< Luke 9 >
1 A'yo wulon don ha ba ye bubu ri na nno ba gbengble ni ikoh u wa ba zu brji, na chu lilo rju ni bi lilo.
Bayan da Yesu ya tara Sha Biyun wuri ɗaya, sai ya ba su iko da izini na fitar da dukan aljanu, da na warkar da cututtuka.
2 Na ton ba hi ndu ba hi na hi bla tre Irji, na chu lilo rju ni bi lilo.
Ya kuma aike su, su yi wa’azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
3 Nna hla bawu, nadi ndu ba na ban ikpe rirme nji u bi hi ni zren na; na ban kpalah na, na ban gopelena, na ban bi rina, na nji inklen na, ni na nji inkolom ri u siran na.
Ya ce musu, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, wato, ba sanda, ba jaka, ba burodi, ba kuɗi, ba riga na biyu.
4 Ko ni ko irime bi ri ni mi bika son zu nikima ni ka lu zu niki hi kpambi.
Duk gidan da kuka sauka, ku zauna nan sai kun bar garin.
5 Bubu wa ba na kpa yina, u bika lunde ni gbu ki, ni k'bon wru zah mbi hle ni bawu ndu k'ri gban (Alama) ni bawa ni kah wo'a.
In mutane ba su karɓe ku ba, sa’ad da kun bar garinsu, ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”
6 U ba lunde shan ni nkanka hi ni gbu'gbu na ni bla tre Irji na ni ju lilo ni rju.
Sai suka tashi suka shiga ƙauye zuwa ƙauye suna wa’azin bishara, suna warkar da marasa lafiya a ko’ina.
7 U ba he u Hiridus, Ichu, a wo kpe wa a si zren wawu'a. Wa ti sissri ni wa a wo bari ba si tre andi Yahaya wa ani tie Batisma a la ye ni rema.
Yanzu fa, Hiridus mai sarauta ya ji labarin dukan abubuwan da suke faruwa. Sai ya rikice, don waɗansu mutane suna cewa, Yohanna Mai Baftisma ne ya tashi daga matattu,
8 Ba ri ba tre nda ahi Anabi Iliya, ba rju ye ni re u ba ri ba tre nda ahi iri nimi Anabawa bi sen ba a la rju ye ni re.
waɗansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sāke bayyana. Waɗansu kuma har wa yau, suna cewa, ɗaya daga cikin annabawa na dā ne, ya tashi.
9 Hiridus tre andi ana Yahaya ne, don wawu nna chutu ma ye, u zizan ahi nha mba mi si wo bibi tre yi nitu ma? Rji niki wa soma wa nkon wa ani toh Yesu.
Amma Hiridus ya ce, “Yohanna dai na yanke kansa, amma wanne mutum ne nake jin labarin abubuwan nan a kansa?” Sai ya yi ƙoƙari ya ga Yesu.
10 U bi hla tre Irji ba rji ni zren mba ye na ye hla ni Yesu ikpe wa ba ka ti'a wawu. Niki u wa vuba u ba hi ni mi gbu Betsaida.
Da manzannin suka dawo, sai suka faɗa wa Yesu abin da suka yi. Sai ya ɗauke su, suka keɓe kansu su kaɗai, zuwa wani gari da ake kira Betsaida.
11 Da jubu ndji'a ba wo wu rji wa Yesu hi, na hu zah ma hi niki wa kpa ba na hla tre Bachi ni tre u son nkon Irji ni klekle'a na no bi wa ba si wa sikpa'a si.
Amma taron mutane suka ji labari, sai suka bi shi. Ya marabce su, kuma ya yi musu magana a kan mulkin Allah, ya kuma warkar da masu bukatar warkarwa.
12 U Almajere ba ba toh yalu ni tie nan myen ndi ko ani kpanyeme ni ndu ndji bi wa ba ye ndu ba lu ri mi gbu wa ba he ni hwehwre ni rju yi na fe bubu kru ni kpe wa ba rhi. Don kina he hwehwre ni gbu na.
Da rana ta kusa fāɗuwa, sai Sha Biyun suka zo wurinsa, suka ce, “Ka sallami taron domin su shiga ƙauyuka na kewaye, su nemi abin da za su ci, da wurin kwana, don inda muke, ba kowa.”
13 I wa hla, ni bawu ndu ba no ba kpe-wa ba rhi. U ba tre andi ki he ni gble bredi iton migyen ni lambe hari se de ki ka hi le biri ye ni bawa wa bari'a.
Yesu ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Sai suka ce masa, “Muna da burodi biyar da kifi biyu kaɗai. Sai dai, in mun je mu sayi abinci domin dukan wannan taron.”
14 (U ba kei indji dubu ton.) Wa ndu Almajere (mri koh ma) ndu ba hla ni bawu ni ndu ba kuson ni wuwlon k'bu-titton ni k'klen wawu.
Maza kaɗai sun kai kusan dubu biyar. Amma ya ce wa almajiransa, “Ku sa su su zauna a ƙungiya hamsin-hamsin.”
15 U ba ti tohki, u indji ba kuson.
Haka almajiran suka yi, kowa kuwa ya zauna.
16 U wa ban bredi'a ni lambe hari'a na nzuttu hi ni shulu, na ti lulu yo bawu na genba ti zizah, na ka no mri koh ma (Almajere) ni ndu ba gaba.
Sai Yesu ya ɗauki burodin biyar da kifin biyun, ya ɗaga kansa sama, ya yi godiya, ya kuma kakkarya su. Ya ba wa almajiransa, domin su rarraba wa mutanen.
17 U ba ri wrji wa wu mba wu na ni mbru ma, u mri koh ma (Almajere) ba vu mbru ma shuti shu ni sisen Ise-ri.
Duka kuwa suka ci suka ƙoshi. Almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
18 Ni viri Yesu si bre Bachi ni kankrji ma, u mri koh ma (Almajere) ba ye niwu, wa myen ba, “A hi nha indji ba yo me?”
Wata rana sa’ad da Yesu yana addu’a a ɓoye, almajiransa kuma suna tare da shi, sai ya tambaye, su ya ce, “Wa, taron mutane ke ce da ni?”
19 U ba hla niwu, “Bari ba tre, Yahaya wa ani tie batisma, bari kuma ba tre ndi Anebi Iliya, hra bari ba tre ndi ahi ri ni mi Anabawa bi sisen mu wa iri mba aka k'ma ye ni re.”
Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu kuma annabi Iliya, har wa yau waɗansu suna cewa, kai ɗaya daga cikin annabawan da ne, da ya tashi da rai.”
20 Wa mye ba, “U bi yi na, bi yo me ndi nha?” Bitrus sa niwu ndi, “U Almisihu wa u rji ni Bachi Irji.
“Amma ku fa, wa, kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kiristi na Allah.”
21 Yesu hron ba suse ni ndu ba na jla ni ndrjo naki rina.
Yesu ya gargaɗe su da ƙarfi, kada su gaya wa kowa wannan magana.
22 Na hla ni bawu, A gbigbi ivren ndji ni sha ya nitu kpie gbugbu; bi ninkon ba kamba niwu ni Piristoci, ni bi nhan, nda la wuu, nivi u tra ba ta'wu shme.
Ya sāke cewa, “Dole ne Ɗan mutum ya sha wahaloli da yawa, dattawa, da manyan firistoci, da malaman dokoki kuma su ƙi shi, kuma dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tā da shi da rai.”
23 Na hla ni bawu wawu mba, nli indi wa ani son hu me gbigbi me ndu kama ni tuma, na ban nkunkron u wa ba kagran ni viri san ma (Giciye) na hume ko ni nton rime.
Sai ya ce wa dukansu, “In wani zai bi ni, dole yă mūsanta kansa, ya ɗauki gicciyensa kowace rana, ya bi ni.
24 Indji wa a tre ndi wawu ni kpa tuma chuwo'a, ana nawo na, ama indji wa a ka tuma no nitu mu'a, ani kpa tuma chuwo kima.
Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
25 Lada indji a hi nge, wa ani fe gbungblu'a wawa, da na fe re na?
Ina amfani, in mutum ya ribato duniya duka, amma ya rasa ransa, ko kuma ya yi hasarar ransa.
26 Indji wa ni ti shan hla tre mu, Ivren ndji me ni tie shan ma ni nton wa ani k'ma ye ni k'bu Ma ni k'bu Itti ma ni u Maleku njanji.
Duk wanda yake jin kunyana da na kalmomina, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa sa’ad da zai zo a cikin ɗaukakarsa, da ɗaukakar Uban, da kuma ta tsarkaka mala’ikun.
27 Misi hla ni yiwu iwa yi a gbigbi, nimi mbi wa bi klewa bari mbi bana qu na, se ba toh Irji (Mulki).
“Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su ga mutuwa ba, sai sun ga mulkin Allah.”
28 Yesu tre klama bi yi, na ban Bitrus mba Yahaya ni Yakubu, na hon hi nitu ngbulu ni hi bre Bachi ni mu.
Bayan kamar kwana takwas da yin wannan magana, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yohanna, da kuma Yaƙub, suka hau kan dutse tare don yin addu’a.
29 Wa ahe ni mi si bre, u shishima ka siran, U inklon ma a kpan tie kink'lan re me na zan ni ri.
Yana cikin addu’a, sai kamannin fuskarsa ta sāke, tufafinsa kuma suka zama da haske kamar hasken walƙiya.
30 Hihari me indji hari, ba si tre ni Yesu, ba Musa mba Iliya.
Sai ga mutum biyu, Musa da Iliya, suka bayyana cikin kyakkyawar daraja, suna magana da Yesu.
31 U ba rju kagon mba ni nikon u Bachi. U ba tre ni Yesu ni tu hi kpama wa a te whre u ye tsar ni Wurushelima.
Suka yi zance a kan tashinsa, wanda shi ya kusan ya kawo ga cikarsa a Urushalima.
32 Bitrus ni Almajire wa ba he baba ba kle si kru nna na k'mo, da ba lunde, nan ba toh ikpan ma ni ndji hari ba kri niwu.
Barci kuwa ya kama Bitrus da abokan tafiyarsa sosai. Da idanunsu suka warware, sai suka ga ɗaukakarsa da kuma mutum biyun tsaye tare da shi.
33 Wa ba lu ni bri Yesu na hi kpa-mba, Bitrus tre andi ttie ko mu, abi ni tawu wa ki he niwa, ani bi ndu ta me-tra tie tra; iri ni wu, iri ni Musa u iri ni Iliya. (Ana toh kpe wa a si tre'a na.
Da mutanen na barin Yesu, sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, wato, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.” (Bai ma san abin da yake faɗi ba.)
34 Wa he nimi tre, u kpalu a lu ka ba, u ba tie sissri ni wa ba lu ri ni kpa lu'a.
Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije ya bayyana ya rufe su, sai suka ji tsoro, yayinda suke shiga cikin girgijen.
35 U ba wo lantre rji ni kpalu'a, ni tre ndi, iwa yi mba ahi vren Mu wa me chu'a wo wu.
Wata murya ta fito daga cikin girgijen, tana cewa, “Wannan Ɗana ne, zaɓaɓɓena, ku saurare shi.”
36 U lantre ban chuwo tre ni kpalu'a, Yesu he ni kankrji ma. U ba son ni ngbangbi ba na hla kperi ni ndrjo ni vi bi kii wa ba toh na.
Da muryar ta gama magana, sai suka tarar Yesu shi kaɗai ne. Almajiran kuwa suka riƙe wannan al’amari a zukatansu. A lokacin nan, ba su gaya wa kowa abin da suka gani ba.
37 Ni vi rima wa ba grji rji ni ngbulu ye, u gbugbu indji ba ye niwu.
Kashegari, sa’ad da Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga kan dutsen, sai taro mai yawa ya haɗu da shi.
38 Hihari me, U ri ni mi indji ba a tre ngban me, Mala bubo me, k'ma ya vren mu, ahi vren mu iriri mi gen.
Sai wani mutum daga cikin taron ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Malam, ina roƙonka, ka dubi ɗan nan nawa, gama shi ne kaɗai nake da shi.
39 Meme brji ni hon ni wu tu na yo ku-k'mo, na jijiga niwu na gben glele na yo futen shu yiu. Ni ker ri a ban chuwo ani timba ana fie fie mana idan a ban chuwo.
Wani ruhu yakan kama shi, sai ya yi ihu farar ɗaya. Yakan sa shi farfaɗiya, har bakinsa ya yi kumfa. Da ƙyar yake barinsa, yana kuwa kan hallakar da shi.
40 Mi bre mi ri koh me (Almajere) ni dun ba zu meme brji rju ni wu ni kpa, u bana ya na
Na roƙi almajiranka su fitar da shi, amma ba su iya ba.”
41 Yesu tre andi biyi bi tsren g'gran ni ka kpa nyeme ni k'ma bi ni tan mi ua vu suron ni son ni yi? “Nji vren me ye wa yi.”
Yesu ya amsa ya ce, “Ya karkataccen zamani marar bangaskiya, har yaushe ne zan kasance tare da ku, ina kuma haƙuri da ku? Kawo yaronka nan.”
42 U vren lu ni hi meme brji wru yo k'bon ni menme u Yesu zu meme brji na chu lilo rju niwu na ka no tie ma
Yaron yana kan zuwa ke nan, sai aljanin ya buga shi ƙasa, cikin farfaɗiya. Amma Yesu ya kwaɓe mugun ruhun, ya warkar da yaron, sai ya miƙa shi ga mahaifinsa.
43 U ba tie sissriwawu mba, wa ba toh gbengble u Irji wa a tie na hla ni Almajere ma,
Duk suka yi mamakin girman Allah. Yayinda kowa yana cikin mamakin dukan abubuwan da Yesu ya yi, sai ya ce wa almajiransa,
44 “Bi ka ndu tre yi ri ni yiwu ni ton su se: Ivren Indji mba ka no ba ni wo indji.”
“Ku kasa kunne da kyau ga abin da zan faɗa muku. Za a bashe Ɗan Mutum ga hannun mutane.”
45 U bana toh itu tre na, a ri ni bawu, ni ndu ba toh tu kpi a si tre na, naki me ba tie sissri nda miyen itu tre me na.
Amma ba su fahimci abin da yake nufi da wannan magana ba. Ba su gane ba, don an ɓoye musu shi. Su kuwa sun ji tsoro su tambaye shi.
46 Ba lu ni gbi suron ni kpa mba, andi a nhan zan ma ninkon'a.
Wata gardama ta tashi a tsakanin almajiran, a kan ko wane ne a cikinsu zai zama mafi girma
47 Yesu toh kpe wa a he ni suron mba, na ban kpran vren ye tsi ni kpa ma ko san.
Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa ya tsaya kusa da shi.
48 Na hla bawu, ndu ndji wa a kpa vren klenken yi, ni mi inde mu'a a kpame, indji wa a kpame, a kpa indji wa a ton me. Indji wa a vi zizanma ni yi'a a wa wuyi a ninkon ni mi mbi.
Sai ya ce musu, “Duk wanda ya karɓi wannan ƙaramin yaron a cikin sunana, ni ya karɓa, kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne. Gama mafi ƙanƙanta duka a cikinku, shi ne kuma mafi girma.”
49 Yahaya yo a ndi ninkon mbu, ki toh indji ri niwa mu si ju brji ni ndji ni nde me wana nihu ta ni mi mbu na.
Sai Yohanna ya ce, “Ubangiji, mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, muka yi ƙoƙarin hana shi, don shi ba ɗaya ba ne daga cikinmu.”
50 Yesu tre na zuuna, indji wa ana yo ko shi na ahi u me.
Yesu ya ce, “Kada ku hana shi, gama duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”
51 U vi chibi ye whiwhre wa ba ban hon hi ni shu, wa yo suron ma ndi wa wu ni hi Wurushelima.
Da lokaci ya yi kusa da za a ɗauki Yesu zuwa sama, sai ya ɗaura niyyar tafiya Urushalima.
52 Wa ton Manzani duba guchi hi niwu, u ba ka ri ni gbu Samariya wa be m'lan ko nge tie niwu ki.
Sai ya aiki’yan saƙo, su yi gaba. Su kuwa, suka shiga cikin wani ƙauyen Samariyawa, don su shirya masa abubuwa.
53 U indji ba niki bana kpa ni wo ha na, don ba toh a yo suron u hi ni Wurishelima.
Amma mutanen ƙauyen ba su karɓe shi ba, don yana kan hanyar zuwa Urushalima ne.
54 Wa Imri koh ma (Almajire) Yakubu mba Yohana ba toh naki, nda tre, “Bachi, U son ndu ta ton ilu rji ni shulu dun gon ba?”
Da almajiransa, Yaƙub da Yohanna suka ga haka, sai suka yi tambaya suka ce, “Ubangiji, kana so mu kira wuta ta sauka daga sama ta hallaka su?”
55 Wa k'ma ya ba nda zuba.
Amma Yesu ya juya, ya kwaɓe su.
56 U ba tsi ka hi ni gbu ri kan.
Sai shi da almajiransa suka tafi wani ƙauye.
57 Wa ba he ni mi si hi ni gon, u ndrjo a tre niwu, “Mi huwu hi ni wawu wrji wa usi hi.”
Suna kan tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka, duk inda za ka.”
58 Yesu hla ni wu andi, n'nma bi miji ba he ni juju wa ba ri ni mi, u nchinchen ni shu ba he ni koh mba, u Me Vren Ndji mina he ni wrji u ka tu yo na.
Yesu ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
59 Wa a hla yo ri andi “Hu me.” U ndji'a hla ndi, “Bachi, Mi bre'u dun mi guchi hi rju itti mu ri.”
Ya kuma ce wa wani mutum, “Ka bi ni.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Ubangiji, bari in je in binne mahaifina tukuna.”
60 U wa hla niwu, “Bri k'mo ndu ba rju k'mo ba kimba. Ama niwu hi gbugban mu ni hi hla tre Irji kagon gbungblu.
Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su binne matattunsu, amma kai, ka je ka yi shelar mulkin Allah.”
61 U indji mu kan tre mi hu, Bachi, a ma ndu mi hi hla ndji mi hi ni bawu ni koh mu.
Har wa yau, wani ya ce, “Zan bi ka, Ubangiji, amma ka bar ni in je in yi bankwana da iyalina tukuna.”
62 Yesu hla niwu, “Andi Indji wa a kawo vu zan ni soma yarrhan da hla ka ya gon indji mba ku nyre wa ani toh koh Irji.
Yesu ya amsa ya ce, “Babu wani da yakan sa hannunsa a garman shanu, sa’an nan ya waiwaya baya, da ya isa ya shiga hidima a cikin mulkin Allah ba.”