< 2 Samuel 6 >

1 David loh hlang boeih a coi tih Israel khuikah Te thawng sawmthum a coelh.
Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
2 Te phoeiah caempuei BOEIPA ming la a ming a khue tih a soah Cherub loh a ngol thil, Pathen thingkawng te te lamloh Baale-Judah la khuen ham David Te hlah uh tih amah taengkah pilnam te boeih a caeh puei.
Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
3 Pathen thingkawng te leng a thai dongah a hol uh tih som kah Abinadab im lamloh a khuen uh. Te vaengah leng a thai te Abinadab capa Uzzah neh Ahio loh a hmaithawn.
Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
4 Som kah Abinadab im lamloh Pathen thingkawng a khuen uh vaengah Te Ahio Te thingkawng hmai ah cet.
da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
5 David neh Israel imkhui pum loh BOEIPA kah mikhmuh ah hmaical thing, rhotoeng, thangpa, kamrhing, tingkoei, tlaklak neh boeih luem uh.
Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
6 Nakhawn a pha uh vaengah vaito loh a soek uh hatah Pathen kah thingkawng te Uzzah loh a cuk thil tih a tuuk.
Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
7 Te vaengah BOEIPA kah a thintoek te vik sai. Te dongah Uzzah te Pathen loh pahoi a ngawn. A lolhnah a om dongah Pathen kah thingkawng taengah pahoi duek.
Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
8 BOEIPA loh Uzzah puut te a va dongah David lungoe. Te dongah tekah hmuen te ti hnin due Perezuzzah la a khue.
Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
9 Te khohnin vaengah David loh BOEIPA te a rhih coeng tih, “BOEIPA kah thingkawng loh kai taengah ha pawk thai aya?” a ti.
Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
10 BOEIPA thingkawng te David khopuei ah amah taengla khuen ham David loh huem pawh. Tedae David loh Ghitti Obededom im la a thak.
Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
11 BOEIPA thingkawng tah Ghitti Obededom im ah hla thum yalh. Te vaengah Obededom neh a imkhui pum Te BOEIPA loh yoe a then sak.
Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
12 Te dongah manghai David taengla puen uh tih, “BOEIPA loh Pathen kah thingkawng kongah Obededom imkhui neh a taeng om boeih te yoe a then sak,” a ti nah. Te daengah David Te suntla tih Pathen thingkawng te Obededom im lamloh David Khopuei la kohoenah neh a khuen.
To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
13 BOEIPA thingkawng aka kawt rhoekTe kan rhuk a kan phoeiah tah vaito a puetsuet te a ngawn thil.
Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
14 David khaw a sarhi boeih neh BOEIPA mikhmuh ah lam. Te vaengah David loh takhlawk hnisui te a vah.
Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
15 David neh Israel imkhui tom loh BOEIPA thingkawng te tamlung neh, tuki ol neh a caeh puei uh.
yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
16 BOEIPA thingkawng Te David khopuei khuila a pawk vaengah Saul canu Mikhal loh bangbuet lamkah a dan. Te vaengah BOEIPA mikhmuh ah manghai David soipet tih a lam te a hmuh. Te dongah anih te a lungbuei khuiah a sawtsit.
Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
17 BOEIPA thingkawng te David loh a tuk dap khui la a khuen uh tih amah hmuen ah a khueh uh. Te phoeiah hmueihhlutnah neh rhoepnah hmueihTe David loh BOEIPA mikhmuh ah a khuen.
Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
18 Hmueihhlutnah neh rhoepnah hmueih a tloeng te a coeng phoeiah tah pilnam te David loh caempuei BOEIPA ming neh yoethen a paek.
Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
19 Israel hlangping boeih khuikah pilnam boeih te huta khaw tongpa khaw, hlang pakhat rhip taengah, vaidam laep, buhham neh maehcaeng pakhat, yukhap rhip a tael. Te phoeiah pilnam boeih te amah im la boeih cet uh.
Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
20 A imkhui te yoethen paek ham David a mael vaengah Saul canu Mikhal Te David doe ham ha thawn uh tih, “Israel manghai tihnin ah bahoeng a thangpom a! A salnu salpa mikhmuh ah tihnin ah a hni a pit he, a hong bangla a hni a pit khaw a pit rhoe he,” a ti nah.
Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
21 David loh Mikhal te BOEIPA mikhmuh ah, “Kai he tah na pa lakah khaw, a imkhui boeih lamkah long khaw amah long ni n'tuek. Kai he BOEIPA kah pilnam so neh, Israel soah rhaengsang la ng'uen dongah BOEIPA mikhmuh ah ka luem ni ta.
Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
22 He lakah muep ka tahoeng vetih ka mikhmuh ah tlarhoel la ka om ni. Tedae salnu na thui rhoek long te kai n'thangpom bitni,” a ti nah.
Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
23 Te dongah Saul canu Mikhal tah a dueknah hnin hil a taengah camoe om pawh.
Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.

< 2 Samuel 6 >