< 1 Khokhuen 22 >

1 David loh, “He he BOEIPA Pathen im neh he tah Israel ham hmueihhlutnah hmueihtuk saeh,” a ti.
Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
2 Te dongah David loh Israel khohmuen kah yinlai te calui ham a thui tih Pathen im sak vaengkah lungrhaih lung aka phaek aka dae la a khueh.
Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
3 Vongka thokhaih thohkhaih kah thicung ham neh hnarhui ham David loh a sikim sak dongah thi khaw puh mai tih rhohum khaw a puh coeng dongah a khiing tae lek pawh.
Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
4 Lamphai thing khaw a pum tae lek pawt hil Sidoni neh Tyre lamkah a pawk pah. Lamphai thing he David ham tah thawt mai.
Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
5 David loh, “Ka capa Solomon he camoe tih mongkawt pueng. BOEIPA ham im a sak he khaw a ming a sang neh pantai saeh. Diklai boeih lakli ah boeimang saeh. Anih ham he ka sikim pawn eh?,” a ti. Te dongah David he a duek hlan ah a cungkuem la sikim coeng.
Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
6 Te phoeiah a capa Solomon te a khue tih Israel Pathen BOEIPA im sak hamla anih te a uen.
Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
7 Te vaengah David loh a capa Solomon te, “Ka capa aw, kai he ka thinko ah tah ka Pathen BOEIPA ming la im sak ham om.
Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
8 Tedae BOEIPA ol te kai taengla ha pawk tihThii khaw muep na long sak, caemtloek khaw muep na saii, ka mikhmuh ah diklai la thii muep na long sak dongah ka ming ham he im na sa mahpawh.
Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
9 Na taengah capa na sak coeng te ta. Anih tah hlang mong la om vetih anih te a kaepvai kah a thunkha cungkuem lamloh ka duem sak ni. Solomon ngawn tah a ming khaw om vetih anih tue vaengah tah Israel te rhoepnah neh rhalmongnah ka paek ni.
Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
10 Anih loh ka ming ham he im a sak vetih anih te kamah taengah capa la om ni. Kai khaw a taengah a napa la ka om ni. A ram kah ngolkhoel khaw Israel soah kumhal duela ka cikngae sak ni,’ a ti.
Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
11 Ka capa aw na taengah BOEIPA om saeh lamtah n'thaihtak sak saeh. BOEIPA na Pathen im te na taengkah a thui bangla sa.
“Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
12 Israel soah nang n'uen vaengah he na Pathen BOEIPA kah olkhueng te ngaithuen hamla BOEIPA loh nang taengah lungmingnah neh yakmingnah m'pae bal saeh.
Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
13 BOEIPA loh Israel ham Moses a uen vanbangla oltlueh neh laitloeknah te vai hamla na ngaithuen atah na thaihtak ni. Te dongah thaahuel lamtah namning rhih boeh, rhihyawp boeh.
Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
14 Kamah kah phacipphabaem nen ni BOEIPA im hamla a soepsoei coeng he. Sui he talent thawng yakhat, cak he talent thawng thawng khat, rhohum khaw, thi khaw muep lo coeng tih a khiing tae lek moenih. Thing khaw, lungto khaw ka tawn coeng dae tomthap thil nawn.
“Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
15 Namah taengah bitat aka saii khaw, lungto aka dae neh kutthai khaw, thing thai khaw, bitat cungkuem dongah boeih aka cueih khaw a cungkuem la om coeng.
Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
16 Sui neh, cak neh, rhohum neh, thi neh, a tarhing naa voel moenih. Thoo lamtah saii laeh. Na taengah BOEIPA om saeh,” a ti nah.
zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
17 Te phoeiah David loh Israel mangpa boeih te khaw a capa Solomon te bom hamla a uen.
Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
18 Nangmih kah Pathen BOEIPA he nangmih taengah a om moenih a? Khohmuen khosa rhoek te ka kut dongah m'paek tih kaepvai ah khaw nangmih te n'duem sak. Te dongah khohmuen he BOEIPA mikhmuh neh a pilnam mikhmuh ah khoem uh coeng.
Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
19 Nangmih kah Pathen BOEIPA te toem hamla na thinko neh na hinglu te pae uh laeh. Thoo uh lamtah Pathen BOEIPA kah rhokso te sa uh laeh. BOEIPA kah paipi thingkawng neh Pathen kah hmuencim hnopai te BOEIPA ming ham a sak im khuila khuen ham om,” a ti nah.
Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”

< 1 Khokhuen 22 >