< Luke 16 >

1 Yesu hlani mri koh ma, (Almajirama) “A ndi igu ri he niwo (arziki) na he ni indji wa ani ya bi ndu ni wu'a, U ba ye hla ni wu indji iwo, andi igu ya bi ndu ma a ri woma ni hi kle.
Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya.
2 Indji iwo'a a yo na miyen ahi nge mba mi wo? Ne lisafi ikpe wa u tie ni ya ndu'a u na la tie ndu, u ya indji ngana.
Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'
3 Igu u ya indji ba (wakili) a ta mre, “Ahi nge mi ti, tun nde itie koh mu a vu me kpa ndu u ya? Mina he ni gbengble wami ya ron na, Ishan ni ti me mi na ya bre na.
Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko.
4 Mi toh kpe u wa mi tie'a inde ba zu me ni ndu u ya indji (wakili), indji ba ka kpa me hi ni koh mba.
Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.
5 Ayo bi wa itie koh ma ni huba ihlah, a miyen u mumlan, 'Ahi bren itie koh mu ni hu?'
Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?'
6 Andi uma a Garuwa Iyen Deri. Wa hla ni wu, kpa nvunvu u nha me, gbagbla nha hamsi nihi kuson kpa me ni ka don.
Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.'
7 Wa hla miyen ri, ibren ba hu? Wa tre, buhu alkama dari wa hla niwu, kpa nvunvu yi, ni nha tan mani
Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'
8 U tie koh ma kber igu lah tre san nitu wa a tie whiri, imlen imri bi, zizanyi ni indji mba, ba whiri zan imri bi kpan. (aiōn g165)
Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. (aiōn g165)
9 Mijhla ni yiwu tie kpan nitu he niwo wa ana bie na. Wa ye nna wo kle, u ba ka kpa yi hi ni koh wa bi son hi ni tuntur. (aiōnios g166)
Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama. (aiōnios g166)
10 Indji wa ni tie njanji ni kpi tsitsa ma, A ni ti njanji ni rhi grama, u indji wa ana tie njanji ni kpi vi tsitsa mana, ana tie njanji ni kpi rigra ma na.
Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu.
11 Inde u na tie bi ni wo wa ana u njanji na, u nhan ni kpa nyewme ni wu ni wo u njanji?
Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya?
12 Toh wu na ni tie njanji ni nji kpi u bari na, anha ni no wu inkleh u me?
Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?
13 Ba indji wa ani ya biu tie ko hari, ni mi nton riri, se ka kpa ri na kari don, koh ka kpari tsri na kpari nyime. U na ya hu Irji mba inklen na.
Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba.”
14 Farisawa bi wa ba son inklen kpukpome'a ba wo tre naki wawu na nzah.
Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a.
15 Wa hla bawu, 'Biyi bi ban tu mbi ni shishi ndi ni kperi, ama Irji toh mi suron mbi. Ikpi wa ndi ba kpanyime niwu wawu, ahi kpi u shan ni Irji.
Sai ya ce masu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.
16 Attaura ni Litafi Anabawa ba he si ye ni ye Yohana rji ni nton ki ye zizan yi, ba tsikpa bubu bla tre Irji, indji wa wu ba ri ti tu ni gbengblen ni yo tu mba niwu.
Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta.
17 A hi fie me ni shulu mba ni meme ndu ba su e tu ni wa, iten riri u Attaura ndi joku migen.
Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.
18 Indji wa a ga gran ma ni Iwa-ma na kpa iwa ri a zina a si tie, ni nidji wa a kpa iwa wailon ma zu a hi zina a si ti.
Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.
19 Indji iwo ri a shur kpimabi tie le nani zren zren ma ko ni nton ri meh.
Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana.
20 U indji u bre ri ba yo ni Lazaru ba nji ye ka yo ni nkotra koh ma, ni kpukpa inkpa-n ni kpa,
Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne,
21 Wa ni son rhi birhi wa a kuble ni tu tebru, u yawu ba ye nle kpa-n.
Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.
22 Wa ye tsra ni nton wa indji u bre a ye kyu, u Maleku ba ye ban hi ni nhma ko wa Ibrahim he. U ndji u wo'a (arziki) a kyu u ba ban ka rju.
Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi,
23 wa ka ri ni koh lu, wa zun shishi hi ni shu, na toh Ibrahim gbugban mu ba sun mba Lazarus ni ngbala ko wa Ibrahim he. (Hadēs g86)
yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa. (Hadēs g86)
24 Wa yra yi yo, Itie mu Ibrahim, toh me ni lo suron ni ton Lazarus, ndu ka vren wo ma son ni mma, na chu kpi yo ni mu ni lbe ndu jubu gbugbran mu.
Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'
25 Ibrahim tre vuvren, Rimre ni sun me ni gbungblu, u rhi ro wo me ni kpa kpi bi bie ma, u Lazarus si tiya, u zizan mba ba ndu si toh roma ni wa, Iwu mba u si tiya.
Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 U naki me ba shi juju ni tsitsu bi vron me, ni ndu bi wa ba sun zagran ye niyi ba ka na yana, kuma biwa ba he ni yi ko mba ba ka na zagran ye nita na.
Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'
27 U indji i wo tre, mi bre wu, Itie mu Ibrahim, u ka ton hi ni koh itie mu, u ngrji'a -
Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina -
28 Mi he ni mri vayi mri-lon iton, ndu hi hron ba ni ndu ba na ye ni bubu yi na.
domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'
29 Ibrahim hla niwu, ba he ni Musa ni anabawa, ndu ba wo ba.
Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.'
30 U indji i wo, a sa niwu andi, A'a Itie mu Ibrahim, indrjo ri ni ta rji ni mi bi kyu ka hla ni bawa, ba k'ma suron mba no Irji.
Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.'
31 U Ibrahim hla niwu, inde bana wo Musa ni anabawa bana, ko indji wa a kyu lunde na ka hla ni ba wu bana wo wu na.
Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'”

< Luke 16 >