< Luke 22 >

1 Ba he inton u bredi wa ana sa na, a ti whewhre, wa ba you ndi ngan u za.
Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,
2 Bi ninkon bi tu du Irji, baba bi han be, ba susun da tre nitu bawu Yesu, ni ki basi klu sissri ba ndji.
manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.
3 Ibrji a ri ni Yahuza Iskariyoti, iri ni mi mri koh ma tso.
Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.
4 Yahuda a hi ninkon bi toh ndu Irji, biwa ba yah ndji kpatsri, wawu ni vu Yesu no ba.
Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.
5 U ba ngyiri ni wu, nda no nklen
Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.
6 Wa kpa nyime, da wa nkon wa ani vu noba ni nton wa indji bana he na.
Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
7 Ivi u gah u za, naki ba ti gan u hay ikru wu ton yin.
Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
8 Yesu a ton Bitrus mba Yohana, da tre, Hi ndi mla bubu biri u ton yin, du ta ri.
Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
9 Ba mye, ni nsten wu son ki hi mla bubu ati?
Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
10 A ka sah ni bawu, inde bi ri nimi gbu'a, bi tsra nio ndji a nji iriman. Hu hi ri nimi koh wa ani ri.
Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
11 Hla ni ndji u koh, ndi mala, tre mikoh bi tsri he ni ntsen, wa mi ribi ri ni mri koh mu?
Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
12 Ani tsro yi kikle ko u koshu, wa ba mla ti ye bika mla ti ni mun.
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
13 U ba hi da toh ikpe a he naki. Baka mla bubu u tan bredi wa ana sa na.
Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
14 Da inton ati wa ka sun ni mri koh ma.
Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
15 Wa a hla ni bawu, mi you suron ndi mi tan bredi wa ana sa na ni yi, ri ni yah.
Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
16 Naki mi hla yiwu, mi na la tan bredi ni yi na, se ba mla wu ti ni koh Irji.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
17 Yesu ban gbaju'a da ngyiri nda tre kpa wayi, gaa ni kpambi.
Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
18 Naki mi si hla yiwu mi na la so mma klo kunkro na, se koh Irji ye.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
19 A ban bredi'a nda ngyiri, nda mere no ba nda tre wayi yi nma kpa mu, wa ba no don biyi, bita ti nayi ndi ta ri mre mu.
Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
20 A ban gbaju'a ni kogon bredi, iwa yi a si sa tre'a, a yi mu wa ba kahle don biyi.
Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
21 Bi ka mla yah indji wa ani vu noba, a he nime ni tu tebru.
Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
22 Naki Ivren Ndji hi gbigbi na ba tre, Iyah ndi kima wa ani vu noba.
Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
23 Baka lunde nda ni mye kpa mba, ahi nha ni mi mbu wa ani tie kpe mba.
Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
24 Ba lu si sen nyu ni kpa mba, nitu ninkon u shu.
Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
25 A hla ni bawu, bi tu chu baba ndji biwa bana toh Irji na, ba tsro gbengblen mba, bari ba he ni gbengblen nitu mba, ba you ba ndi bi mulki ni daraja.
Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
26 Du na he naki ni yi na, naki du ndji wa a ninkonni yi du he na vivren tsitsa, indji wa a zan yi ka he na u tindu.
Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
27 A hi nha a hi ninkon, wa a sun ni tebru, ko a wa a si tie ndu'a? Ana wa a sun nitu tebru na? Naki me na ndji u tie ndu ni mi mbi.
Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
28 Naki biyi bi he ni mie ni mi tsra
Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
29 Mi no yi mulki na wa Tie mu a ne.
Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
30 Bi ri ndi so ni tebru u mulki, bi sun ni koh mu, ndi ta blatre ni lbe tso u Israila.
Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
31 Siman, Siman, mla zren me tie, ibrji a wa inton wa ani yre u na alkama.
“Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe kakamar alkama.
32 Naki ba si bre ni wu, du you suron me du na joku na, inde wu kma ye wu ka tre trre ndindi ma wa ani no mri vayi me gbengblen.
Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa’yan’uwanka.”
33 Bitrus a hla wu Bachi mi he ni mereu hu hi ni brusuna mba kyu.
Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”
34 Yesu ka sa ni wu ni hla wu Bitrus, kafi du gba tbu luwa nkpu tra u kpatron ndi wu na toh me na.
Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 Yesu ka hla ni bawu, inton wa mi ton yi hama ni bu ko go ple, ko lagban zah, ibi ka wa kpie hama? U baka trre ndi a'a.
Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?” Suka amsa, “Babu.”
36 Ama zizan'a, i wa a he ni mbu ka ban ni igople. Ndji wa ana he ni inji ngban na, ka ban klon ma le nd le ri.
Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.
37 Naki mi hla yiwu, ikpie wa ba nha nitu mu ani he naki, ba bla you na bi la tre, ikpei wa ba tre ni tumu a he naki.
A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”
38 U ba tre, “Bachi, iyah, ngye inji ngban hari, wa a tre da tsra nu
Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.” Yesu ya ce, “Ya isa.”
39 Da ba ri la u yalu kle, Yesu a hi na ani tie chachuu hi ni ngbulu Zaitun, se mri koh ma ba hu.
Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
40 Da baka kai niki, waka hla bawu, ta bre Irji don du yi ri ni mi lah tre na.
Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
41 A kaba don da ch'bi, nda kukyu ngbarju nda bre,
Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
42 Nda tre, Bachi, inde wu kpa nyime wu ka ban gbarju i rju ni mu.
“Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
43 Se Maleka ni shu ye niwu nda no gbengblen suron.
Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
44 Ahe nimi iyah kpukpo me, a you ni bre, hra ikrji ma ni grji na gble yi.
Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
45 A lunde ni bre ma, da ye ni mri koh, da ye toh ba basi kruna don ani lo ba suron.
Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
46 Wa a mye ba a ngye sa bi si kruna? Lunde ndi bre du yina ri ni yah na.
Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
47 A he ni mi tre, se ga gbugbu ndji ba ye baba Yahuda iri ni mi mri koh ma tso'a, nda ye whewhrre ni Yesu nda hlan vu.
Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.
48 Ni ki Yesu ka tre, Yahuda, wu ban Vren Ndji no ni hlan vu?
Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”
49 U biwa ba krju Yesu you ni tsutsu, ba toh ikpie wa si zren, nda tre, Bachi ki tsen ni inji ngba?
Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”
50 Iri ni mi mri koh ma a chu nji nda yba iton ninkon bi nha be u woh ko ri.
Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.
51 U Yesu ka tre, a tsra naki da taba iton nda wakar ni wu.”
Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.
52 Yesu tre ni tie ndu ni koh Irji, ni bi gben ni koh Irji baba chiche ndji ba, wa ba you ni koh shishi bi rju na bi ye vu ndji u ybi, ni ba nji ngban ni kpala?
Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?
53 Ni wa mi na he ni yi ni tra Irji, bina vu me na, zizan a nton mbi ni gbengblen u bu.
Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”
54 Ba vu nda nji nda hi, ba nji hi ni koh ba, u Bitrus ka ta hu ni gbugban mu.
Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.
55 Niki baka muh lu ni tsutsu ra, nda ku sun niki wawu mbawu, Bitrus a sun ni tsutsu mba.
Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.
56 Sei wa ri a toh a sun ni kpan lu'a, nda you shishi ni wu, nda tre ndji yi ba he mbawu.”
Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 U Bitrus a kpa tron, nda tre iwa mi na toh na.”
Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
58 Vi toh fi me yi, u ndji ri ka toh nda tre, wu mewu he ni mi mba. Bitrus tre ndi, “Ana me na.”
Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
59 Intonri hi, i ndji ri a kama nda la tre, njanji ndji yi ahe ni wu, a vren Galili.
Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
60 Bitrus a tre, ndi mi na toh kpie wa asi tre na, nda asi he ni mi tre u gbah lu tbi.
Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
61 A kma u Bachi ka yah Bitrus. Se Bitrus ka ri mre ikpie wa Bachi tre'a, se a hla niwu, kafi du gbah du tbi luwa, u kpa tron nkpu tra ndi wu wu na toh me na.
Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
62 Da Bitrus rju nda yi u'lo suron.
Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
63 Se ndji bi wa ba troh baba Yesu ba ka zah wu da tsi me.
Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
64 Da baka kawu shishi, nda mye hla tawu a nha wru'u?
Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
65 Ba ka tre trre u nanye, ni meme tre ni Yesu.
Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
66 Da imble kpan u chiche ndji baka ka bi baba bi toh ndu Irji, baba bi nha lbe se da nji'u hi ni bi tuchu, baba bi ninkon bari.
Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
67 Da tre hla ni tawu a wuyi wu Almasihu'a” wa a hla ni bawu ko mi hla yiwu, bina kpanyime na,
Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
68 Inde mi ye yi, bi na kasa ni muh na.
in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
69 Aman ni ko shishi, Ivren Indji ni sun ni woh ko ri u gbengblen Irji.
Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
70 Ba ka tre, u u” Vren Irji? Se Yesu ka kasa ni bawu ikpie wa bi tre a me yi.
Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
71 Ba tre don ngye ki si wa shaida? Kita ni tu mbu ki woh ni nyu ma.”
Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”

< Luke 22 >