yaya zan iya, idan ba wani ya bishe ni ba?'' Ya roki Filibus ya shigo cikin karussar ya zauna tare da shi.
32 Te dongah a tae olcim kah a hmuet a hma tah he tlam he om. Tu bangla maeh la a mawt tih, tuca bangla a mul aka rhuep hmaiah olmueh la om. Te dongah a ka khaw ang pawh.
Wannan kuwa shine nassin da Bahabashen yake karantawa, ''An kai shi kamar tunkiya zuwa mayanka; shiru kuma, kamar dan rago a hannun masu sosayarsa, bai bude baki ba.
33 Amah kah laitloeknah loh amah te mathoe khuila a khuen. A hingnah te diklai lamkah a loh pah coeng dongah a rhuirhong te u long a thui eh?
Cikin kaskancinsa aka yi masa shari'a da rashin adalci: Wa zai bada tarihin tsararsa? Domin an dauke ransa daga duniya.''
34 Te vaengah hlueikhu boei loh Philip te a doo tih, “Nang kan dawt lah eh, tahae kah a thui tonghma he u nim ca? Amah kawng a? A tloe khat khat kah a kawng a?” a ti nah.
Sai baban ya tambayi Filibus, ya ce, ''Na roke ka, gaya mani, game da wa annabin yake magana? Da kansa, ko kuwa wani mutum dabam?''
35 Te dongah Philip loh a ka a ong tih cacim lamloh a tong phoeiah Jesuh te anih taengah a phong.
Filibus ya fara magana; akan littafin Ishaya, ya kuwa yi masa wa'azi akan Yesu.
36 Long te a caeh phai rhoi vaengah tui pakhat te a pha rhoi. Te vaengah hlueikhu boei loh, “Tui ke, nuem ham ba long lae kai n'kang,” a ti nah.
Yayin da suke tafiya akan hanya, sai suka iso bakin wani kogi; Baban ya ce, “Duba, ga ruwa anan; me zai hana ayi mani baftisma?”
37 Te dongah Philip loh, “Na thinko boeih neh na tangnah nim ca?,” a ti nah hatah, “Jesuh Khrih tah Pathen capa ni tila ka tangnah,” a ti nah.
Filibus ya ce,” Idan ka gaskanta da zuciya daya, ana iya yi maka baftisma.” Sai Bahabashen ya ce, “Na gaskata Yesu Almasihu shine Dan Allah.”
38 Te dongah leng te pai sak ham ol a paek. Te phoeiah Philip khaw, hlueikhu boei khaw, tui khuila bok suntla rhoi tih anih te a nuem.
Sai Bahabashen ya umarta a tsai da karussar. Sai suka zo wurin ruwa dukan su biyu, Filibus da baban, Filibus kuwa yayi masa baftisma.
39 Tedae tui lamkah loh ha yoeng hang vaengah Philip te Boeipa kah Mueihla loh vik a khuen. Te vaengah hlueikhu boei loh anih te hmu voel pawh. Tedae a caehlong ah omngaih la cet.
Yayin da suka fito daga cikin ruwan, Ruhun Ubangiji ya dauke Filibus; baban bai sake ganin shi ba, sai ya ci gaba da tafiyar sa yana murna.
40 Te phoeiah Philip tah Azotus ah phoe tih, aka cet te Kaisarea a pha hlan khuiah khopuei takuem la olthangthen a phong.
Amma Filibus ya bayyana a Azotus. Ya ratsa wannan yankin yana wa'azin bishara a dukan garuruwan, har sa'anda ya iso Kaisariya.