< Titus 2 >

1 I wu u ka hla njaaji ilan.
Dole ka koyar da abin da yake bisa sahihiyar koyarwa.
2 Gbi bi ciche lila du mba hi he vutu bey vu sunro be toh jaji ni mi kpakyeme ni itere u Irji.
Ka koya wa tsofaffin maza su kasance masu sauƙinkai, waɗanda suka cancanci girmamawa, masu kamunkai, sahihai wajen bangaskiya, da ƙauna da kuma jimiri.
3 Na ki imba be niko be ka vutu bi bana be tere totona du bana so ima u tehuwa na.
Haka ma, ka koya wa tsofaffin mata su zama masu bangirma cikin rayuwarsu, ba masu ɓata suna ko masu jarrabar shan giya ba, sai dai su zama masu koyar da abin da yake nagari.
4 Du ba tsoro imba be tsitsama itere sunko wa balilo.
Sa’an nan za su iya su koya wa mata masu ƙuruciya su ƙaunaci mazansu da’ya’yansu,
5 Du mba hi be mlaya mba komba bata tee naki itere Irji a ni bi kerekereme.
su kasance da kamunkai da kuma tsarki, masu aiki a gida, masu kirki da kuma masu biyayya ga mazansu, don kada wani yă rena maganar Allah.
6 Na ki u ka hla imirize du mba hey be sisuron.
Haka kuma, ka ƙarfafa samari su zama masu kamunkai.
7 Ko ni konrime u ka zeren dedeme.
Cikin kowane abu ka zama musu misali mai kyau ta wurin aikata abin da yake nagari. A cikin koyarwarka ka nuna mutunci da ƙwazo
8 Hla tere be dedema. bewa bana toh itere Irji na Ishan ka temba.
da kuma sahihanci cikin maganar da ba za a iya kushewa ba, domin masu gāba da kai su ji kunya, su kuma rasa wani mugun abin da za su faɗa game da mu.
9 I miri ko mba wo tere ni tei komba ni mi kogeh mba na sunyu ni mbana.
Ka koya wa bayi su yi wa iyayengijinsu biyayya cikin kowane abu, su yi ƙoƙari su gamshe su, kada su mayar musu da magana,
10 Du ba na tee yibi na. Mba ka ji kpakyeme U Irji gbahgbah me.
kada kuma su yi musu sata, sai dai su nuna za a iya amince da su sosai, don ta kowace hanya su sa koyarwa game da Allah Mai Cetonmu ta zama abin ɗaukan hankali.
11 U imiri Irji ba toh didima wawumba.
Gama alherin Allah mai kawo ceto ya bayyana ga dukan mutane.
12 Ani hla du keh ka memetee u gbu gblu tagah. (aiōn g165)
Yana koya mana mu ce, “A’a” ga rashin tsoron Allah da kuma sha’awace-sha’awacen duniya, mu kuma yi rayuwa ta kamunkai, ta adalci da kuma ta tsoron Allah a cikin wannan zamani, (aiōn g165)
13 Keh ta zere di ta gbey tee lulu ni ze sunro u ye ivere Irji tee bu.
yayinda muke sauraron begenmu mai albarka bayyanuwar ɗaukakar Allahnmu mai girma da kuma Mai Cetonmu, Yesu Kiristi,
14 Yesu a kpa hla tere u bu ni gbu gblu da ikheu ubu wawu. na ki khi ka hu hla terema.
wanda ya ba da kansa dominmu don yă fanshe mu daga dukan mugunta yă kuma tsarkake wa kansa mutanen da suke nasa, waɗanda suke marmarin yin abin da yake nagari.
15 U ka tere ni gbe gble de tshoro ba jaji ndah na kpa u tsirina.
Waɗannan kam, su ne abubuwan da ya kamata ka koyar, ka ƙarfafa ka kuma tsawata da dukan iko. Kada ka yarda wani yă rena ka.

< Titus 2 >