< Ndu Manzaniba 26 >
1 Niki Agrippa a tre ni Bulus, “Wu ka tre kime.” Nikima Bulus a nmerju ni woma nda lu tre wu kpa tuma chuwo.
Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “An ba ka izini ka yi magana.” Saboda haka Bulus ya yi alama da hannunsa ya fara kāriyarsa.
2 “Mi ban ndi mi ngyiri ni kpamu, Ichu Agrippa, ni wa mi nji tre mu niye ni shishime luwa, nitu wawu kpi meme wa Yahudawa ba nji ye nha nimu niwuu;
Ya ce, “Sarki Agiriffa, na yi sa’a da na tsaya a gabanka yau yayinda nake kāriyata game da dukan zargin Yahudawa,
3 kima me nitu wu to zan tu ni tu nkon zren Yahudawa rhini sen. Niki, mi bre du u wome ni kru sron.
musamman ma domin ka saba sosai da dukan al’adun Yahudawa da kuma maganganunsu. Saboda haka ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
4 Njanji, Yahudawa wawu ba to zren son mu rhini wa mi vren nze ni meme mu mba ni Urushelima.
“Yahudawa duk sun san yadda na yi rayuwa tun ina yaro, daga farkon rayuwata a ƙasarmu da kuma a Urushalima.
5 Ba to nitumu rhini ni mumla, batini son nyme niki, nitu mison na Farasii, grji bi kri gbangban ni nkon hu Irji mbu.
Sun san ni tun da daɗewa za su kuwa shaida, in suna so, cewa bisa ga ɗarikar addininmu mafi tsanani, na yi rayuwar Bafarisiye ne.
6 Zizan mi kri ni wayi du ba gaatre nimu nitu yo sron mu ni yo sron kpe ni shishi wa Irji a ti ni ba titi mbu.
Yanzu kuwa saboda begena cikin abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari ne, ake mini shari’a yau.
7 A he nitu yo sron kpe ni shishi wa ba grji wlon don ha ba ba yo sron wu kpa niwa ba nzu nde Irji hon ni chu mba ni virhi. Wa a he nitu yo sron a, Ichu Yahudawa ba ban nha me.
Wannan shi ne alkawarin da kabilanmu goma sha biyu suke bege su ga cikawarsa, yayinda suke bauta wa Allah da himma dare da rana. Ya Sarki, saboda wannan bege ne fa Yahudawa suke zargena.
8 A ngye nizu du mla ya ni kpanyme ndi Irji ni nzu indji lu rjini kwu?
Don me wani a cikinku zai yi shakka cewa Allah yana tā da matattu?
9 Zizan, a toki, Ime me mina ta mren ndi mi ti kpi gbugbuwu nitu ka nde Yesu wu Nazarat su.
“Ni ma a dā na tabbata cewa ya kamata in yi duk abin da zan iya yi domin in yi gāba da sunan Yesu Banazare.
10 Mi ti kpi biyi ni Urushelima, Mi vu loyo ni mi tratro gbugbu indji tsatsra wu Irji, ni vunvu kpanyme wa mi kpa rhini ninkon Prist, mba niwa ba sia wuuba, mi yo wo nyime mu nitu kima.
Abin da na yi ke nan a Urushalima. Da izinin manyan firistoci na sa tsarkaka da yawa a kurkuku, sa’ad da kuma ake kashe su, nakan ka da ƙuri’ata gāba da su.
11 Mi ti ba ya, nton gbugbuwu ni mi Sinagog, mba ni ta tsra yoba ni gbengblen du ba tre meme ntiu Irji. Mi ta vra ni nfu nitumba, mba nini tiba ya ka rhini igbu wu meme bari.
Sau da dama nakan bi majami’a-majami’a, in sa a yi musu hukunci. Na kuma yi ƙoƙarin tilasta su su yi saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.
12 Niwa mi sia ti toyi, mi hini Damaskus ni yawo kpanyme mba nu nkon rhini kikle Prist;
“A cikin irin tafiye-tafiyen nan ne ina kan hanya zuwa Damaskus tare da izini daga manyan firistoci.
13 mba ni nkon, hiki, ni tsutsu irji, ichu, mi to kpan lu rjini shulu wa a kpan zan irji, nda bwu kpan kagon me baba indji biwa bana si zren hume.
Da tsakar rana, ya sarki, sa’ad da nake kan hanya, sai na ga wani haske daga sama, fiye da hasken rana, yana haskakawa kewaye da ni da abokan tafiyata.
14 Niwa wawumbu ki kurjoku ni meme mi wo ilan ni tre ni me ni ilbe Ibraniyawa ndi Shawulu, Shawulu, u i tie me ya nitu ngye? A ni he ni ya ni du chuza too kpe wu ntsen nyu.
Dukanmu muka fāɗi ƙasa, na kuwa ji wata murya tana ce mini da harshen Arameyik, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Yana da wuya ka shuri tsinken tsokanar dabba.’
15 Niki mi tre ndi, “Wu nha, Bachi?” I Bachi a sa mu ndi, 'A hi me Yesu wa wu si tiwu ya.
“Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
16 Zizan lu kri ni zande; anitu ndu yi mi tsro kpamu niwu, nitu youyo ni tindu vrenko, mba wa wu vu bla nitu kpi wa wuto nitumu zizan mba kpi wa mi tsro ni ko shishi;
Yanzu ka tashi, ka tsaya da ƙafafunka. Na bayyana a gare ka don in naɗa ka bawa da kuma mai shaidar abin da ka gani game da ni da kuma abin da zan nuna maka.
17 i mi kpau chuwo rhini wo indji ba mba rjini Bikora wa mi si ton ni hi niba,
Zan tsirar da kai daga mutanenka da kuma daga Al’ummai. Ina aikan ka zuwa gare su domin
18 ni du hi bwu shishi mba, ndi kma ba sran rjini bwu hini kpan mba rjini son niwobrji shango hini Irji, ni du ba kpa rjini Irji, kpa wru latre mba (gado) wa mi nu ibiwa ba kri bi nitu kpanyme ni me.
ka buɗe idanunsu su kuwa juyo daga duhu zuwa haske, daga mulkin Shaiɗan kuma zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai da kuma matsayi a cikin waɗanda aka tsarkake ta wurin bangaskiya a cikina.’
19 Ni tu kima, Ichu Agrippa, mina kamu ni hutre ira wa a rjini shulu na;
“Saboda haka fa, Sarki Agiriffa, ban yi rashin biyayya ga wahayin nan daga sama ba.
20 Mi hi ni bi Damaskus guchi, nda ka ri ni Urushelima, nda ka kagon gbungblu Judiya, mba ni bikora ngame, mi nu ba tondua, nitu du ba kma sran nda kma ye ni Irji, nda ti ndu wa a bi tsra ni kma sran sron mba.
Da farko ga waɗanda suke a Damaskus, sa’an nan ga waɗanda suke a Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya, da kuma ga Al’ummai su ma, na yi wa’azi don su tuba su juyo ga Allah su kuma tabbatar da tubansu ta wurin ayyukansu.
21 Nitu kima Yahudawa ba vu me lo nimi hekali nda ta son wuu me.
Shi ya sa Yahudawa suka kama ni a filin haikali suka kuma yi ƙoƙarin kashe ni.
22 Ni kima, me kpa zo wa a ye rji ni Irji, ye ni vi wu luwa, ndi ni kri ni nran hla ni bi tsitsa baba bi kikle ana kpe nkan na, hama niwa anabawa mba Musa ba tre ndi naiye he toki -
Amma na sami taimakon Allah har yă zuwa yau. Yanzu ga ni a tsaye a nan, ina shaida ga babba da yaro. Ba na faɗin kome fiye da abin da annabawa da Musa suka ce zai faru,
23 ndi Kristi niye ti ya, nitu wawuyi ni guchi tashme rjini kwu, ndani bwuhla ikpan ni indji mbu mba ni bi kora.”
cewa Kiristi zai sha wahala, kuma a matsayin wanda yake na fari da zai tashi daga matattu, zai yi shelar haske ga mutanensa da kuma Al’ummai.”
24 Niwa Bulus akle ngla kpama a, Festus a tre ni kikle lan, “Bulus, wu sran; to gbugbu tsro me du ni sran.”
A nan ne fa Festus ya tsai da kāriyar Bulus. Ya yi ihu ya ce, “Bulus! Kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”
25 I Bulus a tre ndi, “Mina sran na, wa azan bi Festus, mi si dbu bla lan tre wu njanji mba wu gaatre ndindi.
Bulus ya amsa ya ce, “Ba na hauka, ya mafifici Festus. Abin da nake faɗi gaskiya ne da kuma mai kyau.
26 Nitu Ichu to kpi biyi; niki mi tre ni gbengblen sron niwu, nitu mi nyme pempe ndi kpi biyi bana he ni bwu ni wu na, nitu ikpe biyi bana tiba ni kosan na.
Sarki ya san waɗannan abubuwa, ina kuma iya yin magana da shi a sake. Na tabbata cewa ba ɗaya daga cikin waɗannan da ya kuɓuce saninsa, domin ba a ɓoye aka yi shi ba.
27 Wu kpanyme ni anabawa ba, Ichu Agrippa? Mi to ndi wu kpanyme.”
Sarki Agiriffa ka gaskata da annabawa? Na san ka gaskata.”
28 Agrippa hla ni Bulus nid, ni nton fiime toyi, wu son gbronmeyo dumi kma ti Krista?”
Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “Kana tsammani cewa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kana so ka mai da ni Kirista?”
29 Bulus tre ndi, “Mi bre Irji ndi, anita nton fiime ka wu gbron me ana wu megen na, mba wawu biwa ba wo me luwa, du ba he too me, hama ni rjiri ij'bo wu ko tro yi.”
Bulus ya amsa ya ce, “Ko a ɗan lokaci, ko a lokaci mai yawa, ina addu’a ga Allah cewa, ba kai kaɗai ba amma duk waɗanda suke saurare ni a yau su zama abin da nake, sai dai ban da sarƙoƙin nan.”
30 Niki Ichua lunde kri, i gomna mba Bernice ngame, baba biwa bana ki niba.
Sai sarki ya tashi, haka kuma gwamna da Bernis da kuma waɗanda suke zaune tare da su.
31 Niwa ba rju don kikle tra u son mba, ba si tre ni kpamba ndi, “Igu yi na ti kpe wa ani tsra u kwu ko ka u lo zi na.”
Suka bar ɗakin, kuma yayinda suke magana da juna, sai suka ce, “Wannan mutum ba ya yin kome da ya isa kisa ko dauri.”
32 Agrippa a tre ni Festus ndi, kinina chu Iguyi chuwo hama wa ana bre hi to Kaisar.”
Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Da ba don wannan mutum ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba da an sake shi.”