< Ezekiel 8 >
1 Kum rhuk kum hla rhuk dongkah hnin nga a lo vaengah kamah im ah ka ngol tih kamah mikhmuh ah Judah kah patong rhoek khaw ngol uh. Te vaengah ka Boeipa Yahovah kah kut he kai sola pahoi ha tla.
A shekara ta shida, a wata shida a ranar ta biya, yayinda nake zaune a gidana dattawan Yahuda kuma suna zaune a gabana, hannun Ubangiji Mai Iko Duka ya zo a kaina a can.
2 Ka sawt vaengah hmai kah a mueimae bangla phek om he. A mueimae te a cinghen lamloh a dang due hmai bangla om. A cinghen lamloh a so duela rhohumbok kah a pang neh khophaa kah mueimae bangla om.
Na duba, sai na ga siffa kamar na mutum. Daga kwankwaso zuwa ƙasa ya yi kamar wuta, kuma daga kwankwaso zuwa sama kamanninsa ya yi haske yana ƙyalli kamar ƙarfe mai haske.
3 Kut kah muei bang te a thueng tih ka lu samtoel ah kai n'doek. Te vaengah mueihla loh kai he diklai laklo neh vaan laklo la m'pom. Te phoeiah kai te Pathen kah mangthui khuiah tlangpuei la aka mael Jerusalem khui kah vongka thohka la ng'khuen. Te te thatlainah mueimae neh aka thatlai kah tolrhum ni.
Ya miƙa abin da ya yi kamar hannu ya kama a gashin kaina. Ruhu ya ɗaga ni tsakanin sama da ƙasa, a cikin wahayoyi kuma Allah ya ɗauke ni zuwa Urushalima, zuwa ƙofa zuwa gabas na cikin fili, inda gunki mai tsokanar kishi yake tsaye.
4 Te vaengah Israel Pathen kah thangpomnah he kolbawn ah a mueimae la pahoi ka hmuh coeng he.
A can gabana kuwa ga ɗaukakar Allah na Isra’ila, kamar a wahayin da na gani a fili.
5 Te phoeiah kai taengah, “Hlang capa aw, tlangpuei longpuei la na mik huel laeh,” a ti. Ka mik he tlangpuei longpuei la ka huel tangloeng hatah thatlainah mueimae kah hmueihtuk vongka te tlangpuei ah kak ka hmuh. Te te thohkaeng ah ni a om.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, duba waje arewa.” Sai na duba, a mashigin arewa na ƙofar bagaden kuwa na ga wannan gunki na tsokanar kishi.
6 Te phoeiah kai taengah, “Hlang capa, amih te na hmuh nama? Amih loh tueilaehkoi a saii uh khungdaeng coeng te. Ka rhokso lamloh lakhla ham he Israel imkhui long ni a saii. Tedae koep na mael vetih tueilaehkoi khaw muep na hmuh bitni,” a ti.
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da suke yi, abubuwan banƙyamar da gidan Isra’ila ke yi a nan, abubuwan da za su kore ni daga wuri mai tsarkina? Amma za ka ga abubuwan da suka ma fi banƙyama.”
7 Te phoeiah kai te vongup thohka la ng'khuen hatah pangbueng dongah a khui pakhat te lawt ka hmuh.
Sa’an nan ya kawo ni mashigin filin. Na duba, na kuma ga rami a bango.
8 Te vaengah kai taengah, “Hlang capa, pangbueng te thuk laeh,” a ti. Te dongah pangbueng te ka thuk hatah thohka pakhat lawt ka hmuh.
Ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka haƙa cikin bangon.” Da na haƙa cikin bangon sai na ga ƙofar shiga a can.
9 Te phoeiah kai taengah, “Paan lamtah boethae rhoek kah tueilaehkoi te so lah, te te amih long ni he ah he a saii uh,” a ti.
Sai ya ce mini, “Shiga ka ga mugaye da kuma abubuwa banƙyamar da suke yi a can.”
10 Ka kun vaengah rhulcai muei cungkuem neh konawhnah rhamsa kah mueirhol boeih khaw kak ka hmuh. Te te Israel im ah pangbueng kah a kaep a kaep ah a vuel.
Na kuwa shiga na duba, sai na ga zāne-zāne ko’ina a bangon na kowane irin abubuwa masu rarrafe da kuma dabbobi masu ƙazanta da dukan gumakan gidan Isra’ila.
11 Amih lakli ah Israel imkhui kah patong hlang sawmrhih neh Shaphan capa Jaazaniah khaw pai. Amih hmai ah aka pai hlang loh a kut dongah hmaibael te a pom. Te vaengah bo-ul kah a hu a thah la khu.
A gabansu ga dattawa saba’in na gidan Isra’ila tsaye a cikinsu, Ya’azaniya ɗan Shafan kuwa yana tsaye a cikinsu. Kowa yana da farantin ƙona turare a hannunsa, tulin hayaƙin turare mai ƙanshi ya tunnuƙe zuwa sama.
12 Te phoeiah kai taengah, “Hlang capa, Israel im kah patong rhoek loh a ngaihlih imkhui kah hlang neh hmaisuep ah a saii te na hmuh nama? 'BOEIPA loh mamih m'hmuh pawt tih khohmuen he BOEIPA loh a hnoo coeng,” a ti uh,” a ti.
Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da dattawan gidan Isra’ila suke yi a cikin duhu, kowa yana a ɗakin tsafin gunkinsa? Suna cewa, ‘Ubangiji ba ya ganinmu; Ubangiji ya yashe ƙasar.’”
13 Te phoeiah kai taengah, “Koep na mael vaengah amih loh tueilaehkoi a tanglue a saii uh te na hmuh bitni,” a ti.
Ya kuma ce, “Za ka gan su suna yin abubuwan da suka fi waɗannan banƙyama.”
14 Te dongah kai te tlangpuei kah BOEIPA im vongka kah thohka la m'pawk puei. Te vaengah manu tarha ana ngol pahoi tih Tammuz te a rhah uh.
Sa’an nan ya kawo ni mashigin arewa na ƙofar gidan Ubangiji, sai na ga mata zaune a can, suna makokin Tammuz.
15 Te vaengah kai taengah, “Hlang capa na hmuh coeng nama? Koep na mael vaengah he lakah a nah la tueilaehkoi na hmuh ni,” a ti.
Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan? Za ka ga abubuwan da suke masu banƙyama fiye da wannan.”
16 Te phoeiah kai te BOEIPA im vongup khui la m'pawk puei. Te vaengah BOEIPA bawkim thohka kah ngalha laklo neh hmueihtuk laklo ah hlang pakul panga tluk ana om. BOEIPA bawkim te a hnuk la a rhoe uh tih a maelhmai khothoeng la a khuehuh. Amih loh khothoeng kah khomik te a bawk uh.
Sa’an nan ya kawo ni cikin fili na cikin gidan Ubangiji, a can kuwa a ƙofar haikali, tsakanin shirayi da bagade, akwai kamar mutum ashirin da biyar. Suka ba haikalin Ubangiji baya suna fuskanta wajen gabas, suna rusuna wa rana a gabas.
17 Te vaengah kai taengah, “Hlang capa na hmuh coeng nama? Judah imkhui loh tueilaehkoi a saii te phoeng a? Khohmuen te kuthlahnah neh cung sak kuekluek ham ni a saii uh he. Kai veet ham ni mael uh tih amih loh a hnarhong te thingluei a hu thil lah ko te.
Ya ce mini, “Ka ga wannan, ɗan mutum? Ƙaramin abu ne gidan Yahuda su yi abubuwan banƙyamar da suke yi a nan? Dole ne su cika ƙasar da rikici su kuma ci gaba da tsokane ni in yi fushi? Dube su suna tsokanata!
18 Te dongah kai loh kosi neh ka saii ni. Ka mik loh rhen pawt vetih lungma ka ti mahpawh. Ka hna ah ol ue la ng'khue uh cakhaw amih ol ka hnatun mahpawh,” a ti.
Saboda haka zan hukunta su cikin fushi; Ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba. Ko da yake suna ihu a kunnuwana, ba zan saurare su ba.”