< Luke 23 >

1 Indji ba wawu mba, ba lunji Yesu ye ni koshi Bilatus.
Sai duk taron suka tashi, suka kawo Yesu gaban Bilatus.
2 Na lu ni nhanwu andi, ba ka toh asi kpa indji si ti meme na ni tonba ni timeme, ndu ba na kpanyime na nhan iban hi no Kaisar na, na ni yo tuma Almasihu, Ichu.”
Suka fara saransa, cewa “Mun same wannan mutum yana ruda kasarmu, ya haramta a ba Kaisar haraji, yana kuma cewa shi da kansa ne Almasihu, sarki.”
3 Bilatus Myen, Ahi wuyi Ichu Yahudawa? U Yesu kpanyime niwu, “Anaki wu tre.”
Bilatus ya tambaye shi, cewa “Shin kaine Sarkin Yahudawa?” Sai Yesu ya amsa masa ya ce, “Haka ka ce.”
4 U Bilatus hla ni Firistocin bi ninkon ba ni jubu indji ba, “Mi na vu ni lah tre riri me na.”
Sai Bilatus ya ce wa manyan firistocin da taro mai yawa, “Ban samu ko laifi daya game da wannan mutumin ba.”
5 U ba luni tre, andi, “A kpa suron indji ni tie meme na ni hla tre ma ni Yahudiya, a so ma rji ni Galili ye ni wayi.”
Amma suka yi ta cewa, “Yana ta da hankalin mutane da koyarwa a dukan Yahudiya, ya fara daga Galili har zuwa ga wannan wuri.”
6 Niwa Bilatus a woki ma, na miyen indji bi Galili'a wawu
Sa'adda Bilatus ya ji wannan, sai ya tambaya ko mutumin daga Galiline.
7 Wa ye toh ni mre ma andi a he ni zah (kalkashi) pkancin Hiridus, natru Yesu hi ni Hiridus, wa a he nitu ma Wurushelima ni vi bi ton ki.
Sa'adda ya gane cewa yana karkashin mulkin Hirudus, sai ya tura Yesu wurin Hirudus, wanda shi da kansa yana Urushalima a wadannan kwanakin.
8 Ni wa Hiridus a ku shishi ni wu u ngyiri shu niwu ni suron su se'a ni tu wa azi wau tu lalon mu ni sun toh wu. Wa a wo tre tuma, waa dede ni yoshishi ni sun toh iri kpii wa a ni tie bi so sissri wa a ni tie'a.
Sa'adda Hirudus ya ga Yesu, sai ya cika da farin ciki sosai, saboda ya so ganinsa tunda dadewa. Tun can ya ji game da shi sai ya yi begen ganin wadansu al'ajibai da zai yi.
9 Hiridus a miyen Yesu ni mi tre bi gbugbu, u Yesu na sa kpe riri ni wu na.
Hirudus ya tambaye Yesu cikin kalmomi masu yawa, amma Yesu bai amsa masa da komai ba.
10 Firistocin bi ninkon ba ni biwa ba nhan, lunde kri, ni nha nu
Sai manyan firistoci da marubuta suka tsaya, suna ta yi masa zargi mai zafi.
11 Hiridus ni sojoji ma ba lu ni nhanu, nani whiyen ni wu, u ba sru nkulon bi ndindi ma niwu, na kma tru Yesu hi ni Bilatus.
Hirudus da sojojinsa suka zarge shi, suka kuma yi masa ba'a, suka sa masa tufafi masu kyau, sa'annan ya sake aika Yesu zuwa wurin Bilatus.
12 Ba Hiridus mba Bilatus ba tie kpan ni kpamba chachuki (ba na ta yo kpamba ni ko shishi).
Sai Hirudus da Bilatus suka zama abokai a wannan rana (da ma su abokai gaba ne).
13 Bilatus yo Firistocin ni bi chu ni jubu ndji ba,
Bilatus ya kira manyan firistoci tare da masu mulki da kuma taron jama'ar,
14 na hla ni bawu, wa hla ni bawu, bi ka nji igu yi ye na indji wa ani ton ndji timeme, bi yi me bi toh, mi, miye ni shishi, mina vu lahtre riri me na wa bi ki nhanwu na.
sai ya ce masu, “Kun kawo mani wannan mutum kamar wanda yake jagorar mutane ga munanan ayyuka, ku kuma gani, Ni, na tuhume shi a gabanku, ban sami ko kuskure daya daga mutumin nan game da abinda ku ke zarginsa da shi ba.
15 Ba kpe, Hiridus me, ala ka tru kma ye ni tawu, bi toh, igu yi na tie ikpe wa ba wu'a na
Babu, ko Hirudus ma, ya sake komar mana da shi, kun gani, babu wani abu wanda ya yi da ya cancanci mutuwa,
16 Ni tu ki mi gbi ton niwu ni kachuwo.
saboda haka zan yi masa horo sa'annan in sake shi.”
17 Wa hi gbigbi ni Bilatus ndu chu indji u y'bi iri no ba ni Idin)
[Ya zama dole Bilatus ya sakar wa Yahudawa wani daurarre guda daya lokacin idin.]
18 Wawu mba wu ba lu tre vovome, ndu ba, “Nji gu mba hi, na nji Barabas grji!”
Amma dukansu suka yi ihu tare, cewa, “A tafi da wannan mutumin, sai a sako mana Barabbas!”
19 Barabas a guri wa ba yo ni mitra u lo ndji bi latra, nitu wa aka kpa suron tie meme ni bawu ni gbu na wu ndji.
Barabbas mutum ne wanda aka sa a cikin kurkuku saboda wani tada hankali a cikin birni da kuma kisankai.
20 Bilatus ala tre, asun ka Yesu chuwo.
Bilatus ya sake yi masu magana, yana so ya saki Yesu.
21 Ba la tre vovome, ni, “Giciye wu, giciye wu.”
Amma suka yi ihu, cewa, “A giciye shi, a giciye shi.”
22 A hla ni bawu nkpu u tra, “Nitu ngye, a ngye yi indji yi tie wa a meme? Mi na toh kpe wa a tie wa bi wah bi wu'u ni tu ma na. Ni naki to bi kle nu'u yah, me ka'u chuwo.”
Sai ya sake ce masu sau na uku, “Don me, wace magunta wannan mutum ya yi? Ban sami wani abu da ya isa sanadin mutuwa game da shi ba. Saboda haka bayan na hore shi, zan sake shi.”
23 Ba kri titu, na tre gbangban me, ndi ba sun ndu ba giciye wu, u tre mba ka mren Bilatus saran.
Amma suka nace da murya mai karfi, suna so a giciye shi, sai muryarsu ta rinjayi Bilatus.
24 U Bilatus a kpanyime ni bawu ni kpi wa ba sun.
Sai Bilatus ya yarda ya yi masu bisa ga abin da suke so.
25 Wa ba miyen a nji grji ni bawu na no ba i wa ba yo ni tra u lo ndji'a nitu wa a kpa suron tie meme nda wu ndji, na no Yesu ni kpi wa son.
Ya sako masu wanda suka tambaya ya ba su wanda aka sa a kurkuku domin tada hankali da kuma kisankai. Amma ya ba da Yesu bisa nufinsu.
26 Ba nji hi, na zu vu guri inde ma Siman Bakurane, a rji ni gbu siye, u ba ban giciyen gran ni wu gba, ndu nji hu Yesu.
Da suka tafi da shi, sai suka kama wani mai suna siman Bakurane, yana zuwa daga karkara, sai suka daura masa giciyen ya dauka, yana biye da Yesu.
27 Chubu nji ni mba ba lo suron na ni yi nitu ma, na ni hu.
Babban taron jama'a, da na mata da suke makoki da kuka dominsa, suna binsa.
28 Wa kma yaba, Yesu tre, “Bi mri mba Urushalima, na yi nitu mu na, bi ka yi ni tu-mbi ni mri-mbi.
Amma da ya juya wurinsu, Yesu yace, “Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka domina, amma ku yi kuka domin kanku da 'ya'yanku.
29 Bi toh, ivi ni ye wa ba tre, lulu a biwa ba son ni krju ni bi wa bana ngrji na, ni sisan wa bana mma na.”
Gama ku gani, kwanaki suna zuwa da za su ce, 'Albarka ta tabbata ga bakararru da wadanda basu taba haihuwa ba da kuma wadanda ba a taba shan mamansu ba.'
30 U ba fare tre ndu tita, “Ku chan ta, ni Igbulume, Bika kata.
Sa'annan za su fara ce wa duwatsu, 'Ku fado bisanmu,' da tuddai ma, 'Ku rufe mu.'
31 Ba ni na tie kpi biyi u kunkron a ri he ni shushu, ahi ngeri ani tie u kunkro klu ye?
Gama idan sun yi wadannan abubuwan lokacin da itace yana danye, me zai faru sa'adda ya bushe?”
32 U ba nji indji hari biwa ba lah-tre, hi niwu baba Yesu.
Aka kai wadansu mutum biyu masu laifi, domin a kashe shi tare da su.
33 Wa ba ka ri ni bubu wa ba yo, “kyukyu” niki ba ka kpan ba ni kunkron'a (giciye) ni bi y'bi hari, u ri ni wo kori, u ri ni ko ta.
Sa'adda suka zo wurin da a ke kira kwalluwa, nan suka giciye shi da barayin, daya daga hannun damansa dayan kuma daga hannun hagu.
34 Yesu tre “Itie, kpa wruhle ni bawu, don bana toh kpe wa ba tie na.” Ba lu ni ta chacha, na yaba inklon ga.
Yesu yace, “Uba, ka yafe masu, gama basu san abin da suke yi ba.” Sai suka jefa kuri'a, suka rarraba tufafinsa.
35 Indji ba lu niya bi nji ndji (mulki) ba wa ba ye si tsawu andi, “A kpa bari chuwo. Dun kpa tuma chuwo ki, toh wawu yi hi Almasihu u Irji, wa ba chu'a.”
Mutane sun tsaya suna kallo sa'annan masu mulki suna ta yin masa ba'a, cewa, “Ya ceci wadansu. Bari ya ceci kansa, idan shine Almasihu na Allah, zababben nan.”
36 Bi lokpa me ba tsawu, na wa niye, nda ni dren iman wa'a sa.
Sojojin ma suka yi masa dariya, suna zuwa wurinsa, suna mika masa ruwan tsami,
37 Nani tre, “U ta hi chu Yahudawa, U ka kpa tume chuwo.”
suna cewa, “Idan kai Sarkin Yahudawa ne, ceci kanka.”
38 U gban ri he niwu tu, “I wa yii a chu Yahudawa.”
Akwai wata alama bisansa, “Wannan shine Sarkin Yahudawa.”
39 Iri ni mi bi y'bi hari ba wa ba kpan ba, a mre'u andi, “A na wuyi Almasihu na? ka tu me chuwo ni kita me.
Daya daga cikin barayi wanda aka giciye, ya zage shi, cewa, “Ba kai ne Almasihu ba? Ka ceci kanka da mu.”
40 U ri ma sah, wa ya losuron, “U na tie sissri Irji na, nitu wa ba wuta baba?
Amma dayan ya amsa, ya tsauta masa cewa, “Ba ka tsoron Allah, da yake shari'arka daya ne da nasa?
41 U mbu ba tie tsra, ki kpa mbu nitu kpe wa ki tie, Igu yi ana tie kperi memema na.”
Mu kam an yi ma na daidai, gama mun samu bisa ga abin da muka yi. Amma wannan mutum bai yi wani abu mara kyau ba.”
42 Nna la tre, “Yesu na kparisu ni me na, uta ri ni ko Itie me.”
Sai ya kara, “Yesu, ka tuna da ni sa'adda ka shiga mulkinka.”
43 Yesu hla ni wu, “Njanji tre misi hla niwu, luwa u he nime ni Firdausi.”
Yesu ya ce masa, “Gaskiya ina ce maka, yau za ka kasance tare da ni a firdausi.”
44 U ba he niki ni krafi tanne, u bubu ka tie bwu kagon gbu'a wawu, hi ni krafi tiya.
Anan nan a wajen sa'a na shida, sai duhu ya mamaye kasar duka har zuwa sa'a na tara
45 U rji grji ka ku. U bre gontra tra u tre ni Irji a yar tie hari ni tsutsuma ye ni meme.
sa'adda rana ya fadi. Sai labulen haikalin ya rabu a tsakiya zuwa kasa.
46 Ni yar yi ni lan gbangban me, Yesu tre, “Itie, mi ka Ruhu Mu no niwo me.” wa tre naki, na que.
Da kuka da murya mai karfi, Yesu yace, “Uba, na mika Ruhu na a hannunka.” Bayan da ya fadi wannan, sai ya mutu.
47 U Jirimia a toh kpi wa a tie, na gbire Irji san, “Gbigbi iguyi a hi indji ndindi.”
Sa'adda jarumin ya ga abin da ya faru, ya daukaka Allah, cewa, “Lallai wannan mutumin mai adalci ne.”
48 U Ijubu indji ba wawu, wa ba hu ba ye ndu ba ye toh ikpi wa a tie ni shishi mba, ba kma ni wru wo ni san mba.
Sa'adda dukan taro mai yawa wadanda suka zo tare domin su shaida da idanunsu suka ga abubuwan da suka faru, suka koma suna bugan kirjinsu.
49 Bi wa ba toh wawu mba'wu, ni imba bi wa ba hu ba rji ni Galili, u ba ka kri ni gbugbanmu, na si ya kpe wa a si zren
Amma duk idon sani, da kuma matan da suka bi shi tun daga Galili, suka tsaya daga nesa, suna duban wadannan abubuwa.
50 U indji ri ba yowu Yusufu, ahi vren u majalisan ni ugbu na indji ndindi.
Ga shi kuwa, wani mutum mai suna Yusufu, shi dan majalisa ne, nagari ne kuma mutum mai adalci ne
51 Wa na kpa nyime ni kpi wa ba tre ni kpi wa ba tie na, rji ni Arimatiya ni meme Yahudiya, i wa a si kben hi koh Irji.
(bai yarda da shawarar da kuma abin da suka aikata ba), daga Arimatiya a kasar Yahudiya, wanda yake jiran mulkin Allah.
52 Igu ki, ahi ni Bilatus, na miyen wu a ndu ban ikpon Yesu no wawu.
Wannan mutum, ya sami Bilatus, ya tambaya a bashi jikin Yesu.
53 Wa nji grji ye meme, na nyewu ni pri ndindi, na kayo ni mi bbe wa ba shime ni kpa tita, ni bubu wa ba na rju ndrjo toh na.
Ya saukar da shi kasa, sai ya nade shi cikin likafani na linin mai kyau, ya kwantar da shi cikin kabari da aka sassaka shi daga dutse, inda ba a taba binne wani ba.
54 Ivi ri ri ni vi, u Asabaci te whiwhre.
Ranar kuwa, ranar shiri ce, Asabaci kuma ta kusato.
55 Ba imba biwa ba ye baba Yesu rji ni Galili, ba hu nda toh wrji wa ibbe'a a he nda toh ka ba yo nkpon ma'a.
Matan da suka taho da shi tun daga Galili, suka biyo baya, su ga kabarin da inda aka ajiye shi.
56 U ba kma hi, u ba wa inye u gban ni turare. U ba kusi ni ivi Asabaci, nidu.
Suka koma, sai suka shirya kayan kamshi da mai. Suka kuma huta a ranar Asabaci bisa ga doka.

< Luke 23 >