< 1 Manghai 20 >

1 Aram manghai Benhadad loh amah kah thadueng boeih neh a taengkah manghai sawmthum panit, marhang neh leng khaw a coi. Te phoeiah cet tih Samaria te a dum tih a vathoh thil.
Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
2 Te phoeiah khopuei la Israel manghai Ahab taengla puencawn a tueih.
Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
3 Ahab te, “Benhadad loh, 'Na cak neh na sui khaw kai ham, na yuu neh na ca khaw, na hnothen khaw kai ham,’ a ti,” a ti nah.
‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
4 Israel manghai loh a doo tih, “Ka boei manghai namah ol bangla kai neh ka taengkah boeih he namah ham ni,” a ti nah.
Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
5 Puencawn rhoek te mael tih, “Benhadad loh he ni a thui. Na cak neh na sui, hoe ham nang taengla kan tueih, na yuu na ca rhoek khaw kai taengah m'pae,’ a ti.
Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
6 Thangvuen tahae tue ah ka sal rhoek nang taengla kan tueih vetih na im neh na sal rhoek im khaw a phuelhthaih uh ni. Na mik loh a ngailaemnah boeih te a kut dongah a tloeng uh vetih a khuen ni,” a ti nah.
Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
7 Israel manghai loh khohmuen kah a ham rhoek boeih te a khue tih,” Ming uh laeh lamtah boethae a tlap he hmuh uh. Ka taengla han tueih vaengah ka yuu neh ka ca rhoek, ka cak neh ka sui khaw, anih ham ka hloh moenih,” a ti nah.
Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
8 Te vaengah anih te a ham boeih neh pilnam boeih loh, “Hnatun pah boeh, ngaih pah boeh,” a ti nah.
Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
9 Te dongah Benhadad kah puencawn rhoek te, “Ka boei manghai te thui pah, lamhma la sal nan tueih vaengkah boeih te tah ka ngai ni. Tedae tahae kah ol he ka ngai ham a coeng moenih,” a ti nah. Te phoeiah puencawn rhoek te cet uh tih ol te a mael puei uh.
Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
10 Benhadad loh anih te ol a tah tih, “Samaria kah laipi he ka kho kung kah pilnam boeih ham kutpha dongah a buem atah pathen loh kai taengah n'saii saeh lamtah n'koei van saeh,” a ti nah.
Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
11 Israel manghai loh a doo tih, “Thui pa uh, a ka vah khaw aka dul bangla yan uh boel saeh,’ ti nah.
Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
12 Amah neh manghai rhoek loh dungtlungim ah a ok uh li vaengah he ol he a yaak. Te dongah a sal rhoek te, “Rhuengphong uh,” a ti nah tih khopuei te a rhuengphong thil uh.
Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
13 Te vaengah Israel manghai Ahab taengla tonghma pakhat pakcak a mop pah tih, “BOEIPA loh he ni thui, hlangping he yet he boeih na hmuh nama? Tihnin ah kai loh na kut dongah kam paek coeng tih kai he BOEIPA la nan ming bitni ne,” a ti nah.
Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
14 Te vaengah Ahab loh, “U nen nim?” a ti nah. Te dongah, “BOEIPA loh he ni a thui, paeng kah mangpa cadong rhoek neh,” a ti nah. Te phoeiah, “U long caemtloek a pin eh?” a ti nah hatah, “Nang loh,” a ti nah.
Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
15 Te dongah paeng kah mangpa cadong rhoek te a soep tih yahnih sawmthum panit lo uh. Amih phoeiah Israel ca boeih, pilnam pum te thawng rhih la a soep.
Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
16 Te phoeiah khothun ah a muk uh dae Benhadad tah amah neh anih aka bom manghai rhoek, manghai sawmthum panit rhoek tah dungtlungim ah a ok uh tih rhui uh.
Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
17 Te vaengah paeng kah mangpa cadong rhoek te lamhma la khoong uh tih Benhadad taengla a tueih. Te dongah a taengla puen uh tih, “Samaria lamkah hlang ha khoong,” a ti nah.
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
18 Te vaengah, “Rhoepnah ham ha pawk akhaw amih te a hing la tu uh, caemtloek ham ha pawk akhaw amih te a hing la tu uh,” a ti nah.
Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
19 Te tlam te khopuei lamloh paeng kah mangpa cadong rhoek khoong uh tih amih hnukah tatthai rhoek te omuh.
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
20 Hlang pakhat loh hlang pakhat van a tloek uh dongah Aram rhoek te rhaelrham uh. Amih te Israel loh a hloem dae Aram manghai Benhadad tah marhang caem neh marhang dongah vik loeih.
Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
21 Israel manghai te cet tih marhang khaw leng khaw a ngawn pah. Aram soah hmasoe len neh a ngawn.
Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
22 Te vaengah tonghma te Israel manghai taengla thoeih. Te phoeiah anih te, “Cet, thaahuel lamtah ming laeh. Kum a thok vaengah Aram manghai loh nang taengla ha pawk ham dongah metla na saii ham khaw ana so,” a ti nah.
Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
23 Te vaengah Aram manghai kah sal rhoek loh, “Amih kah pathen tah tlang kah pathen ni. Te dongah mamih lakah tlung uh. Tedae amih te tlangkol ah m'vathoh thil koinih amih lakah n'tlung uh van mapawt nim?
Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
24 He ol bangla saii laeh. Manghai rhoek te amah hmuen lamloh rhip khoe lamtah amih yueng la rhalboei rhoek te tloep khueh laeh.
Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
25 Namah loh nang lamkah caem a ha tarhing ah namah ham caem te hueh laeh. Marhang khaw marhang tarhing ah, leng khaw leng tarhing ah khueh laeh. Tlangkol ah amih m'vathoh thil ham te amih lakah n'tlung het mahpawt nim?” a ti nah. Te dongah amih ol te a hnatun tih a saii tangloeng.
Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
26 Kum a thok vaengah tah Benhadad loh Aram te a soep tih Israel caemtloek thil ham Aphek la cet.
Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
27 Israel ca rhoek khaw soep uh thae, cangbam uh thae tih amih te mah hamla cet uh. Tedae Israel ca rhoek loh amih taengah maae ca rhoi bangla a rhaeh uh vaengah Aram loh diklai a khuk uh coeng.
Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
28 Te vaengah Pathen kah hlang te mop tih Israel manghai te a voek. Te phoeiah, “BOEIPA loh he ni a thui. Aram rhoek loh, 'Yahweh he tlang kah pathen ni, tuikol pathen moenih,’ a ti uh dongah hlangping he yet he nang kut la boeih kam paek. Te dongah kai he BOEIPA la nan ming bitni,” a ti nah.
Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
29 Te rhoek danah hnin rhih rhaeh uh tih a hnin rhih dongah a pha vaengah caemtloek te pha uh. Te vaengah Israel ca rhoek loh khohnin pakhat neh Aram rhalkap thawng yakhat a ngawn uh.
Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
30 Aka sueng rhoek te Aphek khopuei la rhaelrham uh van dae hlang aka sueng duen thawng kul thawng rhih te vongtung loh a cungku thil. Benhadad te rhaelrham tih khopuei ah imkhui kah imkhui patoeng la kun.
Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
31 Te vaengah a sal rhoek loh anih te, “Israel im kah manghai rhoek tah sitlohnah manghai la n'yaak uh coeng he. Mamih cinghen ah tlamhni, mamih lu dongah rhui yil uh mai sih. Israel manghai taengla cet uh sih lamtah na hinglu khaw han hlun khaming,” a ti nauh.
Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
32 Te dongah tlamhni te a cinghen ah, rhui te a lu ah a yen uh. Te phoeiah Israel manghai taengla cet uh tih, “Na sal Benhadad loh, 'Ka hinglu tah hing mai saeh,’ a ti,” a ti nauh. Te vaengah, “Anih ka manuca te amah hing pueng a?” a ti nah.
Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
33 Te vaengah hlang rhoek loh lung a sawt uh tih tokthuet uh. Anih te a hmuek coeng dongah, “Na manuca Benhadad ni,” a ti uh vaengah, “Paan uh lamtah anih te lo uh,” a ti nah. Te dongah Benhadad te a taengla a pawk neh leng dongah a caeh puei.
Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
34 Te vaengah Benhadad loh Ahab te, “A pa loh na pa taeng lamkah a loh khopuei rhoek te kam mael pawn eh. A pa loh Samaria ah a khueh vanbangla Damasku ah namah ham kawtpoeng la khueh,” a ti nah. Te dongah, “Kai khaw paipi bangla nang kan tueih bitni,” a ti nah. Te dongah anih neh paipi a saii tih a tueih.
Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
35 Tonghma ca rhoek khuikah hlang pakhat loh BOEIPA ol bangla a hui taengah, “Kai he n'ngawn laeh,” a ti nah. Tedae hlang loh anih ngawn ham te a aal.
Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
36 Te dongah anih te, “BOEIPA ol te na hnatun pawt dongah kai taeng lamloh na caeh neh sathueng loh nang n'ngawn ni te,” a ti nah. Te dongah anih taeng lamloh a caeh neh anih te sathueng loh a hmuh tih a ngawn.
Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
37 Hlang tloe te a hmuh vaengah, “Kai he n'ngawn mai,” a ti nah. Te dongah anih te hlang pakhat loh a ngawn vaengah a hi hamla a ngawn.
Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
38 Te phoeiah tonghma te cet tih longpuei ah manghai ana pai thil. Te vaengah a mik dongkah mikben neh vik a ben.
Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
39 Manghai a pah phai vaengah manghai te a pang thil tih, “Na sal he caemtloek lakli la ka cet. Tedae hlang khat pakcak ha pawk tih kai taengla hlang hang khuen. Te vaengah, 'He kah hlang he ana dawn dae, a ha la a ha atah a hinglu ham te na hinglu om vetih cak talent khat neh na sah ni, ' a ti.
Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
40 Tedae na sal he heben hebang ah aka tok la a om vaengah anih ana om voel pawh,” a ti nah. Tedae Israel manghai loh anih te, “Namah kah laitloeknah te namah loh na hlavawt coeng,” a ti nah.
Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
41 Te phoeiah a mik dong lamkah mikben te hawl a khong daengah anih te Israel manghai loh amah tonghma rhoek khui lamkah la a hmat.
Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
42 Te phoeiah Ahab te, “BOEIPA loh he ni a thui. Hlang he kai kut lamloh yaehtaboeih la na hlah dongah a hinglu yueng la na hinglu, a pilnam yueng la na pilnam te om ni,” a ti nah.
Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
43 Te dongah Israel manghai te a im la rhihnun cukduk neh thintoek la mael tih Samaria la pawk.
Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.

< 1 Manghai 20 >