< 2 Летописи 25 >

1 Амасия бе двадесет и пет години на възраст когато се възцари, и царува двадесет и девет години в Ерусалим. И името на майка му бе Иодана, от Ерусалим.
Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
2 Той върши това, което бе право пред Господа, но не със съвършено сърце.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
3 А като му се утвърди царството, той умъртви слугите си, които бяха убили баща му царя.
Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
4 Но чадата им не умъртви, според писаното в закона на Моисеевата книга, гдето Господ заповядвайки, каза: Бащите да не умират поради чадата, нито чадата да умират поради бащите; но всеки да умира за своя грях.
Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
5 Тогава Амасия събра Юда и постави от тях хилядници и стотници, според бащините им домове, по целия Юда и Вениамин; и като ги преброи от двадесет години и нагоре, намери ги триста хиляди отборни мъже, способни да излизат на война, които можеха да държат копие и щит.
Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
6 А от Израиля нае още сто хиляди силни и храбри мъже за сто таланта сребро.
Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
7 А дойде един Божий човек при него и рече: Царю, да не отиде с тебе Израилевата войска; защото Господ не е с Израиля, с никой от ефремците.
Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
8 Но ако си решил да идеш, действувай храбро, укрепи се за бой; иначе, Бог ще те направи да паднеш пред неприятеля, защото Бог има сила да помага и да сваля.
Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
9 А Амасия рече на Божия човек: Но какво да направим за стоте таланта, които дадох на Израилевата войска? А Божият човек отговори: Господ може да ти даде повече от това.
Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
10 Тогава Амасий ги отдели, то ест, войската, която му беше дошла от Ефрема, за да се върнат у дома си; по която причина гневът им пламна силно против Юда, и се върнаха у дома си твърде разярени.
Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
11 А Амасия се одързости, изведе людете си, и отиде в долината на солта, та порази десет хиляди от Сиировите потомци.
Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
12 А други десет хиляди юдейците плениха живи, и като ги закараха на върха на скалата, хвърлиха ги долу от върха на скалата, така че всичките се смазаха.
Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
13 Но мъжете от войската, която Амасия върна надире, за да не идат с него на бой, нападнаха Юдовите градове, от Самария дори до Ветерон, та поразиха от тях три хиляди души, и взеха много користи.
Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
14 А Амасия, като се върна от поразяването на едомците, донесе боговете на Сиировите потомци та ги постави богове за себе си, кланяше се пред тях, и кадеше им тамян.
Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
15 Затова, гневът на Господа пламна против Амасия, и прати при него пророк, който му рече: Защо си прибягнал към боговете на тия люде, които не можеха да избавят своите си люде от ръката ти?
Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
16 А като му говореше той, царят му каза: Съветник ли те поставиха на царя? Престани: защо да бъдеш убит? И пророкът престана, като рече: Зная, че Бог е решил да те изтреби понеже ти стори това, и не послуша моя съвет.
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
17 Тогава Юдовият цар Амасия, като се съветва, прати до Израилевия цар Иоас, син на Иоахаза, Ииуевия син, да кажат: Дойди да се погледнем един друг в лице.
Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
18 А Израилевият цар Иоас прати до Юдовия цар Амасия да рекат: Ливанският трън пратил до ливанския кедър да кажат: Дай дъщеря си на сина ми за жена. Но един звяр, който бил в ливан, заминал та стъпкал тръна.
Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
19 Ти казваш: Ето, поразих Едома; и сърцето ти те надигна да се хвалиш. Седи сега у дома си; защо да се заплиташ за своята си вреда та да паднеш, ти и Юда с тебе?
Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
20 Но Амасия не послуша; защото от Бога бе това, за да ги предаде в ръката на неприятелите, понеже бяха прибегнали към Едомските богове.
Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
21 Прочее, Израилевият цар Иоас възлезе, та се погледнаха един друг в лице, той и Юдовият цар Амасия, във Ветсемес, който принадлежи на Юда.
Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
22 И Юда биде поразен пред Израиля; и побягнаха всеки в шатъра си.
Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
23 И Израилевият цар Иоас хвана във Ветсемес Юдовия цар Амасия, син на Иоаса, Иоахазовия син и го доведе в Ерусалим, и събори четиристотин лакътя от Ерусалимската стена, от Ефремовата порта до портата на ъгъла.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
24 И като взе всичкото злато и сребро, и всичките съдове, които се намираха в Божия дом при Овидедома, и съкровищата на царската къща, тоже и заложници, върна се в Самария.
Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
25 А след смъртта на Израилевия цар Иоас, Иоахазовият син, Юдовият цар Амасия, Иасовият син, живя петнадесет години.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
26 А останалите дела на Амасия, първите и последните, ето, написани са в Книгата на Юдовите и Израилевите царе.
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 А след като се отклони Амасия от Господа, направиха заговор против него в Ерусалим, и той побягна в Лахис; но пратиха след него в Лахис та го убиха там.
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28 И докараха го на коне та го погребаха с бащите му в Юдовия столичен град.
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.

< 2 Летописи 25 >