< Исая 42 >
1 Ето Моят служител, когото подкрепявам, Моят избраник, в когото благоволи душата Ми; Турих Духа Си на него; Той ще постави правосъдие за народите.
“Ga bawana, wanda na ɗaukaka, zaɓaɓɓen nan nawa wanda nake jin daɗi; Zan sa Ruhuna a cikinsa zai kuwa kawo adalci ga al’ummai.
2 Няма да извика, нито ще издигне високо гласа си, Нито ще го направи да се чуе навън.
Ba zai yi ihu ko ya tā da murya, ko ya daga muryarsa a tituna ba.
3 Смазана тръстика няма да пречупи, И замъждял фитил няма да угаси; Ще постави правосъдие според истината.
Iwan da ta tanƙware ba zai karye ba, ba zai kashe lagwani mai hayaƙi ba. Cikin aminci zai kawo adalci;
4 Няма да ослабне нито да се съкруши Догдето установи правосъдие на земята; И островите ще очакват неговата поука.
ba zai kāsa ko ya karai ba sai ya kafa adalci a duniya. Cikin dokarsa tsibirai za su sa zuciya.”
5 Така казва Бог, Господ, Който е направил небето и го е разпрострял, Който е разтлал земята с произведенията й, Който дава дишане на людете, които са на нея, И дух на тия, които ходят по нея:
Ga abin da Allah Ubangiji ya ce, shi da ya halicci sammai ya kuma miƙe su, wanda ya shimfiɗa duniya da dukan abin da ya fito cikinta, wanda ya ba wa mutanenta numfashi, da rai ga waɗanda suke tafiya a kanta.
6 Аз Господ те призовах в правда, И като хвана ръката ти ще те пазя, И ще те поставя за завет на людете, За светлина на народите,
“Ni Ubangiji, na kira ka cikin adalci; zan riƙe hannunka. Zan kiyaye ka in kuma sa ka zama alkawari ga mutane haske kuma ga Al’ummai,
7 За да отвориш очите на слепите, Да извадиш запрените от затвор, И седящите в мрак из тъмницата.
don ka buɗe idanun makafi ka’yantar da kamammu daga kurkuku kuma kunce ɗaurarrun kurkuku masu zama cikin duhu.
8 Аз съм Господ; това е Моето име; И не ща да дам славата Си на друг, Нито хвалата Си на изваяните идоли.
“Ni ne Ubangiji; sunana ke nan! Ba zan ba da ɗaukakata ga wani ba ko yabona ga gumaka.
9 Ето, нещата, предсказани от начало се сбъднаха, И Аз ви известявам нови, Преди да се появят, казвам ви ги.
Duba, abubuwan da sun tabbata, sababbin abubuwa kuwa nake furtawa; kafin ma su soma faruwa na sanar da su gare ku.”
10 Пейте на Господа нова песен, Хвалата Му от краищата на земята, Вие, които слизате на морето и всичко що е в него, Острови, и вие, които живеете на тях.
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, ku yi yabonsa daga iyakar duniya, ku da kuka gangara zuwa teku, da kome da yake cikinsa, ku tsibirai, da waɗanda suke zama a cikinsu.
11 Пустинята и градовете й нека извикат с висок глас, Силата, гдето живее Кидар; Нека пият жителите на Села, Нека възклицават от върховете на планините,
Bari hamada da garuruwanta su tā da muryoyinsu; bari wuraren zaman da Kedar ke zama su yi farin ciki. Bari mutanen Sela su rera don farin ciki; bari su yi sowa daga ƙwanƙolin duwatsu.
12 Нека отдадат слава на Господа, И нека възвестят хвалата Му в островите.
Bari su ɗaukaka Ubangiji su kuma yi shelar yabonsa a tsibirai.
13 Господ ще излезе като силен мъж, Ще възбуди ревнивостта Си като ратник, Ще извика, да! ще изреве. Ще надделее над враговете Си;
Ubangiji zai fita ya yi yaƙi kamar mai ƙarfi, kamar jarumi zai yi himma; da ihu zai tā da kirarin yaƙi zai kuma yi nasara a kan abokan gābansa.
14 За дълго време мълчах, казва Той. Останах тих, въздържах Себе Си; Но сега ще извикам като жена, която ражда, Ще погубя и същевременно ще погълна.
“Na daɗe ina shiru, na yi shiru na kuma ƙame kaina. Amma yanzu, kamar mace mai naƙuda, na yi ƙara, ina nishi ina kuma haki.
15 Ще запустя планини и хълмове, И ще изсуша всичката им трева; Ще обърна реките в острови, И ще пресуша езерата.
Zan lalatar da duwatsu da tuddai in busar da dukan itatuwansu; zan mai da koguna su zama tsibirai in kuma busar da tafkuna.
16 Ще доведа слепите през път, който не са знаели, Ще ги водя в пътеки, които им са били непознати; Ще обърна тъмнината в светлина пред тях, И неравните места ще направя равни. Това ще сторя, и няма да ги оставя.
Zan yi wa makafi jagora a hanyoyin da ba su taɓa sani ba, a hanyoyin da ba a saba ba zan bishe su; zan mai da duhu ya zama haske a gabansu in kuma mai da ƙasa mai kururrumai ta zama sumul. Abubuwan da zan yi ke nan; ba zan yashe su ba.
17 Ще се върнат назад, съвсем ще се посрамят Ония, които уповават на ваяните идоли, Които казват на леяните: Вие сте наши богове.
Amma waɗanda suka dogara ga gumaka, waɗanda suke ce wa siffofi, ‘Ku ne allolinmu,’ za a mai da su baya da kunya.
18 Чуите, глухи, И гледайте, слепи, за да видите.
“Ka ji, kai kurma; duba, kai makaho, ka kuma gani!
19 Кой е сляп, ако не е служителят Ми, Или глух, както посланика, когото изпращам? Кой е сляп както предания Богу, И сляп както служителя Господен?
Wane ne makaho in ba bawana ba, da kuma kurma in ba ɗan aikan da na aika ba? Wane ne makaho kamar wanda ya miƙa kai gare ni, makaho kamar bawan Ubangiji?
20 Ти гледаш много неща но не наблюдаваш; Ушите му са отворени, но той не чува.
Kun ga abubuwa masu yawa, amma ba ku kula ba; kunnuwanku suna a buɗe, amma ba kwa jin wani abu.”
21 Господ благоволи заради правдата Си Да възвеличи учението и да го направи почитаемо.
Yakan gamsar da Ubangiji saboda adalcinsa ya sa dokarsa ta zama mai girma da kuma mai ɗaukaka.
22 Но те са ограбени и оголени люде; Всички са впримчени в пещери и скрити в тъмници; Плячка са, и няма избавител, Обир са, и никой не казва: Върни го.
Amma ga mutanen da aka washe aka kuma kwashe ganima, an yi wa dukansu tarko a cikin rammuka ko kuma an ɓoye su cikin kurkuku. Sun zama ganima, babu wani da zai kuɓutar da su; an mai da su ganima, ba wanda zai ce, “Mayar da su.”
23 Кой от вас ще даде ухо на това? Кой ще внимава и слуша за бъдещето?
Wane ne a cikinku zai saurari wannan ko ya kasa kunne sosai a cikin kwanaki masu zuwa?
24 Кой предаде Якова на обир, И Израиля на грабител? Не Господ ли, на Когото съгрешихме? Защото не искаха да ходят в пътищата Му, Нито послушаха учението Му.
Wa ya ba da Yaƙub don yă zama ganima Isra’ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Ubangiji ba ne, wanda kuka yi wa zunubi? Gama ba su bi hanyoyinsa ba; ba su yi biyayya da dokarsa ba.
25 Затова изля на него лютостта на гнева Си И свирепостта на боя; И това го запали изоколо, но той не се сети, Изгори го, но той не го вложи в сърцето си.
Saboda haka ya zuba musu zafin fushinsa, yaƙi mai tsanani. Ya rufe su cikin harsunan wuta, duk da haka ba su gane ba; ya cinye su, amma ba su koyi kome ba.