< Luke 18 >

1 A lu tre ni tre ni bawu nitu duba ta bre Irji chachu nda na tie suu na.
Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
2 A hla ndi “Ni gbu ri, ndji wu han tre njanji ri a he wandi ana tie sissri Irji na, dana toh ndji ngame ni nfutu na.
Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
3 Niki, iwari wu s'ro ri ason ni gbu'a ngame. A ta hi ni ndji wu han tre njanji chachu nda bre ndi, “Zome kpa ikrji mu niwo bi yo me ni shishi.
A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
4 A ban nton gbaa me ndana son zo na. A son ni vi ntor ri nda rhimre kikima, nda hla ni tuma ndi, “Mina ti sissri Irji na, nina ya ndji ni nfutu ngame na.
“An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
5 Nitu du iwayi na nne iya ni ye bre ma chachu na, Mi zo u kpa njanji ikrji ma nduna lo me kpa ni yema na.
amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
6 I Bachi a tre ndi “wo tre andi ndji wa ana han tre njanji na a hla.
Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
7 Zizan Irji ngame na nji njanji ye ni bi wa a chu ba, ndani yi yo'u chachu ni Irji mba ni chu na? Ani tie sesren ye gbagbla ni ba?
Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
8 Mi hla yiwu ndi, ani ye ni njanji ni bawu gbagbla. Nikima vren ndji nita ye, ani ye toh nime ni gbungblu meme?
Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
9 Me a lu tre toh choloncho ni bari wandi ba yo suron ni gbengblen mba, ndi ba zren tsatsra ndani ya bari grji tu,
Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
10 Ndji ha ba hon hi ni tra Irji nda hi bre, iri ana Farasi, i rhima bi kpa iban.
“Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
11 Farasi a lu kri ni zande nda bre ni tuma ndi, 'Irji, mi ngyiri nitu mina he to ndji bari na - bi y'bi, bi lahtre, bi humba, ba bi kpa ban too ndi yi.
Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
12 Mi zu kpa mu rhi biri nkpu ha ni sati. Mi nu zakka (iri nimi wlon) nitu wawu kpi ndi a ri nime.'
Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
13 Ndji wu kpa ban'a a kri gbagban nda na nzu shishi hi ni shu mena, wru wo ni san nda tre ndi, “Irji, ya me ni lo suron, ndji wu lahtre.”
“Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
14 Mi hla yiwu, igu hi a kma hi kpama ni si suron zan ndi rima'a, nitu ndji wandi a nzu tuma hi shu, ba gbron grji, i wandi a ban tuma grji (nitu ana kpe na) ba nzu hi shu.”
“Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
15 Ndji ba basi'a nji mri tsitsa ni du sa wo ni tu mba, i mri koh bi nduma ba to ba nda puaha tre.
Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
16 I Yesu a yo ba ye ni kpama nda tre ndi, “Du mri bi tsitsa ba ye nime, na zu ba na. Ikoh Irji ni shulu a wu biwa ba he to mba.
Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
17 Tre njanji, ndji wa na kpa ikoh Irji to mri bi tsitsa na, ana ri mi na.
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
18 I chu mba ri a mye ndi, “Ticha ndindi, mi tie ngye ri ni kpa ko Irji?” (aiōnios g166)
Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
19 Yesu a hal wu ndi, “Nitu ngye wu yome ndji ndindi? Ndrjo na ndindi na se Irji kankle ma.
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
20 Bi toh doka Irji na tie nka na, na wu ndji na, na y'bi na, na nu sheda che na, wo tre time mba yime.”
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
21 Ichu a tre ndi “Mi zi hu kpi bi mba wawuu rhi ni nzemu.”
Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
22 Yesu a woo nda tre ndi ikpe riri rhi don, hi le ni kpi wandi wu he niwu ni gah ni bi ya, i wu he ni lada ni shulu, ni ye huma.”
Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
23 Ni wa ichu a wo tre, a loh suron kpukpome, nitu ana ndji wu wo.
Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
24 Ni wa Yesu a toh kma ti gbon me ni lo suron (gbugbu chiche tre vunvu ni Greek ba sa tu tre ndi a kma ta lo suron/ama gbugbu bari bana he ni lan kima na), a tre ndi, “Ani he ni du du ndi wu wo du rhi ni koh Irji.
Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
25 A he ni du ni ndi wu wo du ri ni koh Irji, zan du ra kumi ri zu ni shishi n'ro.”
Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26 Bi wa basi'a wa'a ba tre ndji. “I nha ni nawo?”
Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
27 Yesu a sa ndi “Ikpi wa ba he ni iya tie ni ndji bana he ni iya ni Irji na.”
Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
28 Bitrus ngame a tre ndi, “Toh, ki bri wawu kpi mbu ndi hu.”
Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
29 Yesu a kma tre ni ba ndi “Njanji, mi hla yiwu, ba ndji wa a don ikoh ma, ko wama, ko mri vayi ma, ko ba ti ma, ko ni mri ma nitu ikoh Irji,
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
30 wandi ana kpa zan zizan na, ni vi ye, i vri rji wu sisenise.” (aiōn g165, aiōnios g166)
da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
31 A yo ndji wlon-don-ha ba ye ni kpama nda hla bawu ndi, “Toh, ki si yi ni Wurushelima, i wawu kpi wa anabawa ba tere nitu Vren Ndji'a ba tie toki.
Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
32 Ba banwu nu biwa bana mri Israila na, ba nzau, nda nu shan nda ju nte sru niwu.
Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
33 Ba ti tsiwu, ba wuu, i ni vi wu tra ani lunde.”
za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
34 Ba na mla to ikpi biyi na, i lan tre ana ri nibawu, niki bana mla toh ikpi wa a tre na.
Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
35 Niwa Yesu a ye wiewire ni Yeriko ndji wu infyen ri a son si bre ni nyu nkon,
Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
36 ni wo kpaa ndji basi zren ni zu whiwhre niwu, a mye ka ngye si zren.
Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
37 Ba hla wu ndi Yesu wu Nazarat-akasi hi.
Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
38 Ndji wu infyen a yra gro nda hla ndi, “Yesu Vren Dawuda, ya me ni lo suron.”
Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
39 Bi wa bisi'a zren ni ko shishi ba puatre ni ndji wu infyen nda hla niwu du son gbangbi. A kama nda si kpa gro ndi, “Vren Dawuda, ya me ni lo suron.”
Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
40 Yesu a kri kpenme nda nu tre du ba ji igu'a ye niwu. Niwa ndji wu infyen a ye whiwhre, Yesu a mye ndi,
Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
41 “Wu son du mi ti ngye ni wu?” A tre ndi, “Bachi, mi son toh ni shishi mu.”
“Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
42 Yesu a hla niwu ndi, “Kpa toh ni shishi me, kpanyime me a nu si kpa.
Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
43 Hari, a toh ni shishima nda hu si yo ise ni nzu nde Irji.
Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.

< Luke 18 >