< Luke 18 >

1 A lu tre ni tre ni bawu nitu duba ta bre Irji chachu nda na tie suu na.
Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
2 A hla ndi “Ni gbu ri, ndji wu han tre njanji ri a he wandi ana tie sissri Irji na, dana toh ndji ngame ni nfutu na.
yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
3 Niki, iwari wu s'ro ri ason ni gbu'a ngame. A ta hi ni ndji wu han tre njanji chachu nda bre ndi, “Zome kpa ikrji mu niwo bi yo me ni shishi.
Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
4 A ban nton gbaa me ndana son zo na. A son ni vi ntor ri nda rhimre kikima, nda hla ni tuma ndi, “Mina ti sissri Irji na, nina ya ndji ni nfutu ngame na.
An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
5 Nitu du iwayi na nne iya ni ye bre ma chachu na, Mi zo u kpa njanji ikrji ma nduna lo me kpa ni yema na.
duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
6 I Bachi a tre ndi “wo tre andi ndji wa ana han tre njanji na a hla.
Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
7 Zizan Irji ngame na nji njanji ye ni bi wa a chu ba, ndani yi yo'u chachu ni Irji mba ni chu na? Ani tie sesren ye gbagbla ni ba?
A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
8 Mi hla yiwu ndi, ani ye ni njanji ni bawu gbagbla. Nikima vren ndji nita ye, ani ye toh nime ni gbungblu meme?
Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
9 Me a lu tre toh choloncho ni bari wandi ba yo suron ni gbengblen mba, ndi ba zren tsatsra ndani ya bari grji tu,
Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
10 Ndji ha ba hon hi ni tra Irji nda hi bre, iri ana Farasi, i rhima bi kpa iban.
“Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
11 Farasi a lu kri ni zande nda bre ni tuma ndi, 'Irji, mi ngyiri nitu mina he to ndji bari na - bi y'bi, bi lahtre, bi humba, ba bi kpa ban too ndi yi.
Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
12 Mi zu kpa mu rhi biri nkpu ha ni sati. Mi nu zakka (iri nimi wlon) nitu wawu kpi ndi a ri nime.'
Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
13 Ndji wu kpa ban'a a kri gbagban nda na nzu shishi hi ni shu mena, wru wo ni san nda tre ndi, “Irji, ya me ni lo suron, ndji wu lahtre.”
Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
14 Mi hla yiwu, igu hi a kma hi kpama ni si suron zan ndi rima'a, nitu ndji wandi a nzu tuma hi shu, ba gbron grji, i wandi a ban tuma grji (nitu ana kpe na) ba nzu hi shu.”
Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
15 Ndji ba basi'a nji mri tsitsa ni du sa wo ni tu mba, i mri koh bi nduma ba to ba nda puaha tre.
Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
16 I Yesu a yo ba ye ni kpama nda tre ndi, “Du mri bi tsitsa ba ye nime, na zu ba na. Ikoh Irji ni shulu a wu biwa ba he to mba.
Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
17 Tre njanji, ndji wa na kpa ikoh Irji to mri bi tsitsa na, ana ri mi na.
Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
18 I chu mba ri a mye ndi, “Ticha ndindi, mi tie ngye ri ni kpa ko Irji?” (aiōnios g166)
Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
19 Yesu a hal wu ndi, “Nitu ngye wu yome ndji ndindi? Ndrjo na ndindi na se Irji kankle ma.
Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
20 Bi toh doka Irji na tie nka na, na wu ndji na, na y'bi na, na nu sheda che na, wo tre time mba yime.”
Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
21 Ichu a tre ndi “Mi zi hu kpi bi mba wawuu rhi ni nzemu.”
Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
22 Yesu a woo nda tre ndi ikpe riri rhi don, hi le ni kpi wandi wu he niwu ni gah ni bi ya, i wu he ni lada ni shulu, ni ye huma.”
Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
23 Ni wa ichu a wo tre, a loh suron kpukpome, nitu ana ndji wu wo.
Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
24 Ni wa Yesu a toh kma ti gbon me ni lo suron (gbugbu chiche tre vunvu ni Greek ba sa tu tre ndi a kma ta lo suron/ama gbugbu bari bana he ni lan kima na), a tre ndi, “Ani he ni du du ndi wu wo du rhi ni koh Irji.
Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
25 A he ni du ni ndi wu wo du ri ni koh Irji, zan du ra kumi ri zu ni shishi n'ro.”
Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26 Bi wa basi'a wa'a ba tre ndji. “I nha ni nawo?”
Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
27 Yesu a sa ndi “Ikpi wa ba he ni iya tie ni ndji bana he ni iya ni Irji na.”
Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
28 Bitrus ngame a tre ndi, “Toh, ki bri wawu kpi mbu ndi hu.”
Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
29 Yesu a kma tre ni ba ndi “Njanji, mi hla yiwu, ba ndji wa a don ikoh ma, ko wama, ko mri vayi ma, ko ba ti ma, ko ni mri ma nitu ikoh Irji,
Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
30 wandi ana kpa zan zizan na, ni vi ye, i vri rji wu sisenise.” (aiōn g165, aiōnios g166)
sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
31 A yo ndji wlon-don-ha ba ye ni kpama nda hla bawu ndi, “Toh, ki si yi ni Wurushelima, i wawu kpi wa anabawa ba tere nitu Vren Ndji'a ba tie toki.
Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
32 Ba banwu nu biwa bana mri Israila na, ba nzau, nda nu shan nda ju nte sru niwu.
Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
33 Ba ti tsiwu, ba wuu, i ni vi wu tra ani lunde.”
Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
34 Ba na mla to ikpi biyi na, i lan tre ana ri nibawu, niki bana mla toh ikpi wa a tre na.
Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
35 Niwa Yesu a ye wiewire ni Yeriko ndji wu infyen ri a son si bre ni nyu nkon,
Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
36 ni wo kpaa ndji basi zren ni zu whiwhre niwu, a mye ka ngye si zren.
da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
37 Ba hla wu ndi Yesu wu Nazarat-akasi hi.
Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
38 Ndji wu infyen a yra gro nda hla ndi, “Yesu Vren Dawuda, ya me ni lo suron.”
Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
39 Bi wa bisi'a zren ni ko shishi ba puatre ni ndji wu infyen nda hla niwu du son gbangbi. A kama nda si kpa gro ndi, “Vren Dawuda, ya me ni lo suron.”
Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
40 Yesu a kri kpenme nda nu tre du ba ji igu'a ye niwu. Niwa ndji wu infyen a ye whiwhre, Yesu a mye ndi,
Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
41 “Wu son du mi ti ngye ni wu?” A tre ndi, “Bachi, mi son toh ni shishi mu.”
“Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
42 Yesu a hla niwu ndi, “Kpa toh ni shishi me, kpanyime me a nu si kpa.
Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
43 Hari, a toh ni shishima nda hu si yo ise ni nzu nde Irji.
Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.

< Luke 18 >