< 2 Manghai 22 >

1 Josiah he kum rhet a lo ca vaengah manghai tih Jerusalem ah sawmthum kum khat manghai. A manu ming tah Bozkath lamkah Adaiah canu Jedidah ni.
Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
2 BOEIPA mikhmuh ah a thuem a saii. A napa David kah longpuei cungkuem dongah pongpa tih banvoei bantang la phael pawh.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
3 Manghai Josiah kah kum hlai rhet dongla a pha vaengah tah manghai loh BOEIPA im kah cadaek Meshullam koca Azaliah capa Shaphan te a tah tih,
A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
4 “Khosoih puei Hilkiah taengla cet lamtah BOEIPA im kah a khuen tangka te cum sak saeh. Te te cingkhaa aka tawt loh pilnam taeng lamkah ni a coi.
“Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
5 Te phoeiah BOEIPA im kah im bitat aka saii aka hung kut ah pae rhoe pae saeh. Te te BOEIPA im ah bi aka saii taeng neh im puut aka biing roek taengah,
Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
6 kutthai rhoek ham neh im aka sa rhoek ham khaw, aka biing ham neh thing lai ham khaw, im biing vaengkah lungrhaih lung ham khaw pae saeh,” a ti nah.
wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
7 Tedae amih khaw uepomnah neh a saii uh dongah amih kut dongah a paek tangka te amih taengah koep toem voel pawh.
Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
8 Te vaengah khosoih puei Hilkiah loh cadaek Shaphan taengah, “BOEIPA im ah olkhueng cabu ka hmuh,” a ti nah. Te phoeiah Hilkiah loh cabu te Shaphan taengah a paek tih a tae.
Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
9 Te phoeiah cadaek Shaphan te manghai taengla pawk tih manghai te ol a mael. Te vaengah, “Im khuikah a hmuh tangka te na sal rhoek loh a khok uh coeng. Te te BOEIPA im kah bi saii rhoek aka hung kut ah a paek uh coeng,” a ti nah.
Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
10 Cadaek Shaphan te manghai taengla puen tih, “Khosoih Hilkiah loh kai taengah cabu m'paek,” a ti nah. Te phoeiah te te Shaphan loh manghai mikhmuh ah a tae.
Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
11 Manghai loh olkhueng cabu dongkah ol te a yaak van neh a himbai te a phen coeng.
Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
12 Te dongah manghai loh khosoih Hilkiah, Shaphan capa Ahikam, Mikaiah capa Akbor, cadaek Shaphan neh manghai kah sal Asaiah te a uen tih,
Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
13 “Cet uh, kai ham neh pilnam ham khaw, Judah pum ham khaw BOEIPA te toem uh laeh. Cabu dongkah ol a hmuh dongah he BOEIPA kah kosi tah mamih taengah muep rhong coeng. He cabu olka he a pa rhoek lohngai uh pawh. Mamih ham a daek tah a cungkuem ah ngai ham om,” a ti nah.
“Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
14 Te dongah khosoih Hilkiah, Ahikam, Akbor, Shaphan neh Asaiah tah himbai aka khoem Harhas koca Tikvah capa Shallum yuu, tonghmanu Huldah taengla cet uh. Te vaengah anih te Jerusalem kah hnukthoi khopuei ah kho a sak tih amah te a voek uh.
Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
15 Te vaengah amih te, “Israel Pathen BOEIPA loh he ni a thui. Kai taengla nangmih aka tueih hlang taengah thui pah.
Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
16 BOEIPA loh he ni a thui. Kai loh he hmuen so neh a khuikah khosa rhoek soah khaw boethae ka khuen coeng. Cabu dongkah ol cungkuem te Judah manghai loh a tae coeng te.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
17 Kai n'toeng uh tih a kut dongkah bitat cungkuem neh kai veet hamla a tloe pathen taengah phum uh. Te dongah ka kosi loh he hmuen he a hlup tih daeh voel mahpawh.
Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
18 BOEIPA toem hamla nangmih aka tueih Judah manghai te a taengah Israel Pathen BOEIPA loh a thui ol he na yaak bangla thui pah.
Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
19 He hmuen so neh a khuikah khosa soah imsuep neh rhunkhuennah la om sak ham ka cal te na yaak vaengah na thinko phoena tih BOEIPA mikhmuh ah na kunyun coeng. Te vaengah na himbai te na phen tih ka mikhmuh ah na rhah khaw ka yaak bal coeng. He tah BOEIPA kah olphong ni.
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
20 Te dongah kai loh nang te na pa rhoek taengla kan humcui sak bini ne. Na phuel ah ngaimong la na khoem uhvetih he hmuen soah ka khuen boethae cungkuem te na mik loh hmu mahpawh,” a ti nah. Te phoeiah manghai te ol a mael uh.
Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.

< 2 Manghai 22 >