< Неемия 6 >
1 А Санавалат, Товия, арабинът Гисам, и останалите от неприятелите ни, като чуха, че съм бил заградил стената, и че не останало вече пролом в нея, ако и да не бях поставил врати на портите до онова време,
Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
2 Санавалат и Гисам пратиха до мене да кажат: Дойди, нека се срещнем в едно от селата на Оновото поле. Но те възнамеряваха да ми сторят зло.
Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
3 И пратих им човеци да кажат: защо да се спира работата като я оставя и сляза при вас?
saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
4 И пращаха до мене четири пъти по същия начин: но аз им отговарях все така.
Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
5 Тогава за пети път Санавалат прати слугата си до мене по същия начин с отворено писмо в ръката му,
Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
6 в което бе писано: Слух се носи между народите, пък и Гисам казва, че ти и юдеите мислите да се подигнете, за която причина ти и градиш стената; и, според тия думи, ти искаш да им станеш цар.
wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
7 Назначил си още и пророци да разгласяват за тебе в Ерусалим, като казват: Цар има в Юда. И сега ще се извести на царя според тия думи. Дойди сега, прочее, и нека се съветваме заедно.
har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
8 Тогава пратих до него човеци да кажат: Няма такова нещо каквото ти казваш; но ти ги измислюваш от себе си.
Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
9 Защото те всички искаха да ни плашат, казвайки: Ръцете им ще ослабнат от работата, та няма да се свърши. А сега, о Боже, подкрепи Ти ръцете ми.
Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
10 Тогава аз отидох в къщата на Самаия син на Делаия, Метавеиловия син, който бе затворен; и той ми каза: Нека се срещнем в Божия дом, всред храма, и нека затворим вратите на храма; защото тия идат да те убият, да! тая нощ ще дойдат да те убият.
Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
11 Но аз казах: Човек като мене бива ли да бяга? и кой човек като мене би влязъл в храма за да избави живота си? Не ща да вляза.
Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
12 И познах, че, ето, Бог не бе го пратил; но той от себе си произнесе това пророчество против мене, и Товия и Санавалат бяха го подкрепили.
Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
13 С тая цел бе подкупен, да се уплаша та да направя така, и да съгреша, и те да имат причина, да злословят, за да ме укорят.
An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
14 Спомни си, Боже мой, за Товия и Санавалат според тия техни дела, още и за пророчицата Ноадия и за други пророци, които искаха да ме плашат.
Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
15 Така се свърши стената на двадест и петия ден от месец Елул, за петдесет и два дни.
Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
16 И когато чуха това всичките ни неприятели, тогова всичките езичници около нас се уплашиха, и много се снишиха пред своите очи, защото познаха, че това дело стана от нашия Бог.
Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
17 При това, в ония дни Юдовите благородни пращаха често писма до Товия, и писма от Товия дохождаха до тях.
A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
18 Защото в Юда имаше мнозина, които се бяха заклели да му бъдат привързани, понеже бе зет на Сехания Араховия син, и син му Иоанан бе взел за жена дъщеря на Месулама Варахиевия син.
Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
19 Още и приказваха пред мене за неговите благодеяния, а моите думи носеха нему. И Товия пращаше писма за да уплаши.
Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.