< Битие 19 >
1 Привечер дойдоха двама ангела в Содом; а Лот седеше в Содомската порта. И като ги видя, Лот стана да ги посрещне, поклони се с лице до земята и рече:
Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
2 Ето, господари мои, свърнете, моля, в къщата на слугата си, пренощувайте и си умийте нозете, и утре станете та си идете по пътя. А те рекоха: Не, на улицата ще пренощуваме.
Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
3 Но, като настояваше много, те се отбиха към него и влязоха в къщата му; и той им направи угощение и изпече безквасни хлябове; и ядоха.
Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
4 А преди да си легнат те, градските мъже, Содомските жители, млади и стари, всичките люде от всякъде, обиколиха къщата
Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
5 и викаха на Лота, казвайки: Где са мъжете, които дойдоха у тебе тая нощ? Изведи ни ги да ги познаем.
Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
6 А Лот излезе при тях пред вратата, затвори вратата след себе си, и рече:
Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
7 Моля ви се, братя мои, не правете такова нечестие.
ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
8 Вижте сега, имам две дъщери, които не са познали мъж; тях да ви изведа вън, и сторете с тях, каквото ви се вижда угодно; само на тия мъже не струвайте нищо, понеже затова са влезли по покрива на стрехата ми.
Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
9 Но те рекоха: Махни се нататък. Рекоха още: Той дойде тук самичък и пришелец, а иска още и съдия да стане; ей сега на тебе ще сторим по-голямо зло, отколкото на тях. И насилваха премного човека, Лота, и приближиха се да разбият вратата.
Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
10 Но мъжете простряха ръце, дръпнаха Лота при себе си, в къщи, и затвориха вратата.
Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
11 Тоже и поразиха със слепота човеците, които бяха пред вратата на къщата, и малък и голям, тъй щото се умориха, като търсеха вратата.
Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
12 Тогава мъжете рекоха на Лота: Имаш ли тука друг някой: зет, синове, дъщери и които и да било други, що имаш в града, изведи ги из това място;
Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
13 защото ние ще съсипем мястото, понеже силен стана викът им пред Господа, и Господ ни изпрати да го съсипем.
gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
14 И тъй, Лот излезе и говори на зетьовете си, които щяха да водят дъщерите му и рече: Станете, излезте из това място, защото Господ ще съсипе града. Но не зетьовете му се видя, че той се шегува.
Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
15 Когато се зазори, ангелите настояваха пред Лота, казвайки: Стани, вземи жена си и двете си дъщери, които са тука, за да не погинеш всред наказанието на тоя град.
Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
16 Но тоя се бавеше; затова мъжете хванаха за ръка него, жена му и двете му дъщери, изведоха го и поставиха го вън от града; понеже Господ го пожали.
Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
17 И като го изведоха вън, рече единият на Лота: Бягай за живота си; да не погледнеш назад, нито да се спреш някъде в цялата тая равнина; бягай на планината, за да не погинеш.
Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
18 А Лот им рече: Ах, Господи, не така!
Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
19 Ето, слугата ти придоби Твоето благоволение, и с опазването на живота ми, Ти правиш още по-голяма милостта, която си показал към мене; но аз не мога да побягна на планината да не би да ме постигне злато и да умра.
Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
20 Гледай, моля, твоя град е близо, за да побягна там, и малък е. Нека побягна там, (не е ли малък град?) и така животът ми ще се опази.
Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
21 Той му каза: Ето слушам те и за това нещо, че няма да разоря града, за който ти говори.
Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
22 Бързай, бягай там защото Аз не мога да сторя нищо, догде ти не стигнеш там. Затова тоя град се наименува Сигор.
Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
23 Слънцето изгряваше на земята, когато Лот влезе в Сигор.
A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
24 Тогава Господ изля върху Содом и Гомор сяра и огън от Господа от небето.
Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
25 Той разори тия градове и цялата равнина, всичките жители на градовете и земните растения.
Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
26 Но жена му, след него, погледна назад, и стана стълб от сол.
Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
27 Сутринта Авраам подрани на мястото, дето беше стоял пред Господа;
Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
28 и погледна към Содом и Гомор и към цялата земя на равнината, и, ето видя, че дим, като дим от пещ, се издигаше от земята.
Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
29 И тъй, когато Бог разоряваше градовете на тая равнина, Бог си спомни за Авраама и изпрати Лота изсред разорението, когато разори градовете, дето живееше Лот.
Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
30 А Лот излезе от Сигор и живееше в планината, и с него двете му дъщери, понеже се боеше да остане в Сигор; затова живееше в една пещера, той и двете му дъщери.
Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
31 Тогава по-старата рече на по-младата: Баща ни е стар, и няма мъж на земята да влезе при нас, според обичая на цялата земя.
Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
32 Ела, да упоим баща си с вино и да преспим с него, за да запазим потомството от баща си.
Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
33 И тъй, оная нощ упоиха баща си с вино; и по-старата влезе та преспа с баща си; а той не усети, нито кога легна тя, нито кога влезе.
A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
34 На другия ден по-старата рече на по-младата: Виж, миналата нощ аз преспах с баща си; да го упоим с вино и тая нощ, та влез ти и преспи с него, за да запазим потомството от баща си.
Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
35 И тъй, оная нощ упоиха баща си с вино, и по-младата влезе та преспа с него; а той не усети нито кога легна тя, нито кога стана.
Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
36 Така и двете лотови дъщери зачнаха от баща си.
Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
37 И по-старата роди син и го наименува Моав; той е до днес отец на моавците.
’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
38 Роди и по-младата син и го наименува Бен-ами; той е и до днес отец на амонците.
’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.