< Ndu Manzaniba 3 >
1 Niki Bitrus mba yohanna basiya hon ni hi ni tra Rji ninton wu bre, mton wu tiya.
Wata rana, Bitrus da Yohanna suna haurawa zuwa haikali a lokacin addu’a da ƙarfe uku na rana.
2 Ba zontu ni ndhi ri, wa a chon kple rhini nine yimma, ba banu bibanmu ye zi ni kikle nkontra hekali wa ba yondi, “wu bi”. Ba ta kau zi niki chachu ni du ta bre biwa ba si rinimi hekalia.
To, sai ga wani da aka haifa gurgu ana ɗauke da shi zuwa ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, inda akan ajiye kowace rana, don yă yi bara daga masu shigowa cikin filayen haikali.
3 Niwa a to Bitrus mba Yohana Basia rini hi nimi hekalia a bre ba du ba nuu kpe.
Da ya ga Bitrus da Yohanna suna gab da shiga, sai ya roƙe su kuɗi.
4 Bitrus a yo shishi nda gba a me mba Yohana niki, nda tre ndi, “ya ta”.
Bitrus kuwa ya kafa masa ido, haka ma Yohanna. Sai Bitrus ya ce, “Dube mu!”
5 Ndi wa chon kple'a nzu shishi nda yaba ni yo suron da ni kpakpe ni womba.
Saboda haka mutumin ya mai da hankalinsa a kansu, yana fata samun wani abu daga gare su.
6 Ama Bitrus tre ndi “mina he ni silva mba Zinariya na, ikpe wa mihe niwu, mi nu. Ni nde Yesu Kristi wu Nazarat, lu zren”
Sai Bitrus ya ce, “Azurfa ko zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. A cikin sunan Yesu Kiristi Banazare, ka yi tafiya.”
7 Bitrus a tiwo vu u ni woma wu ko rhi da nzu u lunde, mle iza mba toza ma ba sen ququ.
Ta wurin kama hannunsa na dama, ya taimake shi ya miƙe, nan take ƙafafu da idon sawun mutumin suka yi ƙarfi.
8 Gurugu mba a duo lunde kri nda ni zren; nda rhi hu ba Bitrus mba Yohana hinimi haikalia, ni zren da za ndani yose wu gbre Irjhi san
Sai ya yi wuf da ƙafafunsa ya fara tafiya. Ya tafi tare da su ya shiga cikin filin haikali yana tafiya yana tsalle, yana kuma yabon Allah.
9 Ndhi ba wawumbawu ba too si zren ndani yose u gbre Rji san.
Sa’ad da dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana yabon Allah,
10 Ba ya nda to ahi gu wa atason ndani bre nkle ni kikle nkontra haikali wa ba yondi nkontra wu bi a sisiri ni mre a shubawu ni suron nitu kpe wa ba to ni igu'a.
sai suka gane cewa shi ne mutumin nan wanda dā yake zama yana bara a bakin ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, suka kuwa cika da mamaki da tsoro a kan abin da ya faru gare shi.
11 Niwa a si hu za Bitrus mba Yohana, ndhi ba ba tsutsu hi riba ni nkalhang nyunko wa ba yo hihiwu Sulemanu a ndani bwu nyu yo ni wuo nitu kikle kpe wa a he nitu ma'a.
Tun mai bawan yana riƙe da Bitrus da Yohanna, dukan mutanen suka yi mamaki, suka zo wurinsu a guje a inda ake kira Shirayin Solomon.
12 Niwa Bitrus a to toki, a sa ni ndhi ba ndi. “Biyi Ndi lilon bi Israila, a ngye du yi ni bwunyu ni yo ni wuho? Nitu nagye bi sru shishi nita, rhuto kitaayi ki du gua lu zren ni gbengblen mbu koka ni gbugblu mbu
Da Bitrus ya ga haka, sai ya ce musu, “Mutanen Isra’ila, don me wannan ya ba ku mamaki? Don me kuke kallonmu sai ka ce da ikon kanmu ne ko kuwa don ibadarmu ne muka sa wannan mutum ya yi tafiya?
13 Irjhi wu Ibrahim, mba wu Ishaku, ni wu Yakubu, Irjhi wu ba timbu, wawuyi a gbre veren ma Yesu san. Wa wuyi bina vuu lo di kaambi ni wu ni shishi Pilate, wa a ta son shu chuwo'a.
Allah na Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub, Allah na kakanninmu, ya ɗaukaka bawansa Yesu. Ku kuka ba da shi domin a kashe, kuka yi mūsun saninsa a gaban Bilatus, ko da yake ya yi niyya ya sake shi.
14 Bi kanmbi ni Tsatra mba wa a hamma ni atre, ni mye du ba chundhi wa a wuu ndi mu chuwo niyiwu.
Kuka yi mūsun sanin Mai Tsarki da Mai Adalci kuka roƙa a sakar muku mai kisankai.
15 Bi wuu wa ivri rhurhi niwu, wandi jrjhi a nzu lunde baya qu-e kita ki bi wa kito ni shishimbu.
Kuka kashe tushen rai, amma Allah ya tashe shi daga matattu. Mu shaidu ne ga wannan.
16 Nitu kpanyme ni suron riri ni ndema; ndema a du guyi, wa bisi ya ni to ou, a lu kri ni gbengblen ma. kpanyme ma ni Yesu a nu si kpa ni shishi mbi wawu.
Ta wurin bangaskiya cikin sunan Yesu ne wannan mutum da kuke gani kuka kuma sani ya sami ƙarfi. Da sunan Yesu, da kuma bangaskiyar da take samuwa ta wurinsa ne ya ba shi cikakkiyar warkarwa, yadda dukanku kuke gani.
17 Zizan, mir vayi mi to ndi, bi na tona biyi baba bininko mbi, ekpe wa bi tio.
“To,’yan’uwa, na san cewa, kun aikata wannan cikin jahilci ne, yadda shugabanninku suka yi.
18 Ama kpe wa Irjhi ana lhazi ni nyu anabawama, ndi kristi ni ti ya, kima a ye ku tou ki.
Amma ta haka ne Allah ya cika abin da ya rigyafaɗi ta bakin dukan annabawa cewa, Kiristinsa zai sha wahala.
19 Kima gon nu latre di du ba wru latre mbe hlega.
Saboda haka ku tuba, ku juyo ga Allah, don a shafe zunubanku, don lokutan wartsakewa su zo daga wurin Ubangiji,
20 Niton wa bi he tare ni Baci wa a ni ton kristi wa a mla yo ni yiwu Yesu.
don kuma ya iya aika da Kiristi, wanda aka naɗa tun dā saboda ku, Yesu ke nan.
21 Wa wuyi shulu ni kpa har hi ni nton wa kpi ba k'ma ye ti ndidi Irjhi a tre nisen, ni nyu tsatra anabawa ma'a. (aiōn )
Dole yă kasance a sama, sai lokaci ya yi da Allah zai mai da kome sabo, yadda ya yi alkawari tun dā ta wurin annabawansa masu tsarki. (aiōn )
22 Musa a hla ndi. “Baci Irjhi ni nzu anabi grji kama too me nimi mir vayimbi. Bi woowu ni kpi wa ani tre yiwu nitu mba.
Gama Musa ya ce, ‘Ubangiji Allahnku zai tasar muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku; dole ku saurari duk abin da ya faɗa muku.
23 Andi ko nah wa a kama bubu wotre anabi kima, ba gbron ba lhe penpenme ni mi mbru ndhi
Duk wanda bai saurare shi ba za a ware shi gaba ɗaya daga mutanensa.’
24 A toki, anabawa ba wawu rhi ni samuila nibi ye ni kogonba, ba tre nda d'bu lha vi biyi.
“Tabbatacce, dukan annabawa daga Sama’ila zuwa gaba, dukansu da suka yi magana, sun rigya faɗin waɗannan kwanaki.
25 Bi mi anabawa mba ni shirjhi wa Irjhi a tiniba bacimbi, niwa a lha ni Ibrahim ndi, “Ni zuriya me nnedhi ni gbungblu wawu ba kpa lulu.”
Ku kuwa magādan annabawan ne da kuma na alkawarin da Allah ya yi da kakanninku. Ya ce wa Ibrahim, ‘Ta wurin zuriyarka, dukan kabilan duniya za su sami albarka.’
26 Ni wa Irjhi a nzu ndi wunduma a tonye niyi guci, nitu du yo lulu niyiwu, ni du konhambi k'ma gon nu meme drimbi.
Da Allah ya tashe bawansa, ya aike shi da fari zuwa gare ku don yă albarkace ku ta wurin juye kowannenku daga mugayen hanyoyinku.”