< Luke 9 >
1 A'yo wulon don ha ba ye bubu ri na nno ba gbengble ni ikoh u wa ba zu brji, na chu lilo rju ni bi lilo.
Ya kira almajiransa goma sha biyu, ya ba su iko su fitar da kowanne irin aljani, su kuma warkar da cututtuka daga mutane.
2 Na ton ba hi ndu ba hi na hi bla tre Irji, na chu lilo rju ni bi lilo.
Ya aike su, su yi wa'azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
3 Nna hla bawu, nadi ndu ba na ban ikpe rirme nji u bi hi ni zren na; na ban kpalah na, na ban gopelena, na ban bi rina, na nji inklen na, ni na nji inkolom ri u siran na.
Ya ce masu, “Kada ku dauki komi tare da ku domin wannan tafiya. Kada ku dauki sanda, ko jakar matafiyi, ko gurasa, ko kudi - Kada ma ku dauki taguwa biyu.
4 Ko ni ko irime bi ri ni mi bika son zu nikima ni ka lu zu niki hi kpambi.
Dukan gidan da ku ka shiga, ku zauna a gidan har zuwa lokacin da za ku tafi daga wannan yankin.
5 Bubu wa ba na kpa yina, u bika lunde ni gbu ki, ni k'bon wru zah mbi hle ni bawu ndu k'ri gban (Alama) ni bawa ni kah wo'a.
Dukan wadanda ba su marabce ku ba, sa'adda ku ke barin wannan gari, ku karkabe kurar kafufunku a matsayin shaida a kansu.”
6 U ba lunde shan ni nkanka hi ni gbu'gbu na ni bla tre Irji na ni ju lilo ni rju.
Daga nan sai almajiran suka tafi zuwa cikin kauyuka, suka yi ta shelar bishara, su na warkar da mutane a ko'ina.
7 U ba he u Hiridus, Ichu, a wo kpe wa a si zren wawu'a. Wa ti sissri ni wa a wo bari ba si tre andi Yahaya wa ani tie Batisma a la ye ni rema.
Ana nan Hirudus, mai mulki, ya ji labarin dukan abubuwan da su ke faruwa. Ya yi mamaki saboda wadansu mutane suna cewa Yahaya mai yin Baftisma ne ya sake dawowa da ransa.
8 Ba ri ba tre nda ahi Anabi Iliya, ba rju ye ni re u ba ri ba tre nda ahi iri nimi Anabawa bi sen ba a la rju ye ni re.
Wadansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sake bayyana, wadansu kuma suna cewa daya daga cikin annabawa na da can ne ya sake bayyana da rai.
9 Hiridus tre andi ana Yahaya ne, don wawu nna chutu ma ye, u zizan ahi nha mba mi si wo bibi tre yi nitu ma? Rji niki wa soma wa nkon wa ani toh Yesu.
Hirudus ya ce, “Ba zai yiwu Yahaya ne ba, domin na datse masa kai. To, wanene wannan da ni ke jin wadannan abubuwa a kansa?” Daga nan sai ya cigaba da neman hanyar da zai ga Yesu.
10 U bi hla tre Irji ba rji ni zren mba ye na ye hla ni Yesu ikpe wa ba ka ti'a wawu. Niki u wa vuba u ba hi ni mi gbu Betsaida.
Sa'adda manzannin suka dawo daga tafiyarsu, suka gaya wa Yesu dukan abubuwan da suka yi. Daga nan sai ya dauke su domin su tafi tare da shi zuwa garin Baitsaida.
11 Da jubu ndji'a ba wo wu rji wa Yesu hi, na hu zah ma hi niki wa kpa ba na hla tre Bachi ni tre u son nkon Irji ni klekle'a na no bi wa ba si wa sikpa'a si.
Amma sa'adda taron suka ji inda Yesu ya tafi, sai suka bi shi can. Ya marabce su ya yi masu jawabi a kan mulkin Allah, kuma ya warkar da wadanda su ke bukatar warkarwa.
12 U Almajere ba ba toh yalu ni tie nan myen ndi ko ani kpanyeme ni ndu ndji bi wa ba ye ndu ba lu ri mi gbu wa ba he ni hwehwre ni rju yi na fe bubu kru ni kpe wa ba rhi. Don kina he hwehwre ni gbu na.
Da yake yamma ta fara yi, sai almajiransa goma sha biyu suka zo suka ce da shi, “Idan ka yarda ka sallami wannan babban taron mutane dominsu shiga cikin kauyuka, da ke kewaye da gonaki, dominsu sami abinci da wuraren da za su kwana, da yake mu na nan a wurin da ba kowa.”
13 I wa hla, ni bawu ndu ba no ba kpe-wa ba rhi. U ba tre andi ki he ni gble bredi iton migyen ni lambe hari se de ki ka hi le biri ye ni bawa wa bari'a.
Amma sai ya ce da su, “Ku ba su abin da za su ci.” Suka amsa masa, “Dukan abin da muke da shi shine, 'Yan dunkulen gurasa biyar da 'yan kifaye guda biyu, ba za mu iya zuwa mu sawo abincin da zai ishi mutanen nan su duka ba.”
14 (U ba kei indji dubu ton.) Wa ndu Almajere (mri koh ma) ndu ba hla ni bawu ni ndu ba kuson ni wuwlon k'bu-titton ni k'klen wawu.
Mutanen da suke wurin sun kai kimanin mazaje dubu biyar. Sai Yesu ya ce da almajiran, “Ku ce da mutanen su zauna kungiya-kungiya, mutane hamsin a kowacce kungiya.”
15 U ba ti tohki, u indji ba kuson.
Sai almajiran suka yi haka, dukan mutanen suka zauna.
16 U wa ban bredi'a ni lambe hari'a na nzuttu hi ni shulu, na ti lulu yo bawu na genba ti zizah, na ka no mri koh ma (Almajere) ni ndu ba gaba.
Ya dauki dunkulen gurasan guda biyar, da kifin guda biyu, yana dubawa zuwa sama ya albakarce su, sa'annan ya gutsuttsura, ya ba almajiran domin su rarraba wa mutane.
17 U ba ri wrji wa wu mba wu na ni mbru ma, u mri koh ma (Almajere) ba vu mbru ma shuti shu ni sisen Ise-ri.
Dukansu suka ci kowa ya koshi. Daga nan almajiran suka tattara sauran abin da ya rage, har kwanduna goma sha biyu suka cika!
18 Ni viri Yesu si bre Bachi ni kankrji ma, u mri koh ma (Almajere) ba ye niwu, wa myen ba, “A hi nha indji ba yo me?”
Wata rana Yesu yana yin addu'a shi kadai, sai almajiransa suka zo sai ya tambaye su, “Wa mutane suke cewa da ni?”
19 U ba hla niwu, “Bari ba tre, Yahaya wa ani tie batisma, bari kuma ba tre ndi Anebi Iliya, hra bari ba tre ndi ahi ri ni mi Anabawa bi sisen mu wa iri mba aka k'ma ye ni re.”
Suka amsa, “Wadansu suna cewa, Yahaya mai yin Baftisma, wadansu suna cewa kai annabi Iliya ne, har yanzu wadansu suna cewa kai wani cikin annabawa na da can ne ya dawo da rai.”
20 Wa mye ba, “U bi yi na, bi yo me ndi nha?” Bitrus sa niwu ndi, “U Almisihu wa u rji ni Bachi Irji.
Ya tambaye su, “Ku fa? Wa kuke cewa da ni?” Bitrus ya amsa, “Kai Almasihu ne wanda ya zo daga wurin Allah.”
21 Yesu hron ba suse ni ndu ba na jla ni ndrjo naki rina.
Sai Yesu ya gargade su da karfi, kada su gayawa kowa haka tukuna.
22 Na hla ni bawu, A gbigbi ivren ndji ni sha ya nitu kpie gbugbu; bi ninkon ba kamba niwu ni Piristoci, ni bi nhan, nda la wuu, nivi u tra ba ta'wu shme.
Sa'annan ya ce, “Dan Mutum dole ya sha wahalar abubuwa da yawa; dattawa za su ki shi da manyan fristoci da marubuta, sa'annan za a kashe shi. Bayan kwana uku, za a tashe shi da rai.”
23 Na hla ni bawu wawu mba, nli indi wa ani son hu me gbigbi me ndu kama ni tuma, na ban nkunkron u wa ba kagran ni viri san ma (Giciye) na hume ko ni nton rime.
Sai ya ce da su duka, “Dukan wanda ya ke so ya biyo ni, dole ne ya yi musun kansa, ya dauki gicciyen sa kulluyomin, ya biyo ni.
24 Indji wa a tre ndi wawu ni kpa tuma chuwo'a, ana nawo na, ama indji wa a ka tuma no nitu mu'a, ani kpa tuma chuwo kima.
Dukan wanda yake so ya ceci ransa, za ya rasa shi, amma dukan wanda ya ba da ransa domina, za ya cece shi.
25 Lada indji a hi nge, wa ani fe gbungblu'a wawa, da na fe re na?
Wacce riba mutum zai samu idan ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa?
26 Indji wa ni ti shan hla tre mu, Ivren ndji me ni tie shan ma ni nton wa ani k'ma ye ni k'bu Ma ni k'bu Itti ma ni u Maleku njanji.
Dukan wanda yake jin kunya ta da magana ta, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa, sa'adda ya dawo cikin darajarsa da darajar Uba da ta mala'iku masu tsarki.
27 Misi hla ni yiwu iwa yi a gbigbi, nimi mbi wa bi klewa bari mbi bana qu na, se ba toh Irji (Mulki).
Amma ina gaya maku wannan tabbas, wadansu cikinku da ke nan tsaye, ba za su mutu ba sai sun ga mulkin Allah.”
28 Yesu tre klama bi yi, na ban Bitrus mba Yahaya ni Yakubu, na hon hi nitu ngbulu ni hi bre Bachi ni mu.
Kwana takwas bayan Yesu ya fadi wadannan kalmomi, sai ya dauki Bitrus da Yahaya da Yakubu, ya hau kan dutse domin ya yi addu'a a can.
29 Wa ahe ni mi si bre, u shishima ka siran, U inklon ma a kpan tie kink'lan re me na zan ni ri.
Sa'anda ya ke yin addu'a sai yanayin fuskar sa ya canza sosai, tufafinsa kuma suka yi sheki da haske kamar walkiya.
30 Hihari me indji hari, ba si tre ni Yesu, ba Musa mba Iliya.
Nan da nan sai ga mutane biyu suna magana da shi, wato Musa da Iliya.
31 U ba rju kagon mba ni nikon u Bachi. U ba tre ni Yesu ni tu hi kpama wa a te whre u ye tsar ni Wurushelima.
Suka bayyana da daraja kewaye da su, suka yi magana da Yesu a kan tafiyarsa wadda za ta zo ba da dadewa ba a cikin Urushalima.
32 Bitrus ni Almajire wa ba he baba ba kle si kru nna na k'mo, da ba lunde, nan ba toh ikpan ma ni ndji hari ba kri niwu.
Bitrus da almajiran da suke tare da shi barci mai nauyi ya dauke su. Sa'adda suka farka sai su suka ga daukakar Yesu; kuma suka ga mutanen su biyu da ke tsaye tare da shi.
33 Wa ba lu ni bri Yesu na hi kpa-mba, Bitrus tre andi ttie ko mu, abi ni tawu wa ki he niwa, ani bi ndu ta me-tra tie tra; iri ni wu, iri ni Musa u iri ni Iliya. (Ana toh kpe wa a si tre'a na.
Sa'adda Musa da Iliya suke shirin su bar wurin Yesu, sai Bitrus ya ce, “Ya shugaba, ya yi kyau da muke a nan. Zai yi kyau mu yi runfuna uku, daya dominka, daya domin Musa, daya kuma domin Iliya.” Amma hakika bai san abin da ya ke fadi ba.
34 Wa he nimi tre, u kpalu a lu ka ba, u ba tie sissri ni wa ba lu ri ni kpa lu'a.
Sa'adda yake fadin haka sai wani girgije ya zo ya rufe su. Sai suka ji tsoro sa'adda girgijen ya kewaye su.
35 U ba wo lantre rji ni kpalu'a, ni tre ndi, iwa yi mba ahi vren Mu wa me chu'a wo wu.
Sai ga wata murya daga cikin girgijen tana cewa, “Wannan Dana ne wanda na zaba, ku ji shi.”
36 U lantre ban chuwo tre ni kpalu'a, Yesu he ni kankrji ma. U ba son ni ngbangbi ba na hla kperi ni ndrjo ni vi bi kii wa ba toh na.
Sa'adda muryar ta gama magana, Yesu yana nan shi kadai. Suka yi shiru ba su iya cewa kome ba a kan abin da suka gani a kwanakin nan.
37 Ni vi rima wa ba grji rji ni ngbulu ye, u gbugbu indji ba ye niwu.
Washe gari, da suka sauko daga kan dutsen, sai taron mutane da yawa suka zo wurinsa.
38 Hihari me, U ri ni mi indji ba a tre ngban me, Mala bubo me, k'ma ya vren mu, ahi vren mu iriri mi gen.
Nan da nan, wani mutum daga cikin taron mutanen ya yi magana da karfi, “Mallam, kayi wani abu dominka taimaki da na, shi kadai ne gare ni.
39 Meme brji ni hon ni wu tu na yo ku-k'mo, na jijiga niwu na gben glele na yo futen shu yiu. Ni ker ri a ban chuwo ani timba ana fie fie mana idan a ban chuwo.
Mugun ruhu ya kan hau kansa, ya sa shi ya yi ta magowa. Ya kan girjiza shi da karfi ya sa bakinsa ya yi ta kumfa. Da kyar ya ke rabuwa da shi, kuma ya kan ji masa ciwo ba kadan ba bayan da ya bar shi.
40 Mi bre mi ri koh me (Almajere) ni dun ba zu meme brji rju ni wu ni kpa, u bana ya na
Na roki almajiran ka su umurci mugun ruhun ya fita daga cikinsa, amma ba su iya ba!”
41 Yesu tre andi biyi bi tsren g'gran ni ka kpa nyeme ni k'ma bi ni tan mi ua vu suron ni son ni yi? “Nji vren me ye wa yi.”
Yesu, ya amsa, ya ce, “Ku karkatattun tsara marasa bangaskiya, har yaushe zan zauna da ku ina jimrewa da ku? “Kawo yaronka anan.”
42 U vren lu ni hi meme brji wru yo k'bon ni menme u Yesu zu meme brji na chu lilo rju niwu na ka no tie ma
Sa'adda yaron yake zuwa, sai mugun ruhun ya fyada yaron a kasa, ya jijjiga shi sosai. Amma Yesu ya tsauta wa mugun ruhun, ya warkar da yaron. Sa'annan ya mika yaron wurin mahaifinsa.
43 U ba tie sissriwawu mba, wa ba toh gbengble u Irji wa a tie na hla ni Almajere ma,
Dukansu suka yi mamaki da girman ikon Allah. Amma sa'anda suke ta yin mamaki a kan dukan al'ajiban da ya yi, ya ce da almajiransa,
44 “Bi ka ndu tre yi ri ni yiwu ni ton su se: Ivren Indji mba ka no ba ni wo indji.”
“Ku saurara da kyau a kan abin da zan gaya maku, ba da dadewa ba za a bada Dan Mutum ga mutane.”
45 U bana toh itu tre na, a ri ni bawu, ni ndu ba toh tu kpi a si tre na, naki me ba tie sissri nda miyen itu tre me na.
Amma almajiran ba su gane abin da yake nufi da haka ba, an hana su fahimta, domin kada su gane abin da ya ke nufi tukuna, kuma suna jin tsoron su tambaye shi.
46 Ba lu ni gbi suron ni kpa mba, andi a nhan zan ma ninkon'a.
Wani lokaci, almajiran suka fara gardama a tsakaninsu game da wanene za ya zama mafi girma a cikinsu.
47 Yesu toh kpe wa a he ni suron mba, na ban kpran vren ye tsi ni kpa ma ko san.
Amma Yesu ya san abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya kawo dan karamin yaro ya tsaya a kusa da shi,
48 Na hla bawu, ndu ndji wa a kpa vren klenken yi, ni mi inde mu'a a kpame, indji wa a kpame, a kpa indji wa a ton me. Indji wa a vi zizanma ni yi'a a wa wuyi a ninkon ni mi mbi.
sai ya ce da su, “Idan wani ya karbi dan karamin yaro kamar wannan saboda ni, dai dai yake da ya karbe ni. Idan kuma wani ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni kenan. Wanda yake mafi kankanta a cikinku, shi ne mafi mahimmanci.”
49 Yahaya yo a ndi ninkon mbu, ki toh indji ri niwa mu si ju brji ni ndji ni nde me wana nihu ta ni mi mbu na.
Yahaya ya amsa yace, “Ya shugaba, mun ga wani mutum yana ba miyagun ruhohi umarni su fita daga cikin mutane da sunanka. Sai muka ce da shi ya dena yin haka saboda baya tare da mu.”
50 Yesu tre na zuuna, indji wa ana yo ko shi na ahi u me.
Amma Yesu ya ce, “Kada ku hana shi yin haka, domin dukan wanda ba ya gaba da ku, yana tare da ku.”
51 U vi chibi ye whiwhre wa ba ban hon hi ni shu, wa yo suron ma ndi wa wu ni hi Wurushelima.
Sa'adda rana ta kusato da zai hawo zuwa sama, ya kudurta sosai zai tafi Urushalima.
52 Wa ton Manzani duba guchi hi niwu, u ba ka ri ni gbu Samariya wa be m'lan ko nge tie niwu ki.
Ya aiki wadansu manzanni su shirya wuri dominsa kafin ya zo. Suka shiga wani kauye a cikin kauyen Samariya domin su shirya masa wuri a can.
53 U indji ba niki bana kpa ni wo ha na, don ba toh a yo suron u hi ni Wurishelima.
Amma mutanen can ba su karbe shi ba tun da ya ke Urushalima zai tafi.
54 Wa Imri koh ma (Almajire) Yakubu mba Yohana ba toh naki, nda tre, “Bachi, U son ndu ta ton ilu rji ni shulu dun gon ba?”
Sa'adda biyu daga cikin almajiransa, wato Yakubu da Yahaya suka ga haka, suka ce, “Ubangiji, kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama, ta hallaka su?”
55 Wa k'ma ya ba nda zuba.
Amma, ya juya ya tsauta masu.
56 U ba tsi ka hi ni gbu ri kan.
Sai suka tafi wani kauye dabam.
57 Wa ba he ni mi si hi ni gon, u ndrjo a tre niwu, “Mi huwu hi ni wawu wrji wa usi hi.”
Da suna cikin tafiya a kan hanya, sai wani mutum ya ce da shi, “Zan bi ka dukan inda za ka tafi.”
58 Yesu hla ni wu andi, n'nma bi miji ba he ni juju wa ba ri ni mi, u nchinchen ni shu ba he ni koh mba, u Me Vren Ndji mina he ni wrji u ka tu yo na.
Yesu ya amsa masa, “Dila suna da ramuka a kasa inda za su shiga, tsuntsaye kuma suna da sheka, amma Dan Mutum ba shi da inda zai kwanta.”
59 Wa a hla yo ri andi “Hu me.” U ndji'a hla ndi, “Bachi, Mi bre'u dun mi guchi hi rju itti mu ri.”
Yesu, ya ce da wani mutumin kuma, “Ka biyo ni.” Amma mutumin ya ce, “Ubangiji, ka bari in koma gida in bizine mahaifina tukuna.”
60 U wa hla niwu, “Bri k'mo ndu ba rju k'mo ba kimba. Ama niwu hi gbugban mu ni hi hla tre Irji kagon gbungblu.
Amma Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su bizine matattunsu; amma kai ka tafi ka yi wa mutane shelar mulkin Allah a ko'ina.”
61 U indji mu kan tre mi hu, Bachi, a ma ndu mi hi hla ndji mi hi ni bawu ni koh mu.
Wani kuma ya ce, “Ubangiji zan tafi tare da kai, amma bari in je gida inyi ban kwana da mutanena tukuna.”
62 Yesu hla niwu, “Andi Indji wa a kawo vu zan ni soma yarrhan da hla ka ya gon indji mba ku nyre wa ani toh koh Irji.
Yesu ya ce da shi, “Dukan wanda ya fara huda a gonarsa idan ya dubi baya, bai isa ya shiga mulkin Allah ba.”