< Ndu Manzaniba 5 >
1 Ndhiri bayo ndi Ananias mba wama safira ba ban bubumba ri le.
To wani mutum mai suna Ananiyas tare da matarsa Saffiratu, shi ma ya sayar da wata mallakarsa.
2 Nda zi mbru nkle wa ba kpa`a (uwama ngame a to), nda nji mbru nkle ka zi ni za manzaniba.
Da cikakken sanin matarsa ya ajiye sashi daga cikin kuɗin don kansa, ya kuma kawo sauran ya ajiye a sawun manzanni.
3 Bitrus a tre ndi, “Ananias wu ti he ni du brij shusron me nda du, u tiche ni Ruhi Tsatsra ni kma mbru nkle bubua'a zi ni tume?
Sai Bitrus ya ce, “Ananiyas, ta yaya Shaiɗan ya cika zuciyarka haka da ka yi wa Ruhu Mai Tsarki ƙarya ka kuma ajiye wa kanka sauran kuɗin da ka karɓa na filin?
4 Niwa wuna rhihe u banle'a ana wumena, u niwa wu banle ana rhihe ni wome na? A nha yo kpeyi ni suron me? wuna tiche ni ndhi na, ama ni irjhi”.
Ba naka ba ne kafin ka sayar da shi? Bayan da ka sayar da shi kuma, kuɗin ba naka ba ne? Me ya sa ka yi tunanin yin irin wannan abu? Ba mutum ne ka yi wa ƙarya ba, Allah ne ka yi masa.”
5 Niwo tre`a Ananias a ku rhoku u veri ma ka klekle, u biwa ba wo kpe yi ba ti sisiri kpukopme.
Da Ananiyas ya ji wannan, sai ya fāɗi ya mutu. Sai babban tsoro kuwa ya kama duk waɗanda suka ji abin da ya faru.
6 Mri rize ba balu banwu cibi nda lo u nda ba u rhu ka rhu.
Sai samari suka zo gaba, suka naɗe gawarsa, suka fitar da shi suka je suka binne.
7 Niwa nton tra ati, uwama a riye, ana to ka ngye si grensi zren na.
Bayan kusan awa uku, sai matarsa ta shigo, ba da sanin abin da ya faru ba.
8 Bitrus a tre niwu ndi, “Hla nitawu bi le ni bubumbi mba nitu kpe to yi?” A tre ndi “Ehh, nitu toki.”
Bitrus ya tambaye ta ya ce, “Gaya mini, kuɗin da yake da Ananiyas kuka sayar da filin ke nan?” Ta ce, “I, haka ne muka sayar.”
9 Mle Bitrus alha niwu ndi, “Ahi ngyeti du yi zontu ni kpambi ndi tsra Ruhu Baci?, ya, za ndhi wa baka rhu lon me ba he ni kontra, ba banwu hi rhu.”
Bitrus ya ce mata, “Ta yaya kuka yarda ku gwada Ruhun Ubangiji? Duba! Sawun mutanen da suka binne mijinki suna bakin ƙofa, za su kuwa ɗauke ki zuwa waje ke ma.”
10 A kri ku rhoku ni za ma nda gbron vri ma wu kle. Niwa mir nzeba ba ri ye nimi ba to a que nda banwu rhu ka rhu ni kosan bei lonma.
Nan take ta fāɗi a ƙafafunsa ta mutu. Sai samarin suka shigo ciki, suka kuwa same ta matacciya, suka ɗauke ta suka kai ta waje suka binne ta kusa da mijinta.
11 sisir rigra ma a ti eklisiya wawu ni biwa bawo kpi biyi”a.
Babban tsoro ya kama dukan ikkilisiya da kuma duk wanda ya ji game da abubuwan nan.
12 ikpi gbugbuwu wa bana taba to ni son ba na ni chu tro nkankan ba kiya faru ni cikin ndi tawuri mazani ba. Ba ki wawumba ni trankon solomon.
Manzannin suka yi ayyukan da alamu masu banmamaki masu yawa a cikin mutanen. Dukan masu bi kuwa sukan taru a Shirayin Solomon.
13 Mbru ndhi ba bana hini gbengble suron u huba hikina ama ndhiba ba to ba ni nfutu.
Ba wanda ya yi karambanin shiga cikinsu, duk da haka mutane suna girmama su ƙwarai.
14 Nikima, ndhi ba ta ye nda ni kpa Bau; ndi lilon baba mba gbugbuwu.
Duk da haka, maza da matan da suke gaskata ga Ubangiji sai ƙaruwa suke, suka kuma ƙaru a yawa.
15 Nda duba vu bi lilo thuka zi nitu nkon tu bubu kru ko ni bla krumba, ndi i dan Bitrus si zren zu, iwhi ma ni ku nitu bari mba.
A sakamakon haka, mutane suka kawo marasa lafiya a tituna suka kwantar da su a kan gadaje da tabarmai domin aƙalla inuwar Bitrus za tă bi kan waɗansunsu yayinda yake wucewa.
16 Kpandhi ngame ba ye rhi ni gbu biwa ba ne we were ni urishilima, ni bi lilo baba biwa meme brjhi loba, ba kpa si kpa mba
Jama’a ma suka tattaru daga garuruwa kewaye da Urushalima suna kawo marasa lafiyarsu da kuma waɗanda mugayen ruhohi suke damun su, dukansu kuwa suka warke.
17 Nikima, niko firist alu kri, ni wawu biwa ba heniwu'a (biwa ba he ni derika sadukiawa); ba shuni ngu,
Sai babban firist da dukan abokan aikinsa, waɗanda suke na ƙungiyar Sadukiyawa suka cika da kishi.
18 nda yo wo vu manzani ba ka tro ni buba tro. “
Suka kama manzannin suka sa su a kurkukun da ake sa kowa da kowa.
19 Nikimame, niwa chu ati malaika u Baci a bwunko wu bubu tro'a nda njiba rhu ra, nda tha bawu ndi
Amma da dare wani mala’ikan Ubangiji ya buɗe ƙofofin kurkukun ya fitar da su.
20 “Hi, kri nimi Haikali ni tre ndi ndhiba wawu nitu lantre wu nu vriji”.
Ya ce, “Ku je ku tsaya a filin haikali ku sanar wa mutane cikakken saƙon wannan sabon rai.”
21 Niwa ba wo tre yi a, ba ri hi ni haikalia tsra ni bwunble nda tsroba. I a ninkon firt a ye baba biwa baheni wu'a nda yo son shubi bi ninkon gbu baba datibai ndhi bi Israila wawumba, nda tonba hi ni ko tre duba hi nii manzani ba ye.
Da gari ya waye, sai suka shiga filin haikali, yadda aka faɗa musu, suka kuwa fara koyar da mutane. Sa’ad da babban firist da abokan aikinsa suka iso, sai suka kira Majalisa gaba ɗaya dukan dattawan Isra’ila, suka kuma aika kurkuku a zo da manzannin.
22 Ofisa wa ba tonbarba hi ka waba hamani ko tro'a nda kima ye lha bawu.
Amma da dogarawan suka iso kurkukun, ba su same su a can ba. Saboda haka suka dawo suka ba da labari, suka ce,
23 “Kika to nkotraba baki ni tro vrenme, ni bi ki gben ba ni kontra. Ama niwa ki bwu ni ri, kina to ndior nimi na.
“Mun iske kurkukun a kulle sosai, da masu gadi suna tsaye a bakin ƙofofin; amma da muka buɗe su, sai muka tarar ba kowa a ciki.”
24 Ni wo tre yi, captin wu haikalia mba ninko first wawu, ba ku sisiri nitu mba, don kpe wa ni wu gon ma.
Da jin wannan labari, sai shugaban masu gadin haikali da manyan firistocin suka ruɗe, suna tunanin abin da wannan al’amari zai zama.
25 Mle ndhiri a ye nda ye lha bawu ndi, “Ndhi wa bi vu sru ni ko tro ba kri si tero ndhi ni mi haikali.”
Sai wani ya zo ya ce, “Ga shi! Mutanen da kuka sa a kurkuku suna tsaye a filin haikali suna koya wa mutane.”
26 Kaptin babamir binduma ba wru hi nda ka vu ba ye, hama ni gbiba ni gbeneblen, nitu ba ti sisiri ko ndhi ba ta ba ni tita.
Da wannan, shugaban ya tafi tare da dogarawansa suka kawo manzannin. Sun kawo su amma fa ba ƙarfi da yaji ba, don suna tsoro kada mutane su jajjefe su da duwatsu.
27 Niwa ba njiba ye'a ba zi ba shishi bi ninkon'a,
Da suka kawo manzannin, sai suka sa su suka bayyana a gaban Majalisar don babban firist ya tuhume su.
28 Nikon first a tsra ba ni mye ndi, “we mha yi ndife yi ton du yi na tsro ni nde yi na, ama bi ka gbu urishilima ni tsro mbi ndi nison nji yi guyi ye sa nitumbu.”
Ya ce, “Mun kwaɓe ku da gaske kada ku ƙara koyarwa cikin wannan suna, duk da haka kun cika Urushalima da koyarwarku, har ma kuna so ku ɗora mana laifin jinin mutumin nan.”
29 Bitrus baba manzaniba ba sa ndi, kita ki hu tre irjhi zan tre ndhi.
Bitrus da sauran manzannin suka amsa suka ce, “Dole ne mu yi wa Allah biyayya a maimakon mutane!
30 Irjhi ba timbu a nzu Yesu hi, wandi bi klo wuu ni kunkro.
Allahn kakanninmu ya tā da Yesu daga matattu, wanda kuka kashe ta wurin ratayewa a bisan itace.
31 Irjhi a nzu u hon hi ni woko ko rhima na uren u tuchu mba wu kpachuwo, don du buw kon tuba ni mir Israila, nda wru latre mba lhe.
Allah ya ɗaukaka shi zuwa hannun damansa a matsayin Yerima da Mai Ceto don yă kawo tuba da gafarar zunubai ga Isra’ila.
32 kita ki biwa ki to kpibiyi, ni ruhu tsatsra ngame, wandi Irjhi a nu bi wa ba hu tre ma'a.
Mu shaidu ne ga waɗannan abubuwa, haka kuma Ruhu Mai Tsarki, wanda Allah ya ba wa waɗanda suke yin masa biyayya.”
33 Niwa, bi ninko wa ba son'a da trea nfu a toba, u bata son wuu manzani ba.
Da suka ji haka, sai suka yi fushi suka so su kashe su.
34 Ama igu pharisawa ri wu nde ma hi Gamalial ndhi wu tsro doka, wandi ndhi wawu ba kpanyme ni wu'a, a lu kri ni minba nda ti gbuchu du manzani ba rhu dinko ni bawu wu ton fime ri.
Amma wani Bafarisiyen da ake kira Gamaliyel, wani malamin doka, wanda dukan mutane ke girmamawa, ya miƙe tsaye a Majalisar ya umarta a fitar da mutanen waje na ɗan lokaci.
35 Wa alu kri lha ni son ndi, “ndhi Israila, mal ya kpe wa bi tre bi ti ni ndhi biyi.
Sa’an nan ya yi musu jawabi ya ce, “Mutanen Isra’ila, ku yi kula da kyau da abin da kuke niyyar yi wa mutanen nan.
36 Kafi du vi biyi ye, Theudus a lu wru nda gbresan ndi wawu hi ndior, u ndhi bari, ba derinzia ba zontu hu. Ba wuu, duka biwa bata hu'a ba vra hi kankan ni zremba ngame a na ti tu na.
Kwanan baya, Teyudas ya ɓullo, yana cewa wai shi wani mutum ne, kuma wajen mutane ɗari huɗu suka bi shi. Aka kuwa kashe shi, dukan masu binsa kuwa suka watse, kome ya wargaje.
37 Bay ki ma u, Juda wu Galile a lu kri ni vi wa ba bla ndhi nda gbron bari baka hu. wawu ngame a que kado u biwa bata hu'a ba vera hi kan kan.
Bayansa, Yahuda mutumin Galili ya ɓullo a kwanakin ƙidaya, ya jagoranci mutane cikin tawaye. Shi ma aka kashe shi, dukan mabiyansa kuma aka watsar da su.
38 Zizan mi lhayiwu, rhu ni nkon ndhi biyi di don ba toome, idan shiri yo ko ndu yi, hi wundi ana kri gban me na nda vralhe.
Saboda haka, a wannan batu na yanzu, ina ba ku shawara. Ku ƙyale mutanen nan! Ku bar su su tafi! Gama in manufarsu ko ayyukansu na mutum ne, ai, zai rushe.
39 Anita ndu Irjhi, bina iya yi nasara ni ba na bi klna to bisi tsi ni Irjhimu.” Toki ba kpanyme ni tre ma.
Amma in daga Allah ne, ba za ku iya hana waɗannan mutane ba, za ku dai sami kanku kuna gāba da Allah ne.”
40 Mle ba yo manzaniba ri ni son nda lhobatsi nda hla ndi du ba na tre ni nde Yesu na, nda du ba hi kpamba.
Jawabinsa ya rinjaye su. Suka kira manzannin suka sa aka yi musu bulala. Sa’an nan suka kwaɓe su kada su ƙara magana a cikin sunan Yesu, suka kuma bar su suka tafi.
41 Ba rhu rhi ni son bi ninko'a ni takpe don ba he ni mi biwa ba mla duba ti ba ya nitu ndema.
Manzannin suka bar Majalisar, suna farin ciki domin an ga sun cancanta a kunyata su saboda Sunan nan.
42 Hu kima, chachu, ni mi haikali mba ni ko hi ni ko, ba zi tsro ndani d'bu ni lha njo ndi Yesu wawuyi hi Kristi.
Kowace rana, a filin haikali da kuma gida-gida, ba su fasa koyarwa da kuma shelar labari mai daɗi cewa Yesu shi ne Kiristi ba.