< Ndu Manzaniba 3 >
1 Niki Bitrus mba yohanna basiya hon ni hi ni tra Rji ninton wu bre, mton wu tiya.
Sa'adda Bitrus da Yahaya suna hanya zuwa haikali a lokacin addu'ar karfe uku.
2 Ba zontu ni ndhi ri, wa a chon kple rhini nine yimma, ba banu bibanmu ye zi ni kikle nkontra hekali wa ba yondi, “wu bi”. Ba ta kau zi niki chachu ni du ta bre biwa ba si rinimi hekalia.
Wani mutum, gurgu ne tun daga haihuwa, ana daukar sa kulluyomi zuwa kofar haikali da ake kira Kyakkyawa, domin bara gun mutanen da ke shiga haikalin.
3 Niwa a to Bitrus mba Yohana Basia rini hi nimi hekalia a bre ba du ba nuu kpe.
Da ya ga Bitrus da Yahaya suna shiga haikalin, sai ya roke su sadaka.
4 Bitrus a yo shishi nda gba a me mba Yohana niki, nda tre ndi, “ya ta”.
Bitrus da Yahaya kuwa suka zuba masa ido, Bitrus ya ce, ''Ka dube mu.''
5 Ndi wa chon kple'a nzu shishi nda yaba ni yo suron da ni kpakpe ni womba.
Gurgun nan kuwa ya dube su, yana tsammanin zai sami wani abu a wurin su.
6 Ama Bitrus tre ndi “mina he ni silva mba Zinariya na, ikpe wa mihe niwu, mi nu. Ni nde Yesu Kristi wu Nazarat, lu zren”
Amma Bitrus ya ce, “Azurfa da Zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, zan baka. A cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, Yi tafiya''
7 Bitrus a tiwo vu u ni woma wu ko rhi da nzu u lunde, mle iza mba toza ma ba sen ququ.
Bitrus ya kama hannun damarsa, ya daga shi; nan da nan kafafunsa da kashin idon sawayensa suka samu karfi.
8 Gurugu mba a duo lunde kri nda ni zren; nda rhi hu ba Bitrus mba Yohana hinimi haikalia, ni zren da za ndani yose wu gbre Irjhi san
Da gurgun ya yunkura, ya mike tsaye sai ya fara takawa; ya shiga haikali tare da Bitrus da Yahaya, yana takawa, yana tsalle, yana kuma girmama Allah.
9 Ndhi ba wawumbawu ba too si zren ndani yose u gbre Rji san.
Dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana kuma yabon Allah.
10 Ba ya nda to ahi gu wa atason ndani bre nkle ni kikle nkontra haikali wa ba yondi nkontra wu bi a sisiri ni mre a shubawu ni suron nitu kpe wa ba to ni igu'a.
Sun lura cewa, shine mutumin da ke zama yana bara a Kyakyawar kofar haikali; sai suka cika da mamaki domin abin da ya faru.
11 Niwa a si hu za Bitrus mba Yohana, ndhi ba ba tsutsu hi riba ni nkalhang nyunko wa ba yo hihiwu Sulemanu a ndani bwu nyu yo ni wuo nitu kikle kpe wa a he nitu ma'a.
Yayin da yake rike da Bitrus da Yahaya, dukan jama'a suka matso wurinsu, a gefen dakalin Sulaimanu, suna ta mamaki kwarai.
12 Niwa Bitrus a to toki, a sa ni ndhi ba ndi. “Biyi Ndi lilon bi Israila, a ngye du yi ni bwunyu ni yo ni wuho? Nitu nagye bi sru shishi nita, rhuto kitaayi ki du gua lu zren ni gbengblen mbu koka ni gbugblu mbu
Da Bitrus ya ga haka ya amsa wa jama'ar, “Ya ku mutanen Isra'ila, don me ku ke mamaki?” Don me ku ka zura mana ido, kamar mu ne muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu?
13 Irjhi wu Ibrahim, mba wu Ishaku, ni wu Yakubu, Irjhi wu ba timbu, wawuyi a gbre veren ma Yesu san. Wa wuyi bina vuu lo di kaambi ni wu ni shishi Pilate, wa a ta son shu chuwo'a.
Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allah na iyayenmu ya girmama bawansa Yesu. Shi kuka ki kun kuma bashe shi a gaban Bilatus da ya so ya sake shi.
14 Bi kanmbi ni Tsatra mba wa a hamma ni atre, ni mye du ba chundhi wa a wuu ndi mu chuwo niyiwu.
Kuka ki Mai Tsarkin nan, Mai Adalcin, maimakon haka kuka ce a sakkar maku mai kisan kai.
15 Bi wuu wa ivri rhurhi niwu, wandi jrjhi a nzu lunde baya qu-e kita ki bi wa kito ni shishimbu.
Kun kashe mai ba da rai, wanda Allah ya tayar daga matattu, mu kuwa shaidu ne ga wannan al'amari.
16 Nitu kpanyme ni suron riri ni ndema; ndema a du guyi, wa bisi ya ni to ou, a lu kri ni gbengblen ma. kpanyme ma ni Yesu a nu si kpa ni shishi mbi wawu.
Yanzu, ta bangaskiya ga sunansa - wannan mutum da kuke gani kuma kun san shi - ta wurin wannan sunan ne ya sami karfi. Bangaskiya cikin Yesu ta ba shi cikakkiyar lafiya, a gabanku duka.
17 Zizan, mir vayi mi to ndi, bi na tona biyi baba bininko mbi, ekpe wa bi tio.
Ya ku 'yan'uwa, na san kun yi haka ne cikin rashin sani, yadda shugabaninku suka yi.
18 Ama kpe wa Irjhi ana lhazi ni nyu anabawama, ndi kristi ni ti ya, kima a ye ku tou ki.
Amma duk abubuwan da Allah ya fada ta bakin dukan anabawansa, cewa Almasihunsa zai sha wahala, yanzu ya cika.
19 Kima gon nu latre di du ba wru latre mbe hlega.
Saboda haka, Ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, domin lokacin sabuntuwa daga wurin Ubangiji ya zo;
20 Niton wa bi he tare ni Baci wa a ni ton kristi wa a mla yo ni yiwu Yesu.
domin a aiko maku da Almasihu wanda aka kaddara wato, Yesu.
21 Wa wuyi shulu ni kpa har hi ni nton wa kpi ba k'ma ye ti ndidi Irjhi a tre nisen, ni nyu tsatra anabawa ma'a. (aiōn )
Shine wanda dole sama ta karbe shi har zuwa lokacin komo da dukan abubuwa, game da abubuwan da Allah ya fada tun da ta bakin annabawansa tsarkaka. (aiōn )
22 Musa a hla ndi. “Baci Irjhi ni nzu anabi grji kama too me nimi mir vayimbi. Bi woowu ni kpi wa ani tre yiwu nitu mba.
Musa hakika ya ce, 'Ubangiji Allah zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin, 'yan'uwanku. Za ku saurari dukan abin da zai fada maku.
23 Andi ko nah wa a kama bubu wotre anabi kima, ba gbron ba lhe penpenme ni mi mbru ndhi
Zai kasance kowanne mutum da bai saurari annabin nan ba za a kau da shi gabadaya daga cikin mutanensa.'
24 A toki, anabawa ba wawu rhi ni samuila nibi ye ni kogonba, ba tre nda d'bu lha vi biyi.
I, dukan annabawa tun daga Sama'ila da wadanda suka zo bayansa, sun yi magana sun ambaci wadannan kwanaki.
25 Bi mi anabawa mba ni shirjhi wa Irjhi a tiniba bacimbi, niwa a lha ni Ibrahim ndi, “Ni zuriya me nnedhi ni gbungblu wawu ba kpa lulu.”
Kune 'ya'yan annabawa da na alkawari wanda Allah ya yi da kakanninku, yadda ya ce wa Ibrahim, 'Daga zuriyarka dukan al'uman duniya za su sami albarka.'
26 Ni wa Irjhi a nzu ndi wunduma a tonye niyi guci, nitu du yo lulu niyiwu, ni du konhambi k'ma gon nu meme drimbi.
Bayan da Allah ya ta da bawansa, a gareku ne ya fara aiko shi, domin ya albarkace ku tawurin juyadda kowannenku daga muguntarsa.”