+ Matiyu 1 >
1 Vuvu u Yesu Kristi ivren Dauda, ivren u Ibrahim.
Littafin asalin Yesu Almasihu Dan Dauda, Dan Ibrahim.
2 Ibrahim a ngrji Ishaku, Ishaku ka ngrji Yakubu, u Yakubu a ngrji Yahuda ni ba mrli vayi ma.
Ibrahim shine mahaifin Ishaku, Ishaku shine mahaifin Yakubu, Yakubu shine mahaifin Yahuza da 'yan'uwansa.
3 Yahuda a ngrji Perez mba Zerah ngrji u Tamar, Perez ngrji Hezron, u Hezron ngrji Ram.
Yahuza shine mahaifin Farisa da Zera, ta wurin Tamar. Farisa kuma shine mahaifin Hasruna, Hasruna kuma shine mahaifin Aram.
4 Ram ngrji Amminadah, Amminadah ngrji Nahshon, u Nahshon ngrji Salmon.
Aram shine mahaifin Amminadab, Amminadab shine mahaifin Nashon, Nashon shine mahaifin Salmon.
5 Salmon ngrji Boaz ngrji Rahab, Baoz ngrji Obadiya ngrji u Rautha, Obadiya ngrji Jesse.
Salmon shine mahaifin Bo'aza ta wurin Rahab, Bo'aza shine mahaifin Obida ta wurin Rut. Obida shine mahaifin Yesse,
6 U Jesse ngrji ichu Dauda. Ichu Dauda ngrji Suleman wa iyima ana wa Uraya
Yesse shine mahaifin sarki Dauda. Sarki Dauda shine mahaifin Sulaimanu ta wurin matar Uriya.
7 Suleman a nu ngrji Rehoboam, Rehoboam a ngrji Abijah u Abijah ngrji Asa.
Sulaimanu shine mahaifin Rehobo'am, Rehobo'am shine mahaifin Abija, Abija shine mahaifin Asa.
8 Asa ngrji Jehoshafat, Jehoshafat ngrji Joram, Joram ngrji Uzziya.
Asa shine mahaifin Yehoshafat, Yehoshafat shine mahaifin Yoram, Yoram kuma shine mahaifin Uziya.
9 Uzziya ngrji Jotham, Jotham ngrji Ahaz u Ahaz ngrji Hezekaya.
Uziya shine mahaifin Yotam, Yotam shine mahaifin Ahaz, Ahaz shine mahaifin Hezekiya.
10 Hazekaya a ngrji Manaseh, Manaseh a ngrji Amon u Amon ngrji Yosiya.
Hezekiya shine mahaifin Manassa, Manassa shine mahaifin Amon, sannan Amon shine mahaifin Yosiya.
11 Yosiya ngrji Yekoniya ni mrli vayi ma wiere me ni nton wa ba vu ba hi ni Babila.
Yosiya shine mahaifin Yekoniya da 'yan'uwansa, dai dai locacin da aka kwashe su zuwa kasar Babila.
12 U wa ba nji ye Babila, Yekoniya ngrji Shealtiel u Shealtiel ngrji Yerubabel.
Bayan kwasar su zuwa kasar Babila, Yekoniya shine mahaifin Sheyaltiyel, Sheyaltiyel shine mahaifin Zarubabel.
13 Yerubabel ngrji Abuid, Abuid ngrji Eliakim, u Eliakim ngrji Azor.
Zarubabel shine mahaifin Abihudu, Abihudu shine mahaifin Eliyakim, sannan Eliyakim shine mahaifin Azuru.
14 Azor ngrji Zadok, Zadok ngrji Achim u Achim ngrji Eliud.
Azuru shine mahaifin Saduku. Saduku shine mahaifin Akimu, sannan Akimu shine mahaifin Aliyudu
15 Eliud ngrji Eleazer, Eleazer
Aliyudu shine mahaifin Ali'azara, Ali'azara shine mahaifin Matana, sannan Matana shine mahaifin Yakubu.
16 ngrji Matthan, u Matthan ngrji Yakubu. U Yakubu ngrji Yusufu illon Maryamu wa a ngrji Yesu wa ba yo'u din Kristi.
Yakubu shine mahaifin Yusufu maigidan Maryamu, wadda ta wurin ta ne aka haifi Yesu, wanda ake ce da shi Almasihu.
17 To inzan ba wawu rji ni Ibrahim hi Dauda ba wlon don zia, rji ni Dauda hi ntton wa ba vu hi ni Babila bahi izan zia, u rji ni ni ntton u wa bahe ni Babila hi ni ye Kristi ba nzan wlon don zia.
Tun daga Ibrahim zuwa Dauda, an yi tsara goma sha hudu ne, daga Dauda zuwa lokacin da aka kwashe su zuwa Babila, tsara goma sha hudu ne, sannan daga lokacin da aka kwashe su zuwa Babila zuwa Almasihu tsara goma sha hudu ne
18 Ingrji Yesu Kristi ahe towa: wa ba nna yima Maryamu ni Yusufu gben ntton wa baka gran kpa, u nne Ruhu tsatsar ye riwu.
Ga yadda haihuwar Yesu Almasihu ta kasance. Mahaifiyarsa, Maryamu, tana tashi da Yusufu, amma kafin su yi aure, sai aka same ta da juna biyu ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
19 U Yusufu illon ma indi u klu Rji, nda na son nno shan na, a cu sron ma rju ni gran nda kama ni wu niyay'bi (aboye)
Mijinta, Yusufu, adalin mutum ne, amma ba ya so ya kunyatar da ita a sarari. Sai ya yi shawara ya sake ta a asirce.
20 Amma, asi tamre towa, u malaika Baci ka ye niwu ni rah nda tre, “Yusufu, ivren Dauda, na klu sisri ban wame Maryamu na, don ikpie a wrji anne ma, a u Ruhu tsatsar.
Yana cikin tunanin wadannan al'amura, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gareshi a mafarki, ya ce masa, “Yusufu, dan Dauda, kada ka ji tsoron daukar Maryamu a matsayin matarka. Gama abinda ke cikinta, ta wurin Ruhu Mai Tsarki aka same shi.
21 Ani ngrji vrenlon wa u yowu ndi Yesu, don ani kpa ndi ma cuwo ni gbugbu latre mba.
Za ta haifi Da, za ka kira sunansa Yesu, domin za ya ceci mutanensa daga zunubansu.”
22 To, ahe to yi don ndu tre Baci he na wa a hla din.
Duk wannan ya faru ne domin a cika abinda aka fada ta bakin annabin, cewa,
23 “To mba, vivren wa ri wa ana to lillona ani ye he nne nda ngrji vrenlon wa ba yo wa ndi Imanuwal” wa hi riri ni “Irji he nita”
“Duba, budurwa za ta sami juna biyu sannan za ta haifi da, za su kira sunansa Immanuel”-ma'ana, “Allah tare da mu.”
24 U Yusufu, gbla sh'me ni nah tie ikpie wa Malaika hla niwu nda hi ka ban wa-a hi ni kpama.
Yusufu ya farka daga barci, ya yi kamar yadda mala'ikan Ubangiji ya umarce shi, sai ya dauke ta a matsayin matarsa.
25 Ana rlihe toh wa-a sai wa a ngrji vren ma u mumla. Ayo nde ma di Yesu.
Amma Yusufu bai sadu da ita ba sai bayan da ta haifi da. Ya kira sunansa Yesu.