< Ndu Manzaniba 20 >
1 Niwa gro wu a kle'a, Bulus a ton ba ka yo mri ko bi hu'a nda nron ba du ba ki gbangban, nda tre ndi duba mla ki nda kuunko hi ni Macedonia.
Sa’ad da hayaniyar ta kwanta, sai Bulus ya aika a kira almajiran, kuma bayan ya ƙarfafa su, sai ya yi bankwana ya tafi Makidoniya.
2 Niwa a zren zu ni gbungblu bi koki nda gbre ba ni lantre gbugbuwu, a ye rini Greece.
Ya ratsa wurin yana ƙarfafa mutanen da kalmomi masu yawa, a ƙarshe kuma ya kai Giris,
3 Hu gon kima a son ti wha tre niki. Yahudawa ba ba mla nkon meme ti nitu ma, niwa a ta dran hun koma hi ni Syria; nitu ki a kma sran ka zu ni Macedonia.
inda ya zauna wata uku. Da yake Yahudawa sun ƙulla masa makirci, a lokacin da yake shirin tashi cikin jirgin ruwa zuwa Suriya, sai ya yanka shawara yă koma ta Makidoniya.
4 Kpan zren ma ba wa baka rini Asia, bana sopater ivren Pyrrhus wa a rhini Berea, Aristakus mba Sekondus, hamba bana bi Tasalonika wa ba kpanyime, Gaius wu Derbe, Timoti, mba Tychicus mba Trophimus wa a rhi ni Asia.
Sai Sofater ɗan Fairrus daga Bereya, Aristarkus da Sekundus daga Tessalonika, Gayus daga Derbe, Timoti ma, da Tikikus da Turofimus daga lardin Asiya suka tafi tare da shi.
5 Ndji biyi bana guchi hi nitawu nda ka sia gbenta ni Troas.
Waɗannan mutane suka sha gaba suka kuma jira mu a Toruwas.
6 Ki dran rhuni Philippi niwa ivi bi bredi wa ana fuulu, a kle, mba ni vi u ton ki ye tsra niba ni Troas. Niki ki son u vi tangban.
Amma muka tashi daga Filibbi a jirgin ruwa bayan Bikin Burodi Marar Yisti bayan kuma kwana biyar muka sadu da sauran a Toruwas, inda muka zauna kwana bakwai.
7 Ni vi mumla u Sati ki, niwa kina zontu niki nzi bredi, Bulus a tre ni biwa ba kpanyime'a. A ta son don ba ni viwu hu kima, nitu ki a tre gbron nkon hi ni tsutsuchu.
A ranar farko ta mako muka taru wuri ɗaya don gutsuttsura burodi. Bulus ya yi wa mutane magana, don yana niyyar tashi kashegari, sai ya yi ta yin magana har tsakar dare.
8 Ilu fitila gbugbuu bana he ni tra u koshu, bubu wa kina zontu ki.
Akwai fitilu da yawa a ɗakin gidan saman da muka taru.
9 Ni windo'a, vren nze ri ni nde Eutychus a son, e inna a kri koonvu. Niwa bulus a tre la gbron nkon nha, vren nze yi, wa a risi kruna, a kurjoku rjini tuko u tra i baka baun kmomu.
Akwai wani saurayi zaune a taga mai suna Yitikus, wanda barci mai nauyi ya ɗauke shi yayinda Bulus yake ta tsawaita magana. Sa’ad da yake barci, sai ya fāɗi daga gidan sama a hawa ta uku aka kuma ɗauke shi matacce.
10 Bulus a grji hi, kukru tsra kpama nituma nda maanji ye ni kpama. Mle nda tre, “Du sron mbi na ti meme zan toyi na, a he ni sisren.”
Sai Bulus ya sauka, ya miƙe a kan saurayin ya rungume shi ya ce, “Kada ku damu, yana da rai!”
11 Niki a kma hon hi ni tra u koshu'a nda ka nzi bredi tan. Hu gon wa ala si tre ni ba wu gbro nton ka tsra ni bwu mble, a rju kaba don.
Sai ya koma ɗakin da yake a gidan sama, ya gutsuttsura burodi ya kuma ci. Bayan ya yi magana har gari ya waye, sai ya tafi.
12 Ba nji vren nze'a kma ye ni sisren ma e sron mba a kusi.
Mutanen suka ɗauki saurayin da rai zuwa gida suka kuma ta’azantu ƙwarai da gaske.
13 Kita ngame ki zren guchi ni Bulus nitu jirgi ma, ki dran hi ni Assos, bubu wa kina banzi ki ban Bulus yonji nita. Ana toki me wawu kima ana son ti, nitu ana ya ndi ani hu nkon u meme hi.
Mu kuwa muka ci gaba zuwa jirgin ruwan muka tashi muka nufi Assos inda za mu ɗauki Bulus. Ya yi wannan shirin don zai tafi can da ƙafa.
14 Niwa a zontu nita ni Assos, ki baun yo ni mi jirgi'a ni hi ni Mitylene.
Da ya same mu a Assos, sai muka ɗauke shi a jirgin ruwan muka zo Mitilen.
15 Niki ki dran rhini kima ka ri ni vi wa aka hua, ni bubu wa ata ya nklan meme wu Chios. Ni vi wa ala hu'a, kika yo za ni nklan meme wu Samos, e vi wa aka hu kima, ki ye ri ni kikle gbu Miletus.
Kashegari muka tashi cikin jirgin ruwa daga can muka zo gefen Kiyos. Kwana ɗaya bayan wannan, sai muka ƙetare zuwa Samos, kashegari kuma muka iso Miletus.
16 Nitu Bulus ana banzi ndi ani dran vu Ephesus yba, nitu du wawu na wo nton ni Asia na; a ta sima hi ri ni Urushelima nitu hi tsra ni vi Pentecost, anita bi tiwu toki.
Bulus ya yanke shawara yă wuce Afisa a jirgin ruwa don kada yă ɓata lokaci a lardin Asiya, gama yana sauri yă kai Urushalima, in ya yiwu ma, a ranar Fentekos.
17 Rjini Miletus a ton ndji hi ni Ephesus duba ka yo bi ninkon ekklisiya ye wu.
Daga Miletus, Bulus ya aika zuwa Afisa a kira dattawan ikkilisiya.
18 Niwa ba ye'a, a hla bawu ndi, “Bi yi kimbi bito, rhini vi mumla wa mi yo za ni Asia, niwa chachu mi zi wunton niyi.
Da suka iso, sai ya ce musu, “Kun san irin zaman da na yi tun lokacin da na zauna da ku, daga ranar farkon da na zo cikin lardin Asiya.
19 Mi zi ti ndu Bachi hama ni nzutu mba ni Mashishi, mba ni tsra iya wa ye ni me nitu zon nyu meme wu Yahudawa ba.
Na bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali’u har da hawaye, da gwagwarmaya iri-irin da na sha game da makircin Yahudawa.
20 Bito nitu wa mi na kamu ni dbu bla ni yiwu ko ngye wa ani zoyi na, mba wa mi tsro yi ni shishi ndji wawu mba huyi niko niko,
Kun san cewa ban yi wata-wata yin muku wa’azi game da duk abin da zai amfane ku ba amma na koyar da ku a fili da kuma gida-gida.
21 ni ni vu ni nran ni Yahudawa baba bi Greek nitu kma sron hi ni Irji mba kri ni gbangban sron ni Bachi mbu Yesu.
Na yi shela ga Yahudawa da Hellenawa cewa dole su juye ga Allah cikin tuba su kuma amince da Ubangijinmu Yesu.
22 Zizan ya, mi si hi ni Urushelima, ni gbron Ruhu, nina to kpe wa ani ti nimu niki na,
“Yanzu kuma Ruhu ya tilasta ni, za ni Urushalima, ba tare da sanin abin da zai faru da ni a can ba.
23 hamma wa Ruhu Tsatsra a bwu bla nimu ndi ni gbu kankan wa mi ria, wlo cbo wu lo mba iya ni gben me.
Na dai san cewa a kowace birni Ruhu Mai Tsarki yakan gargaɗe ni cewa kurkuku da shan wuya suna jirana.
24 E me mina ban kpa ivri sisren mu to hi kpe wu tumu na, nitu du mi kle itsu mba ndu wa mi kpa rjini Bachi Yesu, ni du mi bwu nran tre ndindi wa Irji nme wo kpata hama duta ki han kpe.
Amma ni ban ɗauki raina a bakin kome ba, in dai zan iya gama tserena in kuma kammala aikin da Ubangiji Yesu ya ba ni aikin shaida bisharar alherin Allah.
25 Zizan ya, Mito ndi wawu mbi, wa nimi mbi mi zren si dbu hla nitu ikoson Irji, bina la to shishi mu na.
“Yanzu na san cewa ba ko ɗaya daga cikinku wanda na zazzaga ina muku wa’azin mulkin Allah da zai sāke ganina.
26 Nitu kima, mi bwu ni bla yiwu vi wu luwa iyi ndrjo na he ni tumu na.
Saboda haka, ina muku shela a yau cewa ba ni da alhakin kowa a kaina.
27 Nitu mina ka kpe don ni dbu bla wawu kpe wa Irji ni son niyi na.
Gama ban yi wata-wata a sanar muku dukan nufin Allah ba.
28 Nitu kima, bika mla zren ni kpambi, mba ni ba wawu ntma wa Ruhu Tsatsra a yoyi du yi yaba niwu'a. Mla zren ni krju ekklisiya Irji, wa a le ba ni iyi ma. / Nitu du he ndi / ni iyi ma / nha vunvu bi sen bari ba yo ndi / ni iyi wu vren ma
Ku lura da kanku da dukan garken da Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu kula da shi. Ku zama masu kiwon ikkilisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa.
29 Mi toh ndi, mita hi kpamu, meme yawhu bari ni mi mbi ba ye nda na kpa ntma ba chuwo na.
Na san cewa bayan na tafi, mugayen kyarketai za su shigo cikinku ba za su kuwa ƙyale garken ba.
30 Mi to ndi nimi mbi me, ndji bari ba nzulu nda tre kpe bi gbran rhen nitu du ba gbron mriko bihu bari hi ni kpan mba.
Ko cikinku ma mutane za su taso su karkatar da gaskiya don su jawo wa kansu almajirai.
31 Nitu ki bika mla kri. Bika ti mren ndi wu se tra mina don me ni nron yi yiyyri mbi ni mashishi ni chu mba ni irhi.
Saboda haka ku zauna a faɗake! Ku tuna cewa shekara uku, dare da rana ban taɓa fasa yin wa kowannenku gargaɗi ba, har da hawaye.
32 Zizan mi yoyi ni wo Irji mba ni lan tre u wa a kpata, wandi ani to me yi nda nuyi gado nimi biwa ba ngla ba ti tsatsra'a.
“To, yanzu na danƙa ku ga Allah da kuma ga maganar alherinsa, wadda za tă iya gina ku ta kuma ba ku gādo a cikin dukan waɗanda aka tsarkake.
33 Mina ti ngu yo sron nitu azurfa, zinariya ko nklon ndrjo na.
Ban yi ƙyashin azurfa ko zinariya ko tufafin kowa ba.
34 Biyi me bi to ndi iwo mu biyi ba tindu ne kpiwa mi son mba kpison wu bi wa ba he ni me'a.
Ku kanku kun san cewa hannuwan nan nawa sun biya mini bukatuna da kuma na abokan aikina.
35 Ni kpi wawuu, mi bwu nkon tsro yi nitu wa bi zo bi wa bana he ni gbengblen na, ni tindu, mba niwa bi timre ni lantre Bachi Yesu, lan tre wa wawu kima a tre: A zan bi lulu du hu nu ni du hu kpa,”
Cikin kowane abin da na yi, na nuna muku cewa da irin wannan aiki tuƙuru don mu taimaki marasa ƙarfi, muna tunawa da kalmomin da Ubangiji Yesu kansa ya ce, ‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.’”
36 Hu gon tre ma ni nkon yi, a kukwu mgbarju nda bre Irji ni ba wawu mba.
Da ya faɗi haka, ya durƙusa tare da dukansu ya yi addu’a.
37 Ba kuuyi bran nda mankpa Bulus nji nda chiwu bi bi wu sron nyime.
Sai dukansu suka yi kuka suka rungume shi, suka kuma yi masa sumba.
38 Sron mba a ti meme zan nitu wa a tre ndi bana la to shishima ngana. Mle ba huu ka yo ni nkon ni jirgi ma'a.
Abin da ya fi sa su baƙin ciki shi ne maganarsa da ya ce, ba za su ƙara ganin fuskarsa ba. Sai suka raka shi zuwa wajen jirgin ruwa.