< 1 Коринтяни 2 >

1 И аз, братя, когато дойдох при вас, не дойдох с превъзходно говорене или мъдрост да ви известя Божията тайна;
Da na zo wurinku’yan’uwa, ban zo da iya magana ko wani mafificin hikima yayinda na yi muku shelar shaida game da Allah ba.
2 защото бях решил да не зная между вас нещо друго, освен Исуса Христа, и то Христа (Гръцки: Него. ) разпнат.
Don na ƙudura a raina sa’ad da nake tare da ku cewa ba zan mai da hankali ga kome ba sai dai Yesu Kiristi wanda aka gicciye.
3 Аз бях немощен между вас, страхувах се и много треперех.
Na zo wurinku cikin rashin ƙarfi da tsoro, da rawan jiki ƙwarai.
4 И говоренето ми, и проповядването ми не ставаха с убедителните думи на мъдростта, но с доказателство от Дух и от сила;
Saƙona da wa’azina ba su zo cikin hikima da kalmomin lallashi ba, sai dai da nuna ikon Ruhu,
5 за да бъде вярването ви основано не на човешка мъдрост, а на Божията сила.
domin kada bangaskiyarku ta dogara a kan hikimar mutane, sai dai a kan ikon Allah.
6 Обаче, ние поучаваме мъдрост между съвършените, ала не мъдрост от тоя век, нито от властниците на тоя век, които преминават; (aiōn g165)
Duk da haka, muna sanar da saƙon hikima cikin waɗanda suka balaga, amma ba hikima irin ta wannan zamani ba ne, ko kuwa irin ta masu mulkin zamanin nan, waɗanda za su shuɗe ba. (aiōn g165)
7 но поучаваме Божията тайнствена премъдрост, която е била скрита, която е била предопределена от Бога преди вековете да ни докарва слава. (aiōn g165)
A’a, muna magana ne a kan asirin hikimar Allah, hikimar da tun dā, take a ɓoye, wadda Allah ya ƙaddara domin ɗaukakarmu, tun kafin farkon zamanai. (aiōn g165)
8 Никой от властниците на тоя век не я е познал; защото, ако я бяха познали, не биха разпнали Господа на славата. (aiōn g165)
Ba ko ɗaya daga cikin masu mulkin wannan zamani da ya fahimce ta, gama da a ce sun fahimce ta, da ba su gicciye Ubangiji mai ɗaukaka ba. (aiōn g165)
9 А, според както е писано:
Duk da haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Ba idon da ya taɓa gani, ba kunnen da ya taɓa ji, ba kuma zuciyar da ta taɓa tunanin abin da Allah ya shirya wa masu ƙaunarsa.”
10 А на нас Бог откри това чрез Духа; понеже Духът издирва всичко, даже и Божиите дълбочини.
Amma Allah ya bayyana mana shi ta wurin Ruhunsa. Ruhu yana bincika dukan abubuwa, har ma da abubuwa masu zurfi na Allah.
11 Защото кой човек знае що има у човека, освен духът на човека, който е в Него? Така и никой не знае що има у Бога, освен Божият Дух.
Wane ne a cikin mutane ya san tunanin mutum, in ba ruhun mutumin da yake cikinsa ba? Haka kuma ba wanda ya san tunanin Allah, sai dai Ruhun Allah.
12 А ние получихме не духа на света, но Духа, който е от Бога, за да познаем това, което Бог е благоволил да ни подари;
Ba mu karɓi ruhun duniya ba, sai dai Ruhun da yake daga Allah, domin mu fahimci abin da Allah ya ba mu hannu sake.
13 което и възвестяваме, не с думи научени от човешка мъдрост, но с думи научени от Духа, като поясняваме духовните неща на духовните човеци.
Wannan shi ne abin da muke sanarwa, ba da kalmomin da muka koya ta wurin hikimar mutum ba, amma da kalmomin da Ruhu yake koyarwa, muna faɗin gaskiya ta ruhaniya da kalmomin ruhaniya.
14 Но естествения човек не подбира това, което е от Божия Дух, защото за него е глупост; и не може да го разбере, понеже, то се изпитва духовно.
Mutumin da ba shi da Ruhu, ba ya yarda da abubuwan da suka fita daga Ruhun Allah, domin wauta ce a gare shi. Ba kuwa zai fahimce su ba, domin ta Ruhu ne ake fahimtarsu.
15 Но духовният човек изпитва всичко; а него никой не изпитва.
Mutumin ruhaniya yakan gwada dukan abubuwa, amma shi kansa ba ya ƙarƙashin shari’ar mutum.
16 Защото, "Кой е познал ума на Господа, За да може да го научи?" А ние имаме ум Христов.
“Wa ya taɓa sanin hankalin Ubangiji, har da zai koya masa?” Amma muna da tunani iri na Kiristi ne.

< 1 Коринтяни 2 >