< 2 Manghai 21 >

1 Manasseh a manghai vaengah kum hlai nit ni a lo ca pueng tih Jerusalem ah kum sawmnga kum nga manghai. A manu ming tah Hephzibah ni.
Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
2 BOEIPA loh Israel ca rhoek mikhmuh lamkah a haek namtom rhoek kah tueilaehkoi bangla BOEIPA mikhmuh ah boethae a saii.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 Mael tih a napa Hezekiah loh a phae hmuensang te a sak. Baal ham hmueihtuk a thoh tih Israel manghai Ahab kah a saii bangla Asherah te a saii. Vaan kah caempuei cungkuem taengah bakop tih te rhoek taengah tho a thueng.
Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
4 BOEIPA loh, “Ka ming he Jerusalem ah ni ka khueh eh?,” a ti vanbangla BOEIPA im ah hmueihtuk a suem.
Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
5 BOEIPA im kah vongup rhoi ah vaan caempuei cungkuem ham hmueihtuk a suem pah.
Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
6 A ca te hmai dongah a kat sak. Kutyaek a sawt tih lung a sawt. Rhaitonghma a dawt tih a mikhmuh ah boethae saii ham neh BOEIPA veet ham te hnam la tlung.
Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
7 Asherah mueithuk a saii te im ah a khueh. Te te BOEIPA loh a ca David taeng neh Solomon taengah tah, “He im khui neh Israel koca cungkuem lamloh ka coelh Jerusalem ah he kumhal duela ka ming ka khueh ni.
Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 A cungkuem dongah amih ka uen bangla saii ham a ngaithuen uh mak atah a napa rhoek taengah ka paek khohmuen lamloh Israel kah khokan rhaehba sak ham ka khoep mahpawh. Te dongah a cungkuem dongkah olkhueng te ka sal Moses loh amih a uen coeng,” a ti nah.
Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
9 Tedae a ngai uh pawt dongah Manasseh loh amih kho a hmang sak. Te dongah BOEIPA loh Israel ca rhoek mikhmuh lamkah a milh sak namtom rhoek lakah boethae a saii.
Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 BOEIPA loh a sal, tonghma rhoek kut ah a thui tih,
Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
11 “Judah manghai Manasseh loh tueilaehkoi a saii vanbangla te rhoek te a mikhmuh kah Amori rhoek loh a saii boeih lakah khaw thae. Te dongah Judah khaw a mueirhol neh a tholh sak.
“Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
12 Te dongah ni Israel Pathen BOEIPA loh he he a thui. Kai loh Jerusalem neh Judah soah boethae ka khuen pah coeng. Te te aka ya la aka ya boeih tah a hna rhoi te umya uh bitni.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
13 Jerusalem soah Samaria rhilam neh Ahab im kah mikrhael ka toe ni. Bael a huih, a huih tih a hmai long a bueng bangla Jerusalem te ka huih ni.
Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
14 Ka rho kah a meet te ka phap vetih amih te a thunkha kut ah ka paek ni. Te vaengah a thunkha cungkuem taengah maeh neh maehbuem la om uh ni.
Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
15 Ka mikhmuh ah boethae a saii uh tih a napa rhoek Egypt lamkah a caeh uh khohnin lamloh tahae khohnin hil kai aka veet la om uh,” a ti nah.
domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
16 Ommongsitoe thii khaw Manasseh loh muep a long sak aih. Jerusalem a hmoi lamloh a hmoi hil a li sak. Amah kah tholhnah bueng kolla BOEIPA mikhmuh ah boethae saii hamla Judah te a tholh sak.
Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
17 Manasseh kah ol noi neh a cungkuem a saii te khaw, a tholhnah neh a tholh te khaw, Judah manghai rhoek kah khokhuen olka cabu dongah a daek uh moenih a?
Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
18 Manasseh te a napa rhoek taengla a khoem uh vaengah tah amah im kah dum, Uzzah dum ah a up uh. Te phoeiah a capa Amon te anih yueng la manghai.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
19 Amon he kum kul kum nit a lo ca vaengah manghai tih Jerusalem ah kum nit manghai. A manu ming tah Jotbah lamkah Haruz canu Meshullemeth ni.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
20 A napa Manasseh kah a saii bangla BOEIPA mikhmuh ah thae a saii bal.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
21 A napa kah a pongpa bangla longpuei cungkuem ah pongpa. A napa kah thothueng bangla mueirhol taengah tho a thueng tih te rhoek taengah bakop.
Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
22 A napa rhoek kah Pathen BOEIPA te a hnoo tih BOEIPA kah longpuei ah pongpa pawh.
Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
23 Tedae anih te Amon sal rhoek loh a taeng tih manghai te amah im ah a duek sakuh.
Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
24 Te dongah Amon manghai aka taeng boeih te khohmuen pilnam loh a ngawn. Te phoeiah tah khohmuen pilnam loh a capa Josiah te anih yueng la a manghai sakuh.
Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
25 Amon kah ol noi neh a saii te Judah manghai rhoek kah khokhuen olka cabu dongah a daek uh moenih a?
Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
26 Anih te Uzzah dum kah amah phuel ah a up. Te phoeiah a capa Josiah te anih yueng la manghai.
Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Manghai 21 >