< 2 Khokhuen 33 >

1 Manasseh te a manghai vaengah kum hlai nit lo ca pueng tih Jerusalem ah sawmnga neh kum nga manghai.
Manasse yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyar.
2 BOEIPA loh Israel ca mikhmuh lamkah a haek tangtae namtom kah tueilaehkoi bangla BOEIPA mik ah boethae a saii.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji, yana bin ayyukan banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 Mael tih a napa Hezekiah loh a palet tangtae hmuensang te a thoh. Baal hamla hmueihtuk a suem tih Asherah a saii. Vaan caempuei boeih taengah bakop tih te rhoek taengah tho a thueng.
Ya sāke gina masujadan kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe; ya tā da bagadan Ba’al, ya kuma gina ginshiƙan Ashera. Ya rusuna wa dukan rundunonin taurari, ya kuma yi musu sujada.
4 BOEIPA loh, “Ka ming he Jerusalem ah kumhal duela om ni,” a ti lalah BOEIPA im khuiah hmueihtuk a suem.
Ya gina bagadai cikin haikalin Ubangiji, waɗanda Ubangiji ya ce, “Sunana zai kasance cikin Urushalima har abada.”
5 BOEIPA im vongup rhoi ah vaan caempuei cungkuem ham hmueihtuk a suem.
Cikin filayen haikalin Ubangiji, ya gina bagadai ga dukan rundunonin taurari.
6 Anih loh a ca rhoek te kolrhawk kah hmai khuila a kat sak. Kutyaek a sawt, lung a sawt, hlang a bi, rhaitonghma neh hnam a saii. Amah veet hamla BOEIPA mik ah boethae a saii khaw khawk.
Ya miƙa’ya’yansa maza hadaya a wuta cikin Kwarin Ben Hinnom, ya yi bokanci, ya yi duba, ya kuma yi maitanci, ya nemi shawarar mabiya da masu ruhohi. Ya yi abin da yake mugu ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanarsa yă yi fushi.
7 Mueimae mueithuk a saii te Pathen im ah a khueh. Te te Pathen loh David taeng neh a capa Solomon taengah khaw, “Israel koca boeih lamloh ka coelh, he im khui neh Jerusalem khuiah tah kumhal duela ka ming te ka khueh eh.
Ya ɗauki siffar da aka sassaƙa wadda ya yi, ya sa ta a cikin haikalin Allah, wanda Allah ya ce wa Dawuda da kuma ɗansa Solomon, “Cikin wannan haikali da kuma cikin Urushalima, wanda na zaɓa daga cikin kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 Tedae Israel kah kho te na pa rhoek taengah ka thoh khohmuen dong lamloh nong sak ham ka khoep mahpawh. Moses kut lamloh amih ka uen bangla olkhueng neh oltlueh neh laitloeknah boeih te a cungkuem la vai ham a ngaithuen mak atah,” a ti.
Ba zan ƙara bari ƙafafun Isra’ilawa su bar ƙasar da na ba wa kakanninku ba, in dai suka yi hankali ga yin kome da na umarce su game da duka dokoki, ƙa’idodi da kuma farillai da na bayar ta wurin Musa.”
9 Tedae Manasseh loh namtom rhoek lakah boethae saii ham Judah neh Jerusalem khosa rhoek te kho a hmang sak. Te rhoek te BOEIPA loh Israel ca rhoek mikhmuh lamkah a mitmoeng sak coeng dae ta.
Amma Manasse ya sa Yahuda da mutanen Urushalima suka kauce, har suka aikata mugunta fiye da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 BOEIPA loh Manasseh taeng neh a pilnam taengah a thui dae hnatung uh pawh.
Ubangiji ya yi magana da Manasse da mutanensa, amma ba su kula ba.
11 Te dongah BOEIPA loh Assyria manghai kah caempuei mangpa rhoek te amih taengla a thak. Manasseh te mutlo hling neh a tuuk uh tih rhohum neh a khih uh phoeiah Babylon la a khuen uh.
Saboda haka Ubangiji ya kawo manyan hafsoshin mayaƙan sarkin Assuriya a kansu, waɗanda suka ɗauki Manasse a matsayi ɗan kurkuku, suka sa ƙugiya a hancinsa, suka daure shi da sarƙoƙin tagulla suka kuma kai shi Babilon.
12 A taengah puen a cak vaengah tah a Pathen BOEIPA mikhmuh ah nue coeng tih a napa rhoek kah Pathen mikhmuh ah muep kunyun.
Cikin wahalarsa ya nemi tagomashin Ubangiji Allahnsa ya kuma ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.
13 Tedae a taengla a thangthui vaengah tah anih te a rhoi tih a lungmacil te a hnatun pah. Te dongah amah khaw a ram te Jerusalem la mael. Te vaengah Manasseh loh Yahweh amah he Pathen ni tila a ming.
Da ya yi addu’a gare shi, sai Ubangiji ya taɓu da tubansa, ya kuma saurari roƙonsa; saboda haka ya dawo da shi Urushalima da kuma zuwa mulkinsa. Sa’an nan Manasse ya san cewa Ubangiji shi ne Allah.
14 A hnukah tah David khopuei rhamvoel kah vongtung te khotlak kah Gihon soklong ah a sak tih nga vongka a pha. Ophel te a tuung tih muep a sang sak. Judah kah vong cak khopuei boeih ah tatthai mangpa rhoek a khueh.
Daga baya ya sāke gina katangar waje na Birnin Dawuda, yamma da maɓulɓular Gihon a cikin kwari, har zuwa mashigin Ƙofar Kifi, ya kuma kewaye tudun Ofel; ya yi ta da tsayi sosai. Ya sa hafsoshin mayaƙa cikin dukan biranen katanga a Yahuda.
15 Kholong pathen rhoek neh a mueimae te khaw BOEIPA im lamloh a khoe tih, BOEIPA im tlang neh Jerusalem kah a sak hmueihtuk boeih khaw khopuei rhamvoel la a voeih.
Ya fid da baƙin alloli, ya kuma fid da siffofi daga haikalin Ubangiji, haka ma dukan bagadan da ya gina a kan tudun haikali da kuma cikin Urushalima, ya zubar da su a bayan birni.
16 BOEIPA kah hmueihtuk te cikngae la a sak bal tih a soah rhoepnah neh uemonah hmueih te a nawn. Judah taengah khaw Israel Pathen BOEIPA taengah thothueng hamla a thui pah.
Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji ya kuma miƙa hadayun salama da kuma hadayun godiya a bagaden, ya kuma faɗa wa Yahuda su bauta wa Ubangiji, Allah na Isra’ila.
17 Tedae pilnam te hmuensang ah a nawn pueng tih a Pathen BOEIPA te khaw a bawkuh.
Mutane dai suka ci gaba da miƙa hadayu a masujadai kan tudu, amma wa Ubangiji Allahnsu kaɗai.
18 Manasseh kah ol noi khaw, a Pathen taengah a thangthuinah khaw, Israel Pathen BOEIPA ming neh anih taengah aka thui khohmu rhoek kah ol khaw, Israel manghai rhoek kah olka khuiah om coeng ke.
Sauran ayyukan mulkin Manasse, haɗe da addu’arsa ga Allahnsa da kuma kalmomin da mai duba ya yi masa cikin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, suna a rubuce cikin tarihin sarakunan Isra’ila.
19 A thangthuinah neh a thangthui khaw, a tholhnah neh a boekoeknah boeih khaw, a soah hmuensang a sak nah hmuen te khaw, Asherah neh mueidaep a hol tih a hmai ah a kunyun khaw, Hozai kah olka khuiah a daek uh coeng ke.
Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
20 Manasseh te a napa rhoek taengla a khoem uh vaengah anih te amah im ah a up uh. Te phoeiah tah a capa Amon te anih yueng la manghai.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a fadansa. Sai Amon ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Amon a manghai vaengah kum kul kum nit lo ca pueng tih Jerusalem ah kum nit manghai.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki a Urushalima shekara biyu.
22 A napa Manasseh kah a saii bangla BOEIPA mik ah boethae a saii. A napa Manasseh kah a saii mueidaep cungkuem taengah Amon loh a nawn tih tho a thueng.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi. Amon ya bauta ya kuma miƙa hadayu ga dukan gumakan da Manasse ya yi.
23 A napa Manasseh kah a kunyun bangla BOEIPA mikhmuh ah a kunyun moenih. Amon amah lat loh dumlai a pung sak.
Amma ba kamar mahaifinsa Manasse ba, bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji ba; Amon ya ƙara laifinsa.
24 Te vaengah anih te a sal rhoek loh a taeng uh tih amah im ah a duek sakuh.
Fadawan Amon sukan yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a fadansa.
25 Te dongah manghai Amon aka taeng boeih te khohmuen pilnam loh a ngawn. Te phoeiah tah khohmuen pilnam loh a capa Josiah te anih yueng la a manghai sak.
Sa’an nan mutanen ƙasar suka kashe dukan waɗanda suka yi wa Sarki Amon maƙarƙashiya, suka naɗa Yosiya ɗansa sarki a maimakonsa.

< 2 Khokhuen 33 >