< Luke 3 >

1 Ni mi ise u tso don tra wa Tiberia Caesar - Chu, u, Pontiyus Bilatus ana gomna Judiya, Hiridus ka Chu ni Galili, vayima Filibus ka chu ni Ituriyada Tarakunitas, mba Lasaniyas ana Chu ni Abaliya.
A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
2 Ni nton wa Hanana ba kayafa bana bi ninkoh bitun tre Irji kaye ni Yahaya vren Zakariya ni miji.
A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
3 Sei ka zren kagon gbugbulu mi yie'u nei u urdu, dani hla tre Irji ni bawu, a yo'u ba duba ye kpa Irji nda dun ba sukpa ni ba wu, duba wru lah tre mba hle ni bawu.
Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
4 Na wa ba na nha nvunvu u tre Anabi Ishaya ndi llan di ri si yo ni miji, mlan koh Bachi tie dun koh ma hi yreyre.
Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
5 Ko san ngbulu ba shu, u ngbulu ba ba gble tita ba kma ti fime, u nkoh bi tie memme ba kma bi ba ba shu, ni ngbulu baba tita ba ba yra ba nda kma me nkoh ni bubu biwa be gblegble me'a.
Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
6 U bi he nimi kpa ba to Ceto u Irji.
Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
7 Sai Yohana a hla ni gbugbu ndji wa ba si ye dun sukpa bawu'a. Yohana yo ba ndi “biyi mri iwan, anha hla ni yiwu dun yi tsutsu ni nfu wa ani ye ni yiwu'a?”
Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Nitu kii, kma tie klo kunkro wa ndi ba bre dun ba wru lla tre hle bawu dana ta tre ni kpamba ndi ki he ni Ibrahim wa a iti mbu, mi hla niwu Irji hei ni gbengble wa ani zu titi biyi kma tie mri ni Ibrahim rji ni tita bi yi.
Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
9 Ko zizan ba mlan gla tie nitu nja bi ba kunkro. U wawu kunkro bi wandi bana klo bi na ba gen ba nda vu ba sru ni lu.”
An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
10 U gbugbu ndji baki mye'u ndi, “Zizan ki tie ni he?”
Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
11 A kasa nda tre “Indji wandi a he ni nklon ha, ka ban rhi ni ndji wandi ana he ni rhi na, u ndji wa ahe ni lah ka tie naki ngame.
Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
12 Bi kpa ban ba ye du ba sukpa ni bawu, nda tre, “Ndji-u-tsro, ki tie ni he?”
Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
13 A hla ni bawu ndi, “Nata kpa inklen zan kpe wandi ba tre dun yi kpa na.”
Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
14 Sojoji bari ngame ba mye, ndi, “U kita na? Ki tie ni he?” A bla hla ni bawu, “Na kpa nkleh niwo njo ni gbengble na, ndi na tie ce ti ndrjo na. Nji kpe-andi bi u mbi dun mla yi.”
Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
15 Zizan wa ba ndji ba si ya nkoh ye u Kristi'a, wawu mba ba si rhimre ni suron mba nitu Yohana, ko wawu mba hi Kristi'a.
Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
16 Yohana a kasa ni bawu nda tre ndi, “Ime mi si sukpa ni yiwu ni mma, u ndji waa si ye ni koshi mu, a zan me ni gbengble, u mina tsra wa mi sie rjirji lagban u zama na. Wawu ni sukpa ni yiwu ni Ruhu Tsratsra ni lu.
Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
17 Ahei ni mumu ni wo ma wandi ani tie ndu niwu nda zen memme bie nda ka waa bi zi nimi iwron. U ani gon biwa ba tie meme'a ni lu wa ana y'bi na.”
Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
18 Ni mi tsro mba Yohana a hla tre ndindi ni ndji ba.
Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
19 Hiridus wa ana Chu, a son gran wa vayi ma Hiridiya, ni mbru meme kpie wa Hiridus azi tie'a,
Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
20 a ka biyi suru nhaa, ndi a ka Yohana tro ni brusuna.
Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
21 Inton wa ba sukpa ba ndji wawu, Yesu me ba sukpa'a niwu ngame, wa asi he ni mi bre wa ka toh shulu bu'u,
Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
22 wa toh Ruhu Tsatsar ka grji ye son nitu ma na ngyu, wa ka wo lan Irji ni shu, “Iwu yi wu vren mu wandi isuron mu a kpa wu. Suron mu ku si ni wu.”
Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
23 Yesu ahe ni sei wlon nkpu tra nda vu tie ndu Irji. Nimi kpa, Yesu hi vren Isuwu wa ba yo tima ndi Heli,
To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
24 ivren Matat, ivren u Levi, ivren u Melki, ivren u janai, ivrn u Isuwu.
ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
25 Isuwu ana vren Mattatiyas, ivren Amos, Ivren Nahum, ivren Esli, ivren Naggai,
ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
26 ivren u Maat, ivren u Mattatiyas, ivren u Semein, ivren u Josech, ivren u Joda.
ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
27 Joda ana vren u Jowanan, ivren u Resa, ivren u Zerubabel, ivren u Salatiyel, ivren u Neri,
ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
28 ivren u Melki, ivren u Addi, ivren u Cosam, ivren u Elmadam, ivren u Er,
ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
29 ivren u Joshuwa, ivren u Eliyeza, ivren u Jorim, ivren u Mattat, ivren u Levi.
ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
30 Levi ana vren Simiyon, ivren Judah, ivren Isuwu, ivren Jonam, ivren Eliakim,
ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
31 ivren Meliya, ivren Menna, ivren Mattata, ivren Natan, ivren Dawuda,
ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
32 ivren Jessi, ivren Obed, ivren Bowaz, ivren Salmon, ivren Nahshon.
ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
33 Nahshon ana vren Amminadab, ivren Admin, ivren Arni, ivren Hezron, ivren Perez, ivren Judah,
ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
34 ivren Yakubu, ivren Isuwa, ivren Ibrahim, ivren Terah, ivren Nahor,
ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
35 ivren Serug, ivren Riyu, ivren Peleg, ivren Eba, ivren Shelah.
ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
36 Shelah ana vren Cayinan, ivren Arfakza, ivren Shem, ivren Noah, ivren Lamech,
ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
37 ivren Metuselah, ivren Enok, ivren Jared ivren Mahalaleel, ivren Cainan,
ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
38 ivren Enos, ivren Seit, ivren Damu, Ivren Irji.
ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.

< Luke 3 >