< Битие 9 >

1 В това време Бог благослови Ноя и синовете му, като им каза: Плодете се, размножавайте се и напълнете земята.
Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
2 Ще се страхуват и ще треперят от вас всички земни животни и всички въздушни птици; те са всичко, що пълзи по земята и с всички земни риби са предадени в ръцете ви.
Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
3 Всичко живо, що се движи ще ви бъде за храна; давам ви всичко също, както дадох зелената трева.
Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
4 Месо обаче с живота му, тоест, с кръвта му, да не ядете.
“Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
5 А вашата кръв, кръвта на живота ви, непременно ще изискам; от всяко животно ще я изискам; и от човека, да! от брата на всеки човек, ще изискам живота на човека.
Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
6 Който пролее човешка кръв, и неговата кръв от човек ще се пролее; защото по Своя образ направи Бог човека.
“Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
7 А вие, плодете се и се размножавайте, разплодете се по земята и умножавайте се по нея.
Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
8 После Бог говори на Ноя и на синовете му с него, казвайки:
Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
9 Вижте, Аз поставям завета Си с вас и с потомството ви подир вас;
“Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
10 и всичко живо, що е с вас, - птиците, добитъкът и всичките земни животни, които са с вас, да! с всяко земно животно от всичко, което е излязло от ковчега.
da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
11 Поставям завета Си с вас, че няма да се изтреби вече никоя твар от водите на потопа, нито ще настане вече потоп да опустоши земята.
Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
12 Бог рече още: Ето белегът на завета, който Аз поставям до вечни поколения между Мене и вас и всичко живо, което е с вас:
Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
13 поставям дъгата Си в облака, и тя ще бъде белег на завет между Мене и земята.
Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
14 Когато докарам облак на земята, дъгата ще се яви в облака:
Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
15 и ще спомня завета Си, който е между мене и вас и всичко живо от всяка твар; и водата няма вече да стане потоп за изтреблението на всяка твар.
zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
16 Дъгата ще бъде в облака: и ще я гледам, за да си напомням всегдашния завет между Бога и всичко живо от всяка твар, което е на земята.
Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
17 Каза Бог на Ноя: Това е белегът на завета, който установих между мене и всяка твар, която е на земята.
Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
18 А излезлите от ковчега Ноеви синове бяха Сим, Хам и Яфет; а Хам беше баща на Ханаана.
’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
19 Тия трима бяха Ноевите синове; и от тях се насели цялата земя.
Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
20 В това време Ной почна да работи земята и насади лозе.
Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
21 като пи от виното опи се и се разголи в шатрата си.
Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
22 И Хам, Ханаановия баща, видя голотата на баща си и каза на двамата си братя отвън.
Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
23 А Сим и Яфет взеха една дреха и, като я туриха двамата на рамената си, пристъпиха заднишком та покриха голотата на баща си; лицата им гледаха назад, та не видяха бащината си голота.
Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
24 Като изтрезня Ной от виното си и се научи за онова, което му бе направил по-младият ме син, рече:
Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
25 Проклет да е Ханаан; Слуга на слуги ще бъде на братята си.
sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
26 Рече още: Благословен Господ, Симовия Бог; И Ханаан да му бъде слуга.
Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
27 Бог да разшири Яфета. И да се засели в шатрите на Сима; И Ханаан да им бъде слуга.
Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
28 И след потопа Ной живя триста и петдесет години.
Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
29 И всичките дни на Ноя станаха деветстотин и петдесет години; и умря.
Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.

< Битие 9 >