< 2 Manghai 15 >

1 Israel manghai Jeroboam kah kum kul kum rhih dongah Judah manghai Amaziah capa Azariah te manghai van.
A shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Yerobowam sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya, sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Anih te kum hlai rhuk a lo ca vaengah manghai coeng tih Jerusalem ah sawmnga kum nit manghai. A manu ming tah Jerusalem lamkah Jekoliah ni.
Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya daga Urushalima.
3 A napa Amaziah loh a cungkuem a saii vanbangla BOEIPA mikhmuh ah a thuem ni a saii van.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
4 Tedae hmuensang te a khoe moenih. Hmuensang ah pilnam a nawn tih a phum pueng.
Amma bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane kuwa suka yi ta yin hadaya da ƙona turare a can.
5 BOEIPA loh manghai te a ben dongah a dueknah hnin duela pahuk. Te dongah im hloeh la om tih im ah manghai capa Jotham loh khohmuen pilnam te lai a tloek pah.
Ubangiji ya sa wa sarki ciwon kuturta har mutuwarsa, ya kuma zauna a keɓe. Yotam ɗan sarki, shi ne ya gudanar da sha’anin fada, ya kuma shugabanci mutanen ƙasar.
6 Azariah kah ol noi neh a cungkuem a saii te Judah manghai rhoek kah khokhuen olka cabu dongah a daek moenih a?
Game da sauran ayyukan mulkin Azariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
7 Azariah te a napa rhoek taengla a khoem uh vaengah anih te David khopuei kah a napa taengah a up uh. Te phoeiah a capa Jotham te anih yueng la manghai.
Azariya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi kusa da su a Birnin Dawuda. Yotam ɗansa, kuma ya gāje shi.
8 Judah manghai Azariah kah a kum sawmthum kum rhet vaengah Samaria kah Israel te Jeroboam capa Zekhariah loh hla rhuk a manghai thil.
A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Zakariya ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki wata shida.
9 A napa rhoek kah a saii bangla BOEIPA mik ah boethae ni a saii. Israel aka tholh sak Nebat capa Jeroboam kah tholhnah lamloh a nong moenih.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi. Bai bar aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi ba.
10 Jabesh capa Shallum loh anih te a taeng tih pilnam mikhmuh ah anih te a ngawn. Anih te a ngawn van nen tah anih yuengla manghai.
Sai Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zakariya maƙarƙashiya. Ya tasam masa a gaban jama’a, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
11 Zekhariah kah ol noi khaw Israel manghai rhoek kah khokhuen olka cabu dongah a daek uh coeng ne.
Game da sauran ayyukan mulkin Zakariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
12 Jehu taengah BOEIPA ol a thui pah bangla, “Nang lamkah a khong li ca hil tah Israel ngolkhoel dongah ngol ni,” a ti nah te thoeng tangloeng coeng.
Ta haka maganar Ubangiji da ya yi wa Yehu ta cika, wadda ya ce, “Zuriyarka za tă zauna a kursiyin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
13 Judah manghai Uzziah kah kum sawmthum kum ko vaengah Jabesh capa Shallum manghai tih Samaria ah hla khat hnin khat manghai.
Shallum ɗan Yabesh ya zama sarki a shekara ta talatin da tara ta mulkin Uzziya sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki na wata ɗaya a Samariya.
14 Te phoeiah tah Tirzah lamkah Gadi capa Menahem te cet tih Samaria la pawk. Te vaengah Samaria kah Jabesh capa Shallum te a ngawn tih anih a duek sak phoeiah tah anih yueng la manghai.
Sa’an nan Menahem ɗan Gadi ya gangara daga Tirza ya haura zuwa Samariya. Ya tasam wa Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
15 Shallum kah ol noi khaw, lairhui loh anih a ven te khaw Israel manghai rhoek kah khokhuen olka cabu dongah a daek uh coeng he.
Game da sauran ayyukan mulkin Shallum, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
16 Tiphsah Menahem neh a khuikah boeih khaw, Tirzah lamloh a khorhi te khaw a tloek. Thoh a ong pah pawt dongah bungvawn boeih te khaw a ngawn tih a bung a boe pah.
A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
17 Judah manghai Azariah kah a kum sawmthum kum ko vaengah Samaria kah Gadi capa Menahem loh Israel te kum rha a manghai thil.
A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya zama sarkin Isra’ila, ya yi mulki a Samariya shekara goma.
18 Amah tue khuiah tah BOEIPA mikhmuh ah boethae a saii tih Israel aka tholh sak Nebat capa Jeroboam kah tholhnah lamloh a nong moenih.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A duk tsawon mulkinsa, bai rabu da zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya sa Isra’ila suka aikata ba.
19 Assyria manghai Pul loh khohmuen a muk vaengah anih neh kut at la om ham khaw, amah kut ah ram duel ham khaw Menahem loh Pul taengah tangka talent thawng khat a paek.
Sai Ful sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar hari, Menahem kuwa ya ba shi talenti dubu na azurfa don yă sami goyon bayansa, yă kuma ƙarfafa kahuwa mulkin.
20 Menahem loh tangka te Israel taeng lamkah khaw, tatthai hlangrhalh boeih taeng lamkah khaw a khuen. Assyria manghai taengah a paek ham te hlang khat ah tangka shekel sawmnga a coi pah daengah Assyria manghai te khoe uh tih khohmuen ah khosa pawh.
Menahem ya tara kuɗin ne ta hanyar haraji a Isra’ila inda ya sa kowane attajiri ya ba da shekel hamsin don a ba sarkin Assuriya. Sa’an nan sarkin Assuriya ya janye, bai ƙara kasance a ƙasar ba.
21 Menahem kah ol noi neh a saii boeih te Israel manghai rhoek kah khokhuen olka cabu dongah a daek uh moenih a?
Game da sauran ayyukan mulkin Menahem, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
22 Menahem te a napa rhoek taengla a khoem uh neh a capa Pekahiah te anih yueng la manghai.
Menahem ya huta tare da kakanninsa. Fekahiya ɗansa kuma ya gāje shi.
23 Judah manghai Azariah kah kum sawmnga kum vaengah Menahem capa Pekahiah tah Samaria ah Israel kum nit a manghai thil.
A shekara ta hamsin ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekara biyu.
24 BOEIPA mikhmuh ah boethae a saii tih Israel aka tholh sak Nebat capa Jeroboam kah tholhnah lamloh a nong moenih.
Fekahiya ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat wanda ya sa Isra’ila ya aikata ba.
25 Anih te a rhalboei Remaliah capa Pekah loh a taeng. Te dongah anih te Argob neh, Arieh neh, a taengkah Giladi ca rhoek lamkah hlang sawmnga loh Samaria kah manghaimanghai im, impuei ah a ngawn. Anih te a duek sak phoeiah tah a yueng la amah tloep manghai.
Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
26 Pekahiah kah ol noi neh a saii boeih te Israel manghai rhoek kah khokhuen olka cabu dongah a daek uh coeng he.
Game da sauran ayyukan mulkin Fekahiya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
27 Judah manghai Azariah kah kum sawmnga kum nit dongah Remaliah capa Pekah loh Samaria ah Israel kum kul a manghai thil.
A shekara ta hamsin da biyu ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Feka ɗan Remaliya ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya yi mulki shekara ashirin.
28 BOEIPA mikhmuh ah boethae a saii tih Israel aka tholh sak Nebat capa Jeroboam kah tholhnah lamloh a nong moenih.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai kauce wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta yi ba.
29 Israel manghai Pekah tue vaengah Assyria manghai Tiglathpileser loh a paan tih Ijon, Abel, Janoah, Kedesh neh Hazor, Gilead, Galilee neh Naphtali khohmuen pum te a loh pah. Te phoeiah amih te Assyria la a poelyoe.
A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
30 Elah capa Hosea loh Remaliah capa Pekah te lairhui a sui thil. Pekah te a ngawn tih a duek sak phoeiah tah Uzziah capa Jotham kah a kum kul vaengah Pekah yueng la manghai.
Sa’an nan Hosheya ɗan Ela ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya. Ya fāɗa masa ya kuma kashe shi, sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki a shekara ta shirin ta mulkin Yotam ɗan Uzziya.
31 Pekah kah ol noi neh a saii boeih te Israel manghai rhoek kah khokhuen olka cabu dongah a daek uh coeng he.
Game da sauran ayyukan mulkin Feka da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 Israel manghai Remaliah capa Pekah kah a kum bae dongah Judah manghai Uzziah capa Jotham manghai van.
A shekara ta biyu ta mulkin Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Uzziya sarkin Yahuda ya fara mulki.
33 Anih te kum kul kum nga a lo ca vaengah manghai tih Jerusalem ah kum hlai rhuk manghai. A manu ming tah Zadok canu Jerusha ni.
Ya zama sarki yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
34 BOEIPA mikhmuh ah a thuem ni a saii. A cungkuem dongah a napa Uzziah kah a saii bangla a saii.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa Uzziya ya yi.
35 Te cakhaw hmuensang te a khoe moenih. Hmuensang ah pilnam a nawn tih a phum pueng. Anih loh BOEIPA im kah imhman vongka te a saii.
Duk da haka, bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙona turare a can. Yotam ya sāke gina Ƙofar Bisa ta haikalin Ubangiji.
36 Jotham kah ol noi neh a bi saii te Judah manghai rhoek kah khokhuen olka cabu dongah a daek uh moenih a?
Game da sauran ayyukan mulkin Yotam da aikin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
37 Te vaeng tue ah ana tong tih BOEIPA loh Judah taengla Aram manghai Rezin neh Remaliah capa Pekah te a tueih coeng.
(A kwanakin nan Ubangiji ya fara aikan Rezin sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, su yi gāba da Yahuda.)
38 Jotham te a napa rhoek taengla a khoem uh vaengah a napa David khopuei kah a napa rhoek taengah a up. Te phoeiah a capa Ahaz te anih yueng la manghai.
Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda, birnin mahaifinsa. Ahaz ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Manghai 15 >