< 2 Timothy 2 >

1 Te dongah ka ca nang Khrih Jesuh ah lungvatnah neh thaphoh uh.
Kai kuma, ɗana, ka yi ƙarfi cikin alherin da yake cikin Kiristi Yesu.
2 Te khaw kai lamloh laipai a yet neh na yaak coeng. He he uepom hlang taengah pae ne. Amih tah a tloe thuituen ham khaw khangmai la om bitni.
Abubuwan da ka ji na faɗa a gaban shaidu masu yawa kuwa ka danƙa wa amintattun mutane waɗanda su ma za su iya koya wa waɗansu.
3 Jesuh Khrih kah rhalkap then la patang puei.
Ka jure wa shan wahala tare da mu kamar soja mai kyau na Kiristi Yesu.
4 Aka vathoh loh a khosaknah dongkah khosak rhamok neh a tingtong pawt daengah ni caemthoh te kolo la a om eh.
Ba wanda yake aikin soja da zai sa kansa a sha’anin mutumin da ba ya aikin soja, domin yakan so yă gamshi wanda ya ɗauke shi soja.
5 Khat khat long khaw a loehlang dae a longim pawt la a loehlang atah rhuisam a khuem moenih.
Haka ma, in wani ya yi gasa a matsayi shi ɗan wasa ne, ba ya sami rawanin nasara, sai in ya yi gasar bisa ga dokoki.
6 Thakthae lotawn te lamhma la a thaih a dang ham a kuek.
Manomi mai aiki sosai ya kamata yă zama na fari wajen samun rabon amfanin gona.
7 Ka thui te yakming lah. A cungkuem dongah yakmingnah te Boeipa loh nang ham m'paek bitni.
Ka yi tunani a kan abin da nake faɗi, gama Ubangiji zai ba ka ganewa cikin dukan wannan.
8 Kaimih kah olthangthen vanbangla David tiingan lamkah neh duek lamkah aka thoo Jesuh Khrih te poek.
Ka tuna da Yesu Kiristi, wanda aka tā da shi daga matattu, zuriyar Dawuda, wanda shi ne bisharata,
9 Te ham te laihmuh bangla thongtlak hilah ka patang dae Pathen kah Olka tah pinyen hlan.
wadda nake shan wahala har ga daurin sarƙa kamar mai laifi. Amma Maganar Allah ba a daure take ba.
10 Te dongah a coelh rhoek ham te boeih ka ueh. Te daengah ni khangnah te amih loh dungyan thangpomnah neh Khrih Jesuh ah a dang uh van eh. (aiōnios g166)
Saboda haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton da yake cikin Kiristi Yesu, tare da madawwamiyar ɗaukaka. (aiōnios g166)
11 He ol he a uepom ta. N'duek atah n'hing puei van ni ta.
Ga wata magana tabbatacciya, “In muka mutu tare da shi, za mu rayu tare da shi;
12 N'ueh uh atah m'manghai uh van ni ta. N'hnawt uh van atah amah loh mamih he n'hnawt van ni.
in muka jimre, za mu yi mulki tare da shi. In muka yi mūsunsa, shi ma zai yi mūsunmu;
13 Amah a hnawt thai pawt dongah n'hnalval uh cakhaw anih tah uepom la naeh ngawn ta.
in ba mu da aminci, shi dai mai aminci ne, domin shi ba zai iya mūsun kansa ba.”
14 He rhoek he thoelh pah. Pathen hmaiah naenam pawt ham kang uen. A hoeikhang ham pawt he aka ya rhoek kah pocinah ham ni te.
Ka riƙa tuna masu da haka, ka kuma gama su da Allah, kada su yi jayayya a kan maganganu, don ba ta da wani amfani, sai ɓad da masu ji kawai take yi.
15 Oltak olka te aka paekhlae, aka birhih pawh bibikung tih namah te Pathen taengah ueppang koi la pai hamla haam lah.
Ka yi iyakacin ƙoƙarinka ka gabatar da kanka a gaban Allah a matsayin wanda aka amince da shi, ma’aikaci wanda ba shi da dalilin jin kunya wanda kuma yake fassara kalmar gaskiya daidai.
16 Tedae a rhonging kah olhong te rhael, hlangrhong khuila muep cungphoek uh ve.
Ka yi nesa da maganganun banza na rashin tsoron Allah, gama waɗanda suka mai da hankali ga yin waɗannan za su ƙara zama marasa tsoron Allah.
17 Amih kah olka te khaw hmapuek manrhaicak bangla cet ni. Te khuiah Hymenaeus neh Philetu om rhoi.
Koyarwarsu za tă bazu kamar ruɓaɓɓen gyambo. A cikinsu akwai Himenayus da Filetus,
18 Amih rhoi loh oltak te a hlihloeh sak rhoi tih thohkoepnah om coeng a ti rhoi. Te vaengah hlangvang kah tangnah te a palet rhoi.
waɗanda suka bauɗe daga gaskiya. Suna cewa tashin matattu ya riga ya faru, suna kuma ɓata bangaskiyar waɗansu.
19 Tedae Pathen kah khoengim tah khangmai la pai. Hekah kutnoek aka om dongah amah kah la aka om rhoek te Boeipa loh aming. Te dongah Boeipa ming aka phoei boeih long tah boethae lamloh nong saeh.
Duk da haka, ƙaƙƙarfan tushen nan na Allah yana nan daram, an hatimce shi da wannan rubutu, “Ubangiji ya san waɗanda suke nasa,” da kuma, “Duk wanda ya bayyana yarda ga sunan Ubangiji, to, dole yă yi nesa da aikata mugunta.”
20 Tahae kah im puei ah sui neh caben hnopai bueng pawt tih thing neh diklai umam khaw om. Te dongah a ngen tah thangpomnah ham om dae a tloe te tah yahpohnah la om.
A babban gida akwai kayayyakin da ba na zinariya da na azurfa kaɗai ba, amma har da na katako da na yumɓu ma; waɗansu domin hidima mai daraja waɗansu kuwa domin hidima marar daraja.
21 Te dongah khat khat loh he lamkah amah a cilpoe atah boeikung kah a congpang koi neh bibi then boeih ham a hmoel tih a ciim thangpomnah hnopai la om ni.
In mutum ya tsabtacce kansa daga na farkon zai zama kayan aikin hidima mai daraja, mai amfani ga Maigida, kuma shiryayye domin yin kowane aiki mai kyau.
22 Te dongah cadongcaloe kah hoehhamnah te rhaelrham tak lamtah duengnah, tangnah, lungnah, thinko a caih la Boeipa aka phoei rhoek neh rhoeprhoinah te huul lah.
Ka yi nesa da mugayen sha’awace-sha’awace na ƙuruciya, ka kuma bi adalci, bangaskiya, ƙauna da kuma salama, tare da waɗanda suke kira ga Ubangiji daga zuciya mai tsabta.
23 Tedae aka ang neh angvawk kah olpungnah te hnawt lamtah rhalthohnah ni a. saii uh tila ming lah.
Kada wani abu yă haɗa ka da gardandamin banza da wofi, domin ka san yadda suke jawo faɗa.
24 Te dongah Boeipa kah sal loh hnueih ham a kuek moenih. Tedae a cungkuem ham kodo la khala neh ueh ham a kuek.
Bai kamata bawan Ubangiji yă zama mai neman faɗa ba; a maimako, dole yă nuna alheri ga kowa, mai iya koyarwa, mai haƙuri kuma.
25 Thimkalh rhoek muelhtuetnah neh toel mai. Amih te Pathen loh oltak mingnah dongla yutnah khaw a paek khaming.
Waɗanda suke gāba da shi kuwa dole yă yi musu gargaɗi cikin hankali, da fata Allah zai sa su tuba su kai ga sanin gaskiya,
26 Te daengah ni amah loh amah kongaih la a tuuk khaw rhaithae kah thaang lamloh a sae uh eh.
su kuma dawo cikin hankulansu su kuɓuta daga tarkon Iblis, wanda ya sa suka zama kamammu don su aikata nufinsa.

< 2 Timothy 2 >