< Yohana 15 >

1 “Ime yi Mi nchi kunkro u njanji, u Ti mu ahi Indji u rju'a.
“Nine itacen inabi na hakika, Ubana kuwa shi ne manomin.
2 Ani gyen ko ilan rime rju ni kpa Mu wa ana klo'a na, iwaani klo'a ani mla'u tie ni ndu la klo babran me.
Yakan cire duk wani rashe a cikina da ba ya bada 'ya'ya, mai bada 'ya'ya kuwa ya kan gyara shi domin ya kara bada 'ya'ya.
3 Bi kpa tsatsra me ye, nitu wa Mi hla tre Mu ni yiwu ye.
Kun rigaya kun tsarkaka saboda maganar da na yi muku.
4 Bi ka son nimi Mu, ima Mi ka son ni mi mbi ngame, na wa ilan kunkro na ya klo kima na se ahe ni nchi konkro'a, na ni me bi na ya na se bi son ni mi Mu.
Ku zauna ciki na, Ni kuma cikin ku. Kamar yadda reshe ba ya iya bada 'ya'ya shi kadai sai ya zauna cikin itacen, haka kuma ba za ku iya ba, sai kun zauna ciki na.
5 Mi nchi kunkron u bi lan ma, indji wa a son ni Me'a Mi he niwu, ani klo gbugbuwu, inda u ta na he ni Me na, bina ya tie kperi na.
Ni ne itacen inabi, ku ne rassan. Wanda ya zauna ciki na, ni kuma cikin sa, yana bada 'ya'ya dayawa, gama in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
6 Indji wa ana son ni Me na, ba kawu taga na ilan kunkro wa ka klu baka kpulu ba sru na yo lu, baka gon tie nton.
Wanda kuma bai zauna a ciki na ba, akan jefar da shi kamar reshe, ya bushe, kuma sukan tattara rassan su jefa a wuta, su kone.
7 U ta son ni Me, u lantre Mu son niwu, minye me ko ngyeri wa u son'a u Mi tie ni yiwu.
In kun zauna a ciki na, maganata kuma ta zauna a cikin ku, sai ku roki duk abinda kuke so, za a kuwa yi maku.
8 Ni naki, inde Timu ni fe gbre san; ni ndu yi klo babran, ni bi almajere Mu.
Ta haka ake daukaka Ubana: cewa ku bada 'ya'ya dayawa, kuma cewa ku almajiraina ne.
9 Na wa Iti Mu ni son Me, anaki Ime me mi son yi. Bika son ni mi son Mu.
Kamar yadda Ubana ya kaunace ni, haka Ni ma na kaunace ku; Ku zauna cikin kaunata.
10 U ta hu du mu, u sun ni mi son Mu nawa Mi hu du Iti Mu ni sun ni mi son ma.
Idan kun kiyaye dokokina, za ku zauna cikin kaunata kamar yadda Na kiyaye dokokin Ubana, na kuma zauna cikin kaunarsa.
11 Mi tre kpe biyi ni yiwu ni ndu si sron Mu nda he ni yi, na ndu si sron a shu.
Ina gaya maku wadannan al'amura domin farincikina ya kasance a cikin ku, kuma domin farincikinku ya zama cikakke.
12 Iwa yi a hi ndu Mu, ni ndu yi son kpa mbi na wa Mi son yi'a.
“Wannan shine umarnina, cewa ku kaunaci juna kamar yadda na kaunace ku.
13 Indrjori na he ni son ri zan wayi na - wa iri ni re (ivri) ma no ni tu kpukpan ma.
Babu wanda ke da kaunar da tafi haka, wato ya bada ransa domin abokansa.
14 Bi kpukpan Mu inde bi tie kpe wa Mi hla ni yiwu dun yi tiewu.
Ku abokaina ne idan kuna yin abubuwan da na umarce ku.
15 Mi na la yo yi tie igran ngana; igran na to kpe wa Iti koh ma ni tie'a na. Mi yo yi kpukpan Mu, ni kpe wa Mi wo ni Timu wawu, wu Mi dun yi to.
Nan gaba ba zan kara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abinda Ubangijinsa ke yi ba. Na kira ku abokaina, domin na sanar da ku duk abinda na ji daga wurin Ubana.
16 Ana biyi bi chu Me na, a Me mi chu yi ni ton yi ni dun yi hi ni klo ni ndu klo mbi ndu ba toh naki iwa yi ni he naki, ni tu ko ngyeri bi minye Ti Mu ni mi nde Mu, ani no yi.
Ba ku kuka zabe ni ba, amma Ni ne na zabe ku, na aike ku don ku je ku bada 'ya'ya, 'ya'yanku kuma su tabbata. Wannan ya zama domin duk abinda kuka roki Uba a cikin sunana, zai baku.
17 Mi yo yi ni ndu yi kpa nyeme ni kpa mbi.
Na baku wannan umarni: domin ku kaunaci juna.
18 I gbungblu'a nita kama ni yi, bi ka to ndi a kama ni Me ri na kama ni yi.
In duniya ta ki ku, ku sani cewa ta kini kafin ta ki ku.
19 Bini na u gbungblu'a, gbungblu'a ba ni son yi nawu mba. Ni wa bina u gbungblu; a na, Mi la juyi ni mi gbungblu'a, nitu ki gbungblu'a ni kama niyi.
Da ku na duniya ne, da duniya ta kaunace ku kamar nata. Amma saboda ku ba na duniya bane, na kuma zabe ku daga duniya, don haka duniya take kin ku.
20 Bi ka rimren ikpe wa Mi na hla ni yiwu'a, “Igran na zan tiko ma ni ninkon na.” Inde ba ti me di, biyi me ba tiyi di'a, inde ba hu tre mu, ba hu tre mbi ngame.
Ku tuna da maganar da na yi muku, 'Bawa ba ya fi Ubangijinsa girma ba.' Idan sun tsananta mani, ku ma za su tsananta maku; Idan sun kiyaye maganata, za su kuma kiyaye maganarku.
21 Ba ti bibi kpe mba ni yiwu wawu ni tu inde Mu, niwa ba na toh indji wa a ton me na.
Za su yi maku duk wadannan abubuwa saboda sunana, don basu san wanda ya aiko ni ba.
22 Mi na ye tre ni ba na, ba na he ni lahtre na, u zizan, ba na he ni kpe u gbisron tu lahtre mba na.
Da ban zo na yi masu magana ba, da basu da zunubi, amma yanzu, basu da wata hujja don zunubinsu.
23 Indji wa a kama ni Me, a kama ni Ti Mu.
Duk wanda ya ki ni ya ki Ubana.
24 Mi na ye ti ndu kpe wa ko indrjori na ti bre ti na ni mi mba na, bana heni lahtre na, u zizan ba to ye, ba ka mba ni Me ni Ti Mu wawu.
Da ban yi ayyukan da babu wanda ya taba yinsu a cikin su ba, da basu da zunubi, amma yanzu sun gani, sun kuma ki ni da Ubana duka.
25 Ba ti ngari ni ndu itre wa ba nha zi ni tron'a, 'Ba kamba ni Me migyen.
An yi wannan kuwa domin a cika maganar da ke rubuce a cikin shari'arsu, ' Sun ki ni ba dalili.'
26 Indji u no si sron ni ta ye - wa Mi ton ye yiwu rji ni ti'a, ahi Ibrji u njanji (Ruhu Gaskiya), iwa a rju rji ni Ti'a aye, ani no gban (shaida) nitu Mu.
Sa'adda Mai Ta'aziya- wanda zan aiko maku daga wurin Uban, wato, Ruhun gaskiya, wanda ke fita daga wurin Uban-ya zo, zai bada shaida a kai na.
27 Bi no gban nitu wa bi he yayi tun rji ni mumla.
Ku ma kuna bada shaida saboda kuna tare da ni tun daga farko.

< Yohana 15 >