< Йов 33 >
1 Затова, Иове, чуй сега словото ми, И слушай всичките мои думи.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Ето, сега отворих устата си, Езикът ми с устата ми говори.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 Думите ми ще бъдат според правотата на сърцето ми, И устните ми ще произнесат чист разум.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 Духът Божии ме е направил, И дишането на Всемогъщия ме оживотворява.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Ако можеш, отговори ми; Опълчи са с думите си пред мене та застани.
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Ето, и аз съм пред Бога както си ти, - И аз съм от кал образуван.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Ето, моят ужас няма да те уплашва. Нито ще тежи ръката ми върху тебе.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 Безсъмнено ти си говорил, като слушах аз, И аз чух гласа на думите ти, като казваше:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 Чист и без престъпление съм; Невинен съм, и баззаконие няма в мене;
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 Ето, Бог намира причини против мене, Счита ме за Свой неприятел;
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 Туря нозете ми в клада, Наблюдава всичките ми пътища.
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Ето, в това ти не си прав; Ще ти отговоря, че Бог е по-велик от човека.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Защо се препираш с Него, Загдето Той не дава отчет ни за едно от Своите дела?
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 Защото сигурно Бог говори веднъж и дваж, Само че човекът не внимава.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 В сън, в нощно видение, Когато дълбок сън напада човеците, Когато сънуват на леглата си,
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 Тогава Той отваря ушите на човеците, И запечатва поука в тях,
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 За да отвърне човека от намерението му, И да извади гордостта из човека;
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 Предпазва душата му от гроба, И животът му, за да не падне от меч.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Той бива е наказван с болки на леглото си, Да! С непрестанни болки в костите си,
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 Така щото душата му се отвръща от хляб, И сърцето му от вкусното ястие.
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 Месата му се изнуряват тъй, че не се виждат, А невидимите му по-преди кости се подават.
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 Да! Душата му се приближава при гроба. И животът му при погубителите,
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 Тогава, ако има ангел с него, Посредник, пръв между хиляда, За да възвести на човека що е за него право,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 И ако Бог му бъди милостив И рече: Избави го, за да не слезе в гроба, Аз промислих откуп за него,
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 Тогава месата му ще се подмладяват повече от месата на дете? Той се връща в дните на младостта си;
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 Ако се помоли Богу, Той е благосклонен към него, И му дава да гледа лицето Му с радост; И възвръща на човека правдата му.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 Той пее пред човеците, казвайки: Съгреших и изкривих правото, И не ми се въздаде според греха ми;
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 Той избави душата ми, за да не отиде в рова; И животът ми ще види виделината.
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Ето всичко това върши Бог Дваж и триж с човека,
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 За да отвърне душата му от рова, Но да се просвети с виделината на живота.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Внимавай, Иове, послушай ме, Мълчи, и аз ще говоря.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Ако имаш какво да кажеш, отговори ми; Говори, защото желая да бъдеш оправдан;
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 Но ако не, то ти слушай мене; Мълчи, и ще те науча мъдрост.
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”