< Olrhaepnah 6 >

1 Tahae kah olpaek, oltlueh neh laitloeknah he pang ham na muk uh khohmuen ah nangmih cang puei ham neh saii sak ham ni na BOEIPA Pathen loh n'uen.
Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
2 Te dongah na BOEIPA Pathen te na rhih tih a khosing neh a olpaek boeih te namah neh na ca long khaw, na ca kah a ca long khaw, na hing tue khuiah ngaithuen sak ham ni kai loh nang kang uen. Te daengah ni na hinglung a vang eh.
saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
3 Aw Israel na yaak van coeng dongah na ngai ham te ngaithuen lah. Te long ni nang te khophoeng m'pha sak vetih na pa rhoek kah BOEIPA Pathen loh nang taengah a thui vanbangla suktui neh khoitui aka long khohmuen ah muep na ping eh.
Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
4 Israel aw hnatun lah BOEIPA pakhat bueng ni mamih kah BOEIPA Pathen la aka om.
Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
5 Na BOEIPA Pathen te na thinko boeih, na hinglu boeih, na cungkuem boeih neh lungnah lah.
Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
6 Tihnin ah kai loh nang kang uen olka he nang kah thinko ah rhaehrhong lah saeh.
Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
7 Na ca rhoek pum dongah pak pah lamtah na im ah na ngol vaengah khaw, long na caeh vaengah khaw, na yalh vaengah khaw, na thoh vaengah khaw thui pah.
Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
8 Na kut ah miknoek la cin pah lamtah na mikhmuh ah samtoelrhui bangla om saeh.
Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
9 Na im rhungsut neh na vongka dongah khaw daek pah.
Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
10 “Tedae nang taengah paek ham na pa rhoek Abraham, Isaak neh Jakob taengah a caeng tangtae na thoong mueh khopuei dangka neh aka then,
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
11 na sang pawt dae thennah cungkuem neh aka khawk im la, na vuet pawt dae a vueh tangtae tuito la, misur neh olive khaw na tue pawt dae na caak tih na hah nah khohmuen ah nang aka thak la na BOEIPA Pathen te om bitni.
gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
12 Namah te ngaithuen, Egypt kho lamkah sal imkhui lamloh nang aka khuen BOEIPA te na hnilh ve.
ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
13 Na BOEIPA Pathen te rhih lah. Amah taengah tho na thueng phoeiah ni a ming nen khaw na toemngam eh.
Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
14 Na kaepvai pilnam rhoek kah pathen, hlangtloe pathen hnukah cet boeh.
Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
15 Na khui kah na Pathen BOEIPA tah thatlai Pathen ni. Na BOEIPA Pathen kah a thintoek he nang taengah ha sai vetih nang te diklai maelhmai dong lamloh m'mit sak ve.
gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
16 Massah ah na noemcai uh bangla na BOEIPA Pathen te noemcai uh boeh.
Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
17 Na BOEIPA Pathen kah olpaek khaw, a olphong neh a oltlueh nang n'uen te khaw ngaithuen rhoela ngaithuen.
Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
18 BOEIPA mikhmuh ah a thuem neh a then la saii. Te daengah ni nang te khophoeng m'pha sak phoeiah na pa rhoek taengah BOEIPA loh a caeng khohmuen then te na paan vetih na pang eh.
Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
19 BOEIPA loh a thui vanbangla na thunkha boeih te na mikhmuh lamloh a thaek ni.”
Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
20 “Thangvuen ah na ca loh nang n'dawt tih, ‘Mamih BOEIPA Pathen kah olphong, oltlueh neh laitloeknah te balae,’ a ti ni.
Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
21 Na ca taengah, Egypt ah Pharaoh sal la n'om uh vaengah BOEIPA loh tlungluen kut neh Egypt lamkah mamih n'doek.
Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
22 BOEIPA loh mamih mikhmuh ah Egypt soah, Pharaoh neh a imkhui boeih soah miknoek neh kopoekrhai a len koek neh yoethae te a paek.
A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
23 Tedae mamih tah a pa rhoek taengah a caeng sut khohmuen te mamih taengah paek ham ni te lamloh n'loh tih n'khuen.
Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
24 Tihnin kah bangla mamih aka hing sak ham mamih ham khohnin takuem a then dongah mamih kah BOEIPA Pathen rhih ham neh he rhoek kah oltlueh boeih he vai sak ham BOEIPA loh mamih n'uen coeng.
Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
25 Mamih n'uen vanbangla tahae kah olpaek boeih he mamih kah BOEIPA Pathen mikhmuh ah vai ham n'ngaithuen uh atah mamih ham duengnah la om van ni.”
In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”

< Olrhaepnah 6 >