< Mahte 19 >
1 Jesuh ngthu a pyen päng ja Kalile üngka naw cit lü Jordan mliktuia caye Judah khawa citki.
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai ya bar Galili, ya tafi yankin Yahudiya a ɗaya gefen Urdun.
2 Khyangpänu naw läk law u se Jesuh naw acuia a jah mdaw be.
Taron mutane mai yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can.
3 Pharise he a veia law u lü ami mhnüteinak am, “Khyang mat naw a khyu ia phäha pi ni se a hlüeia kcün üng a hawih vai hin mi thum üng nglawiki aw?” ti lü ami kthäh.
Waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa don su gwada shi. Suka yi tambaya suka ce, “Daidai ne mutum yă saki matarsa saboda wani dalili da kuma a kan kowane dalili?”
4 Jesuh naw, “Akcüka jah mhnünki naw kpami ja nghnumi a jah mhnün ti hin am nami khe khawikie aw?”
Ya amsa ya ce, “Ba ku taɓa karantawa ba ne cewa, a farkon halitta, Mahalicci ‘ya yi su namiji da ta mace,’
5 Pamhnam naw ‘Kpami naw a nu ja pa jah ceh ta lü a khyua vei ngdawn se nghngih xawi cun mtisa mata kya law khai xawi’ a ti.
ya kuma ce, ‘Saboda wannan dalili, namiji zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa yă manne wa matarsa, biyun kuwa su zama jiki guda’?
6 Acunkäna, nghngiha am ni ti ni, mata kyaki. Acunakyase, Pamhnam naw a jah lu hlin khawsawm cun khyang naw käh jah mtai se,” a ti.
Ta haka, ba sa ƙara zama biyu, sai dai ɗaya. Saboda haka abin da Allah ya haɗa fa, kada mutum yă raba.”
7 Pharise he naw, “Am ani üng ivaia Mosi naw ngkyanaka kca pe u lü hawih vaia a jah mtheh ni,” ami ti.
Suka yi tambaya, suka ce, “To, me ya sa Musa ya umarta cewa mutum yă ba wa matarsa takardar saki, yă kuma kore ta?”
8 Jesuh naw, “Nami mlungmthin nghlang lü mtheh am ngja uki se, Mosi naw nami khyu nami hawih vaia a ning jah mtheh ni. Cunüngpi a jah mhnünceng üng acukba am ni” a ti.
Yesu ya amsa ya ce, “Musa ya ba ku izini ku saki matanku saboda taurin zuciyarku ne. Amma ba haka yake ba daga farko.
9 Acunüng Jesuh naw, “Ka ning jah mthehki, aupi a khyu kpami kce am käh bäühma ni se akcea phäha hawih lü, khyu mah beki cun mkhyeki ni, acuna nghnumi khyu na beki pi mkhyekatki ni,” a ti.
Ina faɗa muku cewa duk wanda ya saki matarsa, sai dai a kan rashin aminci a cikin aure, ya kuwa auri wata, ya yi zina ke nan.”
10 Acunüng axüisaw he naw, “Acukba ani üng ta am khyu mah üng ni a daw hlü bawk ve,” ami ti.
Almajiran suka ce masa, “In haka yake tsakanin miji da mata, ashe, ya ma fi kyau kada a yi aure.”
11 Jesuh naw, “Ahina ngthu cun khyang naküt naw am ngaisim u. Acunüngpi, ngaisim khai hea a jah xü naw ni a mi ngaihsim hlü ve.
Yesu ya ce, “Ba kowa ba ne zai yarda da wannan magana, sai dai waɗanda aka yarda musu.
12 Avang cun a nua puk'um üngka naw käh khyuca mah khai hea a jah mhnün, avang cun khyang naw käh khyuca mah khaia ami jah pyang, avange cun Khankhaw Pea phäh animät käh khyuca mah khai hea nghnüneikie, aupi khyuca mah khaia tängki naw ngaisim se,” a ti.
Gama waɗansu bābānni ne domin haka aka haife su; waɗansu kuwa mutane ne suka mai da su haka; waɗansu kuma sun ƙi aure ne saboda mulkin sama. Duk mai iya ɗaukar wannan yă ɗauka.”
13 Jesuh naw Hnasenea khana a kut mtaih lü a jah ktaiyü pet vaia a veia jah lawpüi u se, axüisaw he naw ami jah ksenak.
Sa’an nan aka kawo yara ƙanana wurin Yesu don yă ɗibiya musu hannuwansa, yă kuma yi musu addu’a. Amma almajirai suka tsawata wa waɗanda suka kawo su.
14 Jesuh naw, “Hnasene ka veia law u se, käh jah mah ua, Khankhaw Pe cun amimia mäiha phäh ni,” a ti.
Yesu ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin sama na irin waɗannan ne.”
15 Jesuh naw hnasenea khana a kut mtaih lü acunkäna akcea citki.
Sa’ad da ya ɗibiya musu hannuwansa, sai ya tafi abinsa.
16 Khyang mat law lü, “Saja aw, khankhawa angsäi xünnak ka yah vaia akdaw i ja ka pawh kawm?” ti se, (aiōnios )
To, fa, sai ga wani ya zo wurin Yesu ya tambaye shi ya ce, “Malam, wane abu mai kyau ne ya zama mini dole in yi don in sami rai madawwami?” (aiōnios )
17 Jesuh naw, “I dawki ti ivai na na kthähki ni? Dawki ta mat däk ni a ve. Angsäi xünnak na yah hlü üng ngthumkhäne jah läklama” a ti.
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake tambayata game da abin da yake mai kyau? Akwai Mai kyau Ɗaya kaɗai. In kana so ka sami rai madawwami, ka kiyaye dokokin nan.”
18 Cawngpyang naw, “Ia ngthumkhäne ni? a ti. Jesuh naw, “Khyang käh na hnim vai, khyanga khyuca käh na mkhyekatnak vai, käh na mpyuk vai, käh na hleihlak vai,”
Mutumin ya yi tambaya ya ce, “Waɗanne?” Yesu ya amsa ya ce, “‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar ƙarya,
19 Na nu ja na pa na jah leisawng vai, namät naw namät na jawngnaka mäiha na impei loceng na jawngnak vai,” a ti,
ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ka kuma ‘ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
20 Cawngpyang naw, “Ahin he cun ka dikca üngkhyüh ka jah läk päih ni, i ka pawh ham khai ni?” a ti.
Saurayin ya ce, “Duk waɗannan na kiyaye. Me kuma ya rage mini?”
21 Jesuh naw, “Na kümkawi vai na ngai üng, cit lü na tak naküt jawi lü sih mpyaki he üng ngui na jah yet vai. Acunüng khana na khawh vai ve khai, acunkäna na läk law kawpi,” a ti.
Yesu ya amsa ya ce, “In kana so ka zama cikakke, ka je, ka sayar da dukan dukiyarka ka kuma ba matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo, ka bi ni.”
22 Cawngpyang naw acun a ngjak üng, pukse lü akcea citeiki. Isetiüng ani cun bawimangkia kyaki.
Da saurayin ya ji haka, sai ya tafi rai a ɓace, don yana da arziki sosai.
23 Acunüng Jesuh naw axüisaw he üng, “Akcanga ka ning jah mthehki, bawimangki hin Khankhaw Pe a luh vai aktäa küi ve,”
Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Gaskiya nake gaya muku, yana da wuya mai arziki yă shiga mulkin sama.
24 Bawimangki Pamhnama Khaw a luha kthaka ta sanghngüksaü mpyüma nghnga khuia a luh vai jä bawki ni,” a ti.
Har wa yau ina gaya muku, zai fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
25 Axüisawe naw ami ngjak üng aktäa müncan u lü, “Acunüng u naw küikyannak yah khawh khai ni?” ti lü ngthähkie.
Sa’ad da almajiran suka ji wannan, sai suka yi mamaki ƙwarai. Suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
26 Jesuh naw jah teng lü, “Ahin cun khyanga phäha i am thawn thei lü pi Pamhnama phäha am thawn theiki am ve” a ti.
Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba ya yiwuwa, amma ga Allah kuwa, dukan abubuwa masu yiwuwa ne.”
27 Acunüng Pita naw, “Tenga ahmäi naküt hawih lü kami ning läk lawki, kami ning läk law phäha i kami ngmangnak khai ni?” a ti.
Sai Bitrus ya amsa masa, “Ga shi mun bar kome don mu bi ka! Me za mu samu ke nan?”
28 Jesuh naw, “Akcanga ka ning jah mthehki, Tuha Khyanga Capa amäta hlüngtainak ja a bawingawhnak üng a ngawh law üng, nami na läk hlükie pi bawingawhnak xaleinghngih üng ngaw hnga u lü, Isarel paca xaleinghngih nami jah uk khai,”
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, a lokacin sabunta dukan kome, sa’ad da Ɗan Mutum ya zauna a kan kursiyinsa mai daraja, ku da kuka bi ni, ku ma za ku zauna a kan kursiyoyi goma sha biyu, kuna yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
29 Aupi keia ngminga phäh a ima pi kyase, a bena cinae pi kyase, a nu pa pi kyase, a ca hea pi kyase, a khawmdeka pi kyase, jah ceh taki cun acun kän cima aphya kthaka yah be lü, angsäi xünnak pi yah khai. (aiōnios )
Duk kuma wanda ya bar gidaje ko’yan’uwa maza ko’yan’uwa mata ko mahaifi ko mahaifiya ko yara ko gonaki, saboda ni, zai sami abin da ya fi haka riɓi ɗari, yă kuma gāji rai madawwami. (aiōnios )
30 Acunsepi akmae hnu u lü akhnuae ma law khaie,” ti lü a jah mtheh.
Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, da yawa kuma da suke na ƙarshe, za su zama na farko.