< 1 Samuel 13 >

1 Saul a manghai kum neh Israel soah kum nit a manghai nen tah,
Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
2 Israel hlang thawng thum te Saul loh amah ham a coelh. Te vaengah Mikmash kah Saul taeng neh Bethel tlang ah a thawng thawng om uh tih Benjamin Gibeah kah Jonathan taengah khaw a thawng thawng la om uh. Pilnam hlangrhuel rhoek te amah dap la boeih a tueih.
Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
3 Geba kah Philisti khohung te Jonathan loh a tloek tih Philisti rhoek loh a yaak uh. Te dongah Saul loh kho takuem ah tuki a ueng tih, “Hebrew rhoek loh ya saeh,” a ti nah.
Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
4 Israel pum loh a yaak uh vaengah, “Saul loh Philisti khohung a tloek dongah Israel he Philisti ham a bo rhim coeng,” a ti uh. Te dongah pilnam khaw Gilgal kah Saul hnukah bukbuk pang uh.
Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
5 Te dongah Philisti loh Israel te vathoh thil ham, leng thawng sawmthum neh marhang caem thawng rhuk neh pilnam te tuipuei tuikaeng kah laivin yet la taai uh. Te phoeiah cet uh tih Bethaven khothoeng Mikmash ah rhaeh uh.
Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
6 Pilnam taengah lai a suk pah tih puen a cak te Israel hlang loh a hmuh vaengah pilnam tah lungko khuila, hlingpuep khuila, thaelpang khuila, hmuensang neh tangrhom khuila thuh uh.
Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
7 Hebrew rhoek khaw Gad kho kah Jordan neh Gilead la kat uh. Tedae Saul amah tah Gilgal ah om pueng tih a hnukkah pilnam boeih long tah lakueng uh.
Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
8 Te dongah a khoning bangla Samuel te hnin rhih khuiah a rhing mai a rhing mai. Tedae Samuel te Gilgal la a pawk pawt dongah pilnam khaw Saul taeng lamloh taekyak uh.
Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
9 Te dongah Saul loh, “Hmueihhlutnah neh rhoepnah te kai taengla hang khuen,” a ti nah tih hmueihhlutnah te a nawn.
Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
10 Tedae hmueihhlutnah a nawn te a khah van neh Samuel te tarha ha pawk tih anih doe ham neh uem hamla Saul te cet.
Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
11 Samuel loh, “Balae na saii?” a ti nah hatah, Saul loh, “Pilnam he kai taeng lamloh haeh coeng tih tingtunnah tue vaengah namah khaw na pawk voel pawh tila ka hmuh. Te vaengah Philisti loh Mikmash ah taai uh coeng.
Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
12 Tedae, “Philisti loh kai taengla Gilgal ah ha suntla uh pawn ni, BOEIPA maelhmai ka tong pawt ah,” ka ti dongah ka thiim uh tih hmueihhlutnah te ka nawn,” a ti nah.
sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
13 Tedae Samuel loh Saul te, “Na pavai dongah ni BOEIPA na Pathen loh nang ng'uen olpaek na tuem pawh. Na ram he BOEIPA loh Israel taengah kumhal duela a thoh pawn suidae ta.
Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
14 Tedae na ram he pai voel mahpawh. BOEIPA loh nang ng'uen te na tuem pawt dongah amah kah thinko aka tong hlang ni BOEIPA loh a toem, anih te BOEIPA loh a pilnam soah rhaengsang la a uen coeng,” a ti nah.
Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
15 Te phoeiah Samuel te thoo tih Gilgal lamloh Benjamin Gibeah la cet. Pilnam te Saul loh a soep vaengah hlang ya rhuk tluk amah taengah a om pah.
Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
16 Saul, a capa Jonathan neh a taengkah aka om pilnam loh Benjamin Geba ah a om vaengah Philisti tah Mikmash ah rhaeh.
Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
17 Te vaengah Philisti caem lamkah kutpo rhoek te, rhoi thum la coe uh tih rhoi at tah Shual kho kah Ophrah longpuei la hooi uh.
Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
18 Rhoi at te Bethhoron longpuei la hooi uh tih rhoi at te kolrhawk la aka dan khosoek rhi kah longpuei la hooi uh.
Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
19 Te vaengah Israel kho tom ah kutthai ana om pawt hatah Philisti loh, “Hebrew te cunghang khaw, caai khaw saii uh phayoe ve,” a ti uh.
Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
20 Tedae a thecung neh a tuktong mai khaw, a hai neh a thecung mai khaw hlang loh a tah ham vaengah tah Philisti te Israel pum loh a suntlak thiluh.
Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
21 Tedae thecung neh tuktong khaw, thingsong pathum neh hai khaw, ciksum a ten ham koi khaw yula man la a om pah.
Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
22 Te dongah caemtloek tue a pha vaengah Saul neh Jonathan taengkah pilnam he pakhat kut dongah khaw cunghang neh caai hmu voel pawh. Tedae Saul neh a capa Jonathan taengah ah dawk hmuh la om.
A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
23 Te vaengah Philisti rhaltawt hmuen tah Mikmash lamkai la pawk coeng.
Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.

< 1 Samuel 13 >