< Johan 11 >

1 Te vaengah Mary neh a manuca Martha kah a kho Bethany kah Lazarus tah satlo la om.
To wani mutum mai suna Li'azaru, yayi rashin lafiya. Shi mutumin Baitanya ne, wato kauyen su Maryamu da 'yar'uwarta Matta.
2 Tekah Mary tah Boeipa te botui neh aka hluk tih a kho te a sam neh aka huih ni. Anih kah nganpa Lazarus tah tlo.
Wato wannan Maryamu da ta shafe Ubangiji da mur ta kuma share masa kafafunsa da gashin kanta, wadda dan'uwanta Li'azaru ke rashin lafiya.
3 Te dongah amih boeina loh Jesuh te a tah tih, “Boeipa, na lungnah te tlo coeng he,” a ti nah.
'Yan'uwannan mata suka aika sako wurin yesu, cewa, “Ubangiji, duba, shi wanda kake kauna yana rashin lafiya”.
4 Jesuh loh a yaak vaengah, “Hekah tloh tah dueknah la om mahpawh tedae Pathen kah thangpomnah ham ni. Te daengah ni te lamloh Pathen capa te a thangpom eh,” a ti nah.
Da Yesu ya ji, sai ya ce “Wannan ciwo ba zai kai ga mutuwa ba, amma domin daukakar Allah ne, domin Dan Allah ya sami daukaka tawurin ta”.
5 Te vaengah Jesuh loh Martha, a mana neh Lazarus te a lungnah.
Yesu yana kaunar Matta, da 'yar'uwarta da Li'azaru.
6 Tedae a tloh te a yaak vaengah a om nah hmuen ah hnin nit bet naeh.
Da yaji cewa Li'azaru na rashin lafiya, sai ya tsaya kwana biyu a inda ya ke.
7 Te phoeiah hnukbang rhoek te, “Judea la koep cet uh sih,” a ti nah.
Bayan haka, sai ya ce wa almajiransa, “Bari mu je Yahudiya kuma.”
8 Hnukbang rhoek loh amah te, “Rhabbi, Judah rhoek loh nang dae ham m'mae uh pueng lalah te la koep na cet aya?” a ti uh.
Sai almajiransa suka ce masa, “Mallam, harwayau Yahudaya na neman ka domin su jefe ka da duwatsu, kuma kana son komawa can?”
9 Jesuh loh, “Hnin at te khonoek loh hlainit a om moenih a? Khat khat long ni khothaih ah a pongpa atah he diklai kah vangnah te a hmuh dongah tongtah pawh.
Yesu ya amsa, “Ba sa'a goma sha biyu ce ta haske a rana guda ba? Idan mutum ya yi tafiya da rana, ba za ya yi tuntube ba, domin yana gani ta wurin hasken wannan duniya.
10 Tedae pakhat loh khoyin ah a pongpa atah anih ah vangnah a om pawt dongah a tongtah,” a ti nah.
Amma idan mutum ya yi tafiya chikin dare, za ya yi tuntube domin haske ba ya tare da shi.
11 Hekah he a thui phoeiah amih te, “Mamih paya Lazarus ip tih anih haeng ham ka cet ni,” a ti nah.
Ya fadi wadannan al'amura, kuma bayan wadannan abubuwa, sai ya ce masu, “Abokinmu Li'azaru ya yi barci, amma zan je don In tashe shi daga barci”.
12 Te dongah hnukbang rhoek loh amah taengah, “Boeipa, a ih atah daem bitni,” a ti na uh.
Sai almajirai suka ce masa, “Ubangiji, idan barci yake yi, ai za ya farka.”
13 Jesuh loh anih kah dueknah kawng a thui. Tedae amih loh aka ip kah duemnah kawng a thui la a poek uh.
Yesu kuwa ya yi maganar mutuwar Li'azaru ne, amma su suna tsammani yana magana akan barci ne na hutu.
14 Te dongah Jesuh loh amih taengah sayalh la, “Lazarus duek coeng.
Sai Yesu ya yi masu bayani cewa, “Li'azaru ya mutu.
15 Tedae nangmih ham ka omngaih. Te daengah ni pahoi ka om pawt te na tangnah uh eh. Tedae anih taengla cet uh sih,” a ti nah.
Ina farinchiki domin ku, da bani a wurin domin ku gaskata. Bari mu je wurinsa.”
16 Te dongah Didymus la a khue hnukbang Thomas loh, “Amah taengah duek puei ham mamih khaw cet uh sih,” a ti.
Toma wanda ake kira Dan tagwaye, ya ce wa sauran almajirai, “Bari mu tafi domin mu mutu tare da Yesu.”
17 Jesuh a pha vaengah anih te hlan khuiah hnin li a om coeng te a hmuh.
Da Yesu ya iso, sai ya tarar cewa Li'azaru ya rigaya ya yi kwana hudu a kabari.
18 Bethany te Jerusalem phatom kah phalong hlainga tluk a hla ah om.
Baitanya kuma tana kusa da Urushalima, 'yar tafiya marar nisa ce a tsakanin su.
19 Te vaengah Judah rhoek khaw Martha neh Mary te a nganpa kongah suem hamla muep pawk uh.
Yahudawa dayawa sun zo wurin Maryamu da Matta domin su yi masu ta'aziyar mutuwar dan'uwansu.
20 Te dongah Jesuh ha lo te Martha loh a yaak vaengah anih te a doe. Tedae Mary tah im ah ngol.
Da Matta ta ji cewa Yesu na zuwa, sai ta tafi domin ta same shi, amma Maryamu na zamne a cikin gida.
21 Te vaengah Martha loh Jesuh te, “Boeipa, he ah na om koinih ka nganpa duek pawt sue.
Matta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan tare da mu, da dan'uwana baya mutu ba”.
22 Tedae tahae pataeng Pathen taengah na bih te tah Pathen loh nang m'paek ni tila ka ming,” a ti nah.
Ko yanzu na san cewa duk abinda ka roka a wurin Allah, za ya ba ka.
23 Jesuh loh anih te, “Na nganpa te thoo bitni,” a ti nah.
Yesu ya ce mata, “Dan'uwanki za ya rayu kuma.
24 Martha loh, “Hnukkhueng khohnin kah thohkoepnah dongah thoo ni tila ka ming ta,” a ti nah.
Sai Matta ta ce masa, “Na san zaya rayu kuma a tashin mattatu na ranar karshe.”
25 Jesuh loh anih taengah, “Kai tah thohkoepnah neh hingnah la ka om. Kai ah aka tangnah tah duek cakhaw hing ni.
Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu, ni ne kuma rai; wanda ya bada gaskiya gare ni, ko ya mutu, za ya rayu;
26 Kai aka tangnah tih aka hing boeih tah kumhal duela duek loengloeng mahpawh, he he na tangnah a?” a ti nah. (aiōn g165)
Kuma duk wanda yake raye, ya kuma bada gaskiya gare ni, ba zai mutu ba dadai. Kin gaskata da wannan?” (aiōn g165)
27 Amah te, “Thuem ngawn Boeipa, nang tah diklai la aka lo Pathen capa Khrih ni tila kan tangnah,” a ti nah.
Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, Na gaskata cewa kaine Almasihu, Dan Allah, wanda ke zuwa duniya.
28 Hekah he a thui phoeiah cet tih a mana Mary a khue tih, “Saya ha pai tih nang n'khue,” duem a ti nah.
Sa'adda ta fadi haka, sai ta koma ta kira yar'uwarta Maryamu gefe guda. Ta ce, “mallam ya iso, kuma yana kiran ki.”
29 Te loh a yaak vaengah hlat thoo tih Jesuh taengla cet.
Da ta ji haka, sai ta tashi da sauri ta tafi wurin sa.
30 Te vaengah kho khuila Jesuh ham pha hlan dae Martha loh a doe nah hmuen ah om pueng.
Yesu bai rigaya ya shiga kauyen ba, yana nan inda Matta ta zo ta same shi.
31 Im ah anih aka om puei Judah rhoek neh anih aka suem rhoek loh Mary hlat thoo tih a caeh te a hmuh uh vaengah aka rhap ham hlan la cet tila a poek uh tih a vai uh.
Da Yahudawan nan dake tare da Maryamu, wato wadannan da suka zo mata ta'aziya, suka ga ta fita daga chikin gida da sauri, sai suka bi ta, suna tsammanin cewa ta tafi ta yi kuka ne a kabari.
32 Mary loh Jesuh om nah a pha tih amah te a hmuh vaengah a kho kung ah bakop tih, “Boeipa, he ah na om koinih ka nganpa duek mahpawh,” a ti nah.
Da Maryamu ta kai inda Yesu ya ke, sai ta fadi gaban sawayensa, ta ce, “Ubangiji, inda kana tare da mu, da dan'uwana bai mutu ba”.
33 Jesuh loh anih a rhah neh anih aka puei uh Judah rhoek kah a rhah te a hmuh vaengah a mueihla thanueih tih thuen.
Da Yesu ya gan ta tana kuka, da wadannan Yahudawa da suka bi ta, sai ya yi juyayi a ruhu ya damu kuma;
34 Te dongah, “Melam anih na khueh uh?” a ti nah. Te vaengah Jesuh te, “Boeipa, ha lo lamtah so lah,” a ti na uh.
sai ya ce, “A ina kuka kwantar da shi?” Sai suka ce masa, “Ubangiji, zo ka gani.”
35 Jesuh tah mikphi bo.
Yesu ya yi kuka.
36 Te dongah Judah rhoek loh, “Lazarus bahoeng a lungnah ke,” a ti uh.
Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake kaunar Li'azaru!”
37 Tedae amih khuikah hlangvang loh, “Mikdael kah mik te aka tueng sak long he te khaw a duek pawt ham a saii thai moenih a?” a ti uh.
Amma wadansun su suka ce, “Shi wannan mutum da ya iya ba makaho ganin gari, da bai iya hana wannan mutum mutuwa ba?
38 Te dongah Jesuh tah a khuiah thanueih tih hlan la koep ha pawk. Tedae hlan te lungko la om tih lungto khoep yalh.
Yesu yana cikin juyayi kuma a cikin kansa, sai ya tafi kabarin. Kabarin a kogo ne an kuma rufe bakinsa da dutse.
39 Jesuh loh, “Lungto te khoe uh lah,” a ti nah hatah aka duek kah a ngannu Martha loh, “Boeipa, hninli om coeng tih rhim coeng,” a ti nah.
Sai Yesu ya ce, “A kawar da dutsen.” Matta yar'uwar Li'azaru wanda ya mutu, ta ce wa Yesu, “Ubangiji, Yanzu jikin ya ruba domin ya kai kwana hudu da mutuwa”.
40 Jesuh loh anih te, “Na tangnah atah Pathen kah thangpomnah na hmuh ni tila nang taengah ka thui moenih a?” a ti nah.
Yesu ya ce mata, “Ba na ce maki idan kin gaskata za ki ga daukakar Allah ba?”
41 Te dongah lungto te a khoe uh. Te phoeiah Jesuh loh a mik te a dai hang tih, “A Pa, kai ol na hnatun dongah nang te kan uem.
Sai suka kawar da dutsen. Yesu ya daga idanunsa ya ce, “Uba, na gode maka domin kana ji na.”
42 Te phoeiah kai kah he na yaak yoeyah tila ka ming. Tedae hlangping loh m'pai thil dongah nang loh kai nan tueih te a tangnah uh ham ka thui,” a ti.
Na san kana ji na a kowane lokaci, amma domin wannan taro da ke tsaye kewaye da ni nike wannan magana, domin su bada gaskiya cewa kaine ka aiko ni.”
43 Te phoeiah ol ue neh pang tih, “Lazarus. pawk ha cu,” a ti nah.
Bayan ya yi wannan magana, sai ya daga murya ya ce, “Li'azaru, ka fito!”
44 Te vaengah aka duek te a kut a kho himbaipen neh a yen tih a hman kah te himbaica neh a yol doela ha thoeng. Jesuh loh amih taengah, “Anih te hlam uh lamtah caeh sak uh,” a ti nah.
Sai mataccen ya fito; kafafunsa da hannayensa na daure da likkafani, fuskarsa kuma na lullube da tsumma. Yesu ya ce masu, “Ku kwance shi, ya tafi”.
45 Te dongah Judah khuikah te yet, Mary taengla a pha tih a saii te aka hmu long tah amah te a tangnah uh.
To dayawa daga cikin yahudawan da suka zo wurin Maryamu suka kuma ga abinda Yesu ya yi, suka gaskata da shi;
46 Tedae amih khuikah a ngen tah Pharisee rhoek taengla cet uh tih Jesuh loh a saii te a thui pa uh.
amma wadansu suka koma wurin farisawa suka fada masu abubuwan da Yesu ya yi.
47 Te dongah khosoihham rhoek neh Pharisee rhoek loh khoboei a hueh uh tih, “Hekah hlang loh miknoek muep a saii dongah metlam n'saii eh?
Sai manyan firistoci da farisawa suka tara majalisa wuri guda, suka ce, “menene za mu yi?” Mutumin nan yana alamu masu yawa.
48 Hetlam he anih n'hlahpham uh koinih anih te boeih a tangnah uh ni. Te vaengah Roman rhoek te ha lo uh vetih mamih kah a hmuen neh namtu khaw a khuen ni,” a ti uh.
Idan mun kyale shi haka, duka za su gaskata da shi; Romawa za su zo su kwace wurinmu da al'ummar mu.
49 Tedae amih khuikah pakhat, tevaeng kum kah khosoihham la aka om Kaiaphas loh amih te, “Nangmih loh pakhat khaw na ming uh moenih.
Duk da haka, wani daga cikin su wato, Kayafas wanda shine babban firist a wannan shekara, ya ce da su, “baku san komai ba”.
50 Hlang pakhat loh pilnam yueng la duek vetih namtu tah boeih a poci pawt koinih nangmih ham rhoei ngai tila na poek uh moenih,” a ti nah.
Ba ku lura cewa ya fi maku kyau mutum daya ya mutu domin mutane, a maimakon dukan al'umma ta hallaka.”
51 Tedae hekah he amah lamkah a thui moenih. Tedae te kum kah khosoihham la a om dongah namtu ham Jesuh duek la a cai te ni a phong coeng.
Ya fadi wannan ne ba don kansa ba, amma sabo da shine babban firist, ya yi anabci ne cewa ya kamata Yesu ya mutu domin al'ummar;
52 Te phoeiah namtom ham bueng pawt tih taekyak tangtae Pathen ca rhoek te khaw pakhat la coicip ham pawn ni.
kuma ba don alummar kawai ba, amma domin a tattara 'ya'yan Allah da suke warwatse ko'ina wuri daya.
53 Te dongah te khohnin lamloh amah te ngawn ham a moeh uh.
Tun daga wannan rana suka fara neman hanyar da za su kashe Yesu.
54 Te dongah Jesuh loh Judah rhoek lakliah sayalh la pongpa voelpawh. Tedae kho yoei kah khosoek Ephraim la a khue kho ah cet tih hnukbang rhoek neh naeh uh.
Tun daga nan Yesu ya dena tafiya a sarari chikin Yahudawa, amma sai ya koma wani yanki kusa da jeji a wani gari da ake kira Ifraimu. A can kuma ya zamna da almajiransa.
55 Te vaengah Judah rhoek kah yoom tah om tom coeng. Te dongah amamih te ciim ham yoom hlanah paeng lamloh Jerusalem la muep cet uh.
Idin ketarewa na Yahudawa ya yi kusa, da yawa sun tafi Urushalima daga yankin kasar kamin ranar idi domin su tsarkake kan su.
56 Jesuh te a toem uh tih bawkim khuiah a pai uh vaengah, “Nangmih ta metlam na poek uh? Khotue la ha pawk loengloeng mahpawh,” tila khat neh khat thui uh thae.
Suka shiga neman Yesu, suna magana da junan su yayin da suke tsaitsaye a haikali, cewa “me kuke tunani? Ba za ya zo idin bane?”
57 Tedae khosoihham rhoek neh Pharisee rhoek loh, “Khat khat loh a om nah a ming atah amah te tuuk ham ha puen saeh,” tila ol a paek uh coeng.
Babban firist da farisawa sun rigaya sun ba da umurni cewa duk inda aka ga Yesu a zo a shaida domin su kama shi.

< Johan 11 >