< Йов 9 >

1 А Иов в отговор рече:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Наистина зная, че това е така, Но как ще се оправдае човек пред Бога?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 Ако поиска да се съди с Него, Не може да му отговори за едно от хиляда.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Мъдро сърце и мощна сила има Бог; Кой, като е упорствувал против Него, е благоденствувал?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 Той премества планините и те не усещат Когато ги е превърнал в гнева Си.
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 Той поклаща земята от мястото й, Тъй щото и стълбовете й треперят.
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 Той заповядва на слънцето, и не изгрява; И туря под печат звездите.
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 Той сам простира небесата, И стъпва на морските вълни.
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 Той прави съзвездията - Мечката, Ориона и Плеядите, И скритите пространства на юг.
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 Той прави велики и неизследими дела. И безбройни чудеса.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Ето, минава край мене, и не Го виждам; Преминава и не Го съглеждам;
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Ако грабна плячка, кой ще Му забрани? Кой ще Му рече: Що правиш?
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 Ако Бог не оттегли гнева Си, Горделивите помощници се повалят под Него!
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 Колко по-малко бих могъл аз да Му отговоря И да избера думите си, за да разисквам с Него!
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 Комуто, и праведен ако бях, не можех отговори, Но щях да повярвам, че е послушал гласа ми.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Ако извиках, и ми отговореше, Не щях да повярвам, че е послушал гласа ми.
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 Защото ме смазва с вихрушка, И умножава раните ми без причина.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 Не ме оставя да си отдъхна, Но ме насища с горчивини.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 Ако е дума за силата на мощните; Ето ме! Би казал Той; И ако за съд, би казал: Кой ще Ми определи време да съдя?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Даже ако бях праведен, осъдили ме биха собствените ми уста; Ако бях непорочен, Той би ме показал опърничав.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 Макар да бях непорочен, не бих зачитал себе си, Презрял бих живота си.
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 Все едно е; затова казвам: Той погубва и непорочния и нечестивия,
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 Ако бичът Му убива внезапно, Той се смее при изпитанията на невинните.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 Земята е предадена в ръцете на нечестивите; Той покрива лицата на съдиите; Ако не, тогава кой е, който прави това?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 А моите дни са по-бързи от бързоходец; Бягат без да видят добро;
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 Преминаха като леки кораби, Като орел, който се спуща върху лова.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 Ако река: Ще забравя оплакването си, Ще оставя желанието си, и ще се утеша.
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 В ужас съм от всичките си скърби Зная, че Ти няма да ме имаш за невинен;
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 Нечестив ще се считам; Защо, прочее, да се трудя напразно?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 Ако се умия със снежна вода, И очистя със сапун ръцете си,
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 Ти пак ще ме хвърлиш в тинята, Така щото и самите ми дрехи ще се гнусят от мене.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 Защото Той не е човек, както съм аз, та да Му отговоря И да дойдем заедно на съд.
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 Няма посредник помежду ни, Който да тури ръката си върху двама ни,
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Нека оттегли от мене тоягата Си, И ужасът Му да не ме уплашва.
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 Тогава ще говоря, и няма да се боя от Него; Защото в себе си не съм така уплашен.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Йов 9 >