< Mahte 14 >

1 Acun k'um üng Kalile Upki Herod naw Jesuha mawng cun ngja lü,
A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
2 a khyang he üng, “Ani cun Baptican Johan ni, thihnak üngka naw tho beki, acunakyase ni müncanksee jah pawhnak khawha johit taki,” a ti.
sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”
3 Herod naw Johan cun man lü, a na Philipa khyu Herodiha phäha thawngim üng ahlana a khyuma kyaki.
To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus,
4 Johan naw Herod üng, “Na naa khyu na khyunak vai ta am nglawiki ni,” a tia phäha kyaki.
gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.”
5 Herod naw Johan hnim hlüki kyaw Judah khyang he a jah kyüh. Isetiakyaküng Johan cun Judah khyang he naw sahmaa ami ngaiha kyaki.
Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.
6 Heroda hminaka mhnüp üng, Herodiha canu cun Herod ja a khinea maa nglamki. Herod amsüma jeki.
A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai,
7 “Ka ng’yünki, na hlüei na tä naküt ka ning pe khai” ti lü Herod naw Herodiha canu üng bekhüt a pet.
har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
8 A nu naw a cüka kba nglaca cun naw, “Mlikbe üng Baptican Johana lu na pea!” a ti.
Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.”
9 Sangpuxang cun pukseki, cunüngpi a khinea maa a khyütama pänga kyase nglacaa hlüei cun ami pawh vaia a jah mtheh.
Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa
10 Acunüng thawngima khyang tüih lü Johana lu a khyüngsak.
ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku.
11 Johana lu cun mlikbe üng lawpüi lü nglaca üng pe u se, nglaca naw a nua veia a cehpüi.
Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta.
12 Johana hnükläke law u lü a yawk cehpüi lü, k’utkie naw Jesuh üng ami va mtheh.
Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.
13 Jesuh naw Johana mawng a ngjak üng, mlawng am ngcum lü ahinak mawkpyawnga citki. Acun ngjaki khyang he naw ami mlüh jah hawih hüt lü ami khaw am läki he.
Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa.
14 Mlawng üngka naw a kyum law üng Jesuh naw khyangpänu jah hmuh lü jah mpyeneiki, am phetkie a jah mdaw be.
Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.
15 Khaw a mü law hlü üng axüisaw he a veia law u lü, “Ahin hin maw ni, khaw pi mthan hnühki ni. Khyang he hin jah tüiha, ami ei vai ngnamea ami ei phäh phäh vai khyäiei hü u se” ami ti.
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
16 Jesuh naw, “Athuknaka ami ceh vai am hlü, nangmi naw ami ei vai aipi jah pe ua,” a ti.
Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
17 Amimi naw, “Muk mhma ja nga nghngihca däk ni kami tak ve u,” ti u se,
Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
18 Acunüng Jesuh naw, “Ka veia lawpüi ua,” a ti.
Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
19 Khyang he cun msaia khana ngaw khai hea a jah mtheh. Acunkäna muk mhma ja nga nghngih cun jah lo lü khana mang lü Pamhnam üng jenak mthehki. Muke cun jah bo lü axüisaw he üng a jah pet. A axüisaw he naw khyang he üng ami jah pet.
Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane.
20 Avan naw ei lü phü u se, ami ei k’hläi cun axüisaw he naw ami mcun be üng cä xaleinghngiha lawki.
Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
21 Eikie naküt cun nghnumi ja hnasen am pakia, kpami däk thawngmhma lawki he.
Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.
22 Acunüng Jesuh naw khyang he a jah tüih be käna, axüisaw he cun mlawng üng cayea a jah na cehsak.
Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron.
23 Acukba khyang he a jah tüih be päng üng, amätca mcunga ktaiyü khaia kaiki. Khaw mü law se, amät däk acuia veki.
Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai,
24 Acunüng mlawng cun kawng üngka naw a thuknak tuili nglunga ve se tuingnawk naw a ceh hü.
jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.
25 Khaw athaih law hlü üng, Jesuh tuia khana a khaw am axüisaw hea veia lawki.
Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin.
26 Axüisawe naw tuia khana a law ami hmuh üng kyühei law u lü, “Hin hin ngmüimkhya ni,” ti u lü ngpyangkie.
Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”
27 Jesuh naw, “Käh kyüei ua, Kei ni,” a ti.
Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
28 Pita naw msang lü, “Bawipa aw, nang na ni üng, tuia khana ka law hnga khaia na mtheha,” a ti.
Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”
29 “Lawa,” Jesuh naw a ti. Acunüng Pita mlawng üngka naw kco law lü Jesuha veia cit khaia tuia khana citki.
Ya ce, “Zo.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu.
30 Acunüngpi khawa khi law a hmuh üng kyühei lü tui üng ju ngcumei lü, “Bawipa aw, na küikyana,” ti lü ngpyang se,
Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
31 Jesuh naw man be lü, “Jumeinak ngcekia khyang aw, ivaia na mlung uplatki ni” a ti.
Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”
32 Mlawng üng ani kai be ja khawkhi ngdüm beki.
Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta.
33 Mlawnga k’uma veki axüisaw he naw hjawkhah law u lü, “Nang hin Pamhnama Capa na kya kcangki ni,” ami ti.
Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”
34 Tuili cayea va pek u lü Kenesaret hnea lawki he.
Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret.
35 Acuia ka khyang he naw Jesuh ami ksing üng, acuna pipei üngkae pe naküt üng khyang he jah tüih hü u lü am phetkie naküt ami jah lawpüi u.
Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu
36 A suisak mdawngca hman hneh vaia nghuinakie, acunüng, aupi hneki naküt cun phet bekie.
suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.

< Mahte 14 >