< Ndu Manzaniba 19 >
1 Aye he niwa Apollos a he ni Corith, Bulus a zren zu ni kotu gbungblu'a nda ye ri ni kikle gbuwu Ephesus, nda ye toh ba mri ko bari niki.
Lokacin da Afollos yake a Korint, Bulus ya bi hanyar da ta ratsa ta Asiya ya zo Afisa. A can ya sadu da waɗansu almajirai,
2 Bulus a hla bawu ndi, “Bi kpa Ruhu tsatsra niwa bi kpanyime a?” Ba sa niwu ndi, “aan, kina wo nitu Ruhu Tsatsra mena.
sai ya tambaye, su ya ce, “Kun karɓi Ruhu Mai Tsarki sa’ad da kuka gaskata?” Suka amsa suka ce, “A’a, ba mu ma san akwai Ruhu Mai Tsarki ba.”
3 Bulus a tre ndi, “Nimi ngye wa ba ti batisma ni yiwu?” Ba tre ndi, “Ni baptisma wu Yohana.”
Saboda haka Bulus ya yi tambaya ya ce, “To, wace baftisma aka yi muku?” Suka ce, “Baftismar Yohanna.”
4 Niki Bulus a sa ndi, “Yohana a ti batisma wu k'ma sron sran. A hla ni ndji ba ndi du ba kpanyime ni wa ani ye ka huu, wa a hi Yesu.”
Bulus ya ce, “Ai, baftismar Yohanna, baftisma ce ta tuba. Ya ce wa mutane su gaskata a wani wanda yake zuwa bayansa, wato, Yesu.”
5 Niwa ndji ba ba wo toki, ba kpa batisma ni nde Bachi Yesu.
Da ji wannan, sai aka yi musu baftisma a cikin sunan Ubangiji Yesu.
6 Niki, wa Bulus a sawo nitu mba, Ruhu Tsatsra a ku nitu mba, nda duba tre ni lan bari nda bwu tre wu ko shishi si bla.
Da Bulus ya ɗibiya musu hannuwansa, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauka musu, suka kuwa yi magana da harsuna, suka kuma yi annabci.
7 Wawu mba bana mla tsra ndji wlon don ha (tso).
Mutane kuwa su wajen mutum goma sha biyu ne.
8 Bulus a ri hi ni sinagog nda ka tre ni gbengblen sron, wu wha tra, shle vu si ya nda nhron ba nitu ngbran ko Irji.
Bulus ya shiga majami’a ya yi magana gabagadi a can na watanni uku, yana muhawwara yana kuma rinjayarsu game da mulkin Allah.
9 E niwa Yahudawa bari ba lo sron zi gbangban nda kamba ni shishi kpaa ndji ba. Niki Bulus a kaa ba don nda chu mriko bari hu nji ni kpama, nda ka vu bla siya ba baa ni ba ni tra wu zontu bi u Tyrannus.
Amma waɗansunsu suka taurara; suka ƙi su gaskata kuma a gaban jama’a suka yi baƙar magana game da Hanyar. Bulus kuwa ya bar su. Ya tafi tare da almajirai ya dinga tattaunawa da su kullum a babban ɗakin jawabi na Tirannus.
10 A si he toki ka tsra se ha, nitu ki wawu mba wa ba kii ni Asia, ba wo lan tre Bachi, ni Yahudawa baba Greek ba.
Wannan ya ci gaba har shekara biyu, sai da ya sa dukan Yahudawa da Hellenawa da suke zaune a lardin Asiya suka ji maganar Ubangiji.
11 Irji a sia ti kikle kpi wa bana ri he wu toh ni son mba, ni wo Bulus.
Allah ya yi ayyukan banmamakin da suka wuce misali ta hannu Bulus,
12 Nitu kii, ngbanjan nklon wu wo mba nklon wu kaa nne wa ana sa wo ni wu ba ban ba ka nubi lilo, i lilo mba a bwa hi don ba e brji ba ba rju don kpamba.
har ma ana kai hankicif da adikan da suka taɓa jikinsa wa marasa lafiya, suka kuwa warke daga cututtukansu mugayen ruhohi kuma suka rabu da su.
13 E Yahudawa bi zu brji rju ni kpa ndji bari ba sia zren zu ni ngbran kima. Ba yo nde BAchi Yesu ni du nuba gbengblen nitu meme brji niwa ba tre ndi, “Ni nde Yesu wa Bulus a dbu hla, mi mha yiyo, rju yi.”
Waɗansu Yahudawa masu yawo gari-gari suna fitar da mugayen ruhohi suka yi ƙoƙari su yi amfani da sunan Ubangiji Yesu a kan waɗanda suke da aljanu. Suna cewa, “A cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa’azi, na umarce ku, ku fito.”
14 Ninkon Prist wu Yahudawa, wa ndema ana Sceva, a he ni mri tangban wa basia ti toyi.
’Ya’ya bakwai maza na Sikeba, wani babban firist na Yahudawa, suna yin haka.
15 Meme brji a sa bawu ndi, “Yesu mi to, mba Bulus mi to, i wu hi nha?”
Wata rana mugun ruhu ya amsa musu ya ce, “Yesu kam na sani, Bulus kuma na sani, amma ku kuma su wane ne?”
16 Meme brji ni mi igu; a a doo lu hon nitu bi zu brji rju'a nda zan ba ni gbengble, nda hloba tsi. Mle ba yotsu rju ni ko'a ni ngbre mba ni nkpan kpa.
Sai mutumin da yake da mugun ruhun ya fāɗa musu ya sha ƙarfinsu duka. Ya yi musu dūkan tsiya har suka fita a guje daga gidan tsirara jini yana zuba.
17 Ikpe yi a ri ton ndji wawu, Yahudawa baba Greeks, wa ba ki ni Ephesus. Sissri a vu ba, u nde Bachi Yesu a nzu hon.
Da Yahudawa da Hellenawan da suke zama a Afisa suka ji wannan labari sai duk tsoro ya kama su, aka kuwa darjanta sunan Ubangiji Yesu ƙwarai.
18 Niki ngame, gbugbu biwa ba kpanyime'a, ba rju ye nran nda vu bla meme kpi wa bana ti yea.
Da yawa cikin waɗanda suka gaskata yanzu suka zo a fili suka furta mugayen ayyukansu.
19 Gbugbu biwa bata ti gbugblu ba ni vunvu mba rju ye sru ni buburi nda goon ba ni shishi ko nha. Niwa ba bla nklen kpi ba, ana dubu se ton wu whlo azurfa.
Waɗansu masu yin sihiri suka kawo naɗaɗɗun littattafansu wuri ɗaya suka kuwa ƙone su a gaban jama’a. Sa’ad da aka lissafta yawan kuɗin naɗaɗɗun littattafan nan, sai jimillar ta kai darik dubu hamsin.
20 Niki lan tre wu Bachi a zren kagon gbagban ni gbengblen.
Ta haka maganar Ubangiji ta bazu ko’ina ta kuma yi ƙarfi.
21 Zizan, hu gon wa Bulus a kle ndu ma ni Ephesus, a yo sron, hu ni gbron Ruhu, nda zren zu ni Macedonia mba Achaia ni nkon ma wu hi ni Urushelima; a tre nde, “Mita ka ri niki, mi hi to Rome ngame.”
Bayan dukan wannan ya faru, sai Bulus ya yanke shawara ya ratsa Makidoniya da Akayya in za shi Urushalima. Ya kuma ce, “Bayan na tafi can, dole in ziyarci Roma ita ma.”
22 Bulus a ton hi ni Macedonia, ha nimi biwa ba ti ndu niwu, Timoti mba Erastus. E wawu kima a son zu wu ton fii ni Asia.
Sai ya aiki biyu daga cikin masu taimakonsa, Timoti da Erastus, zuwa Makidoniya, yayinda shi kuwa ya ɗan dakata a lardin Asiya.
23 Mla tsra ni ton kima, iya wa ana fiime na a lu ni Ephesus nitu nko'a.
Kusan wannan lokaci sai aka yi wani babban hargitsi game da wannan Hanyar.
24 Ndji wu la azurfa ri ni nde Demetius, wa ata la gunki u Artemis ni azurfa, nda ta nji ndu nklen gbugbu ye ni bi laaba.
Wani maƙerin azurfa, mai suna Demetiriyus wanda yake ƙera siffar ɗakunan tsafin Artemis da azurfa, ba ƙaramin ciniki yake kawo wa mutane masu sana’an nan ba.
25 Niki a yo bi ndu kima zi nda tre ndi, “Indji mbu, bito ndi ninkon du mbuyi, nklen ni ri bran.
Sai ya tara su wuri ɗaya, tare da masu irin wannan sana’ar ya ce, “Ku jama’a, kun san muna samun kuɗin shiga sosai daga wannan sana’a.
26 Bi to ndi ni wo ndi, ana ni Ephesus megen na, hu mla ngban gbungblu Asia wawu, Bulus yi, a kma sron ndji gbugbu sran. Ani bla ndi mri irji wa iwo ndji ba laa ba na Irji na.
Kuma kuna ji kuna gani yadda Bulus ɗin nan ya shawo kan mutane da yawa ya kuma sa suka bauɗe a nan a Afisa da dukan lardin Asiya. Yana cewa alloli da mutum ya ƙera ba alloli ba ne ko kaɗan.
27 Ana nitu andi kikle iya wa a ni du ndu mbu kle na, iko kikle irji wu artemis me ni rjoku ni nzohonma ngame. Niki, gbengblen Artemis ani grji, wawu wa Asia mba gbungblu meme wawu ba kukru ni nzuhon.”
Akwai hatsari, ba kawai cewa sana’armu za tă rasa sunanta mai daraja ba, amma za a yi banza da ɗakin tsafin Artemis alliyarmu mai girma, alliyar kanta wadda ake bauta a ko’ina a yankin Asiya da kuma duniya, za a raba ta da darajarta.”
28 Niwa ba wo toki, ndu a shu sron mba, eba kpa gro ndani tre ndi, “Kikle Artemis wu Ephesus.”
Da suka ji haka, sai suka yi fushi ƙwarai suka fara ihu suna cewa, “Girma ta tabbata ga Artemis ta Afisawa!”
29 Kikle gbu'a wawu a tsi shishi, e ndji ba wawu ba vra tsu ni sron ri hi ni ko wu son mba (theatre). Bana vu kpukpan bi zren Bulus ye, Gaius mba Aristarchus, wa ba ye rhini Macedonia.
Jim kaɗan sai hayaniya ta tashi a dukan birnin. Sai mutane suka cafke Gayus da Aristarkus, abokan tafiyar Bulus daga Makidoniya, suka ruga da zuwa fili da nufi ɗaya.
30 Bulus a ta son ri nimi kpaa ndji ba, e mri ko ba ba zuu.
Bulus ya so ya bayyana a gaban taron, amma almajirai ba su bar shi ba.
31 Ngame, bari wa bana bi ninkon du ni ngrji Asia, wa bana kpanma, ba tondu hi wu ni bre ni duna ri ni tra son (theatre) na.
Har waɗansu shugabannin lardin ma, abokan Bulus, suka aika masa suna roƙonsa kada yă kuskura ya shiga filin nan.
32 Ndji bari ba sia ti gro kperi, e bari ikpe nkan, nitu tsi shishi a vu kpaa ndji ba. Gbugbu mba bana to ka a hi ngye si zren nda duba ye zontu ki na.
Taron kuwa ya ruɗe. Waɗansu suna ihu suna ce abu kaza, waɗansu kuma wani abu dabam. Yawancin mutane kuma ba su ma san abin da ya sa suke a wurin ba.
33 Bari ni kpaa mba ba nron Alexanda, wa Yahudawa ba ba tru yo ni shishi, niki Alexanda a ti ba niwo, nitu a ta son yo tre wu ya ni soon mba.
Yahudawa suka tura Alekzanda gaba, sai waɗansu a taron suka riƙa yin masa ihu. Sai ya ɗaga hannu don a yi shiru don yă kāre kansa a gaban mutane.
34 Niwa ba mla to ndi a hi ndji Yahudawa, ba lu yra gro wu ton mla bla ha ni lan riri, ndani hla ndi, “KikleArtemis wu Ephesus.”
Amma sa’ad da suka gane shi mutumin Yahuda ne, sai duk suka yi ihu gaba ɗaya na kusa sa’a biyu, suna cewa, “Girma ta tabbata ga Artemis ta Afisawa!”
35 Niwa ndji wu nha (town clerk) wu gbu'a a du kpaa ndji ba kma ti gbangbi, a tre ndji, “Biyi ndji bi Ephesus, ahi ndji nha wa ana to ndi kikle gbu wu Ephesus yi hi bubu ko wu son wu kikle Artemis, mba iwhiwa grji ku rji ni shulu na?
Sai magatakardar birnin ya sa taron su yi shiru, sa’an nan ya ce, “Mutanen Afisa, ashe duk duniya ba tă san cewa birnin Afisa ce mai lura da haikalin Artemis mai girma da kuma siffarta da ya fāɗi daga sama ba?
36 Bita to ndi kpi biyi bana wu kpa tron na, bika ti wiime ni na kpati vravra mena.
Saboda haka, da yake ba dama a yi mūsun wannan gaskiya, ya kamata ku natsu kada ku yi kome da garaje.
37 Nitu bi nji ndji biyi ye ni shishi ko gaa tre, ana ndji ba bi y'bi iko bre mbi ka bi kpa nde mri Irji mbi ti meme na.
Kun kawo mutanen nan a nan, gashi kuwa ba su yi fashin haikali ba, ba su kuwa saɓa wa alliyarmu ba.
38 Nitu ki, Dimetrius baba bi ndu la wa ba he niwu'a ba he ni tre wu lo nitu ndrjo, tra wu gaa tre a he ni who mba bi wa bawoba nda gaatre'a. Du ba tsra kpa mba.
To, in haka ne, in Demetiriyus da abokan sana’arsa suna da wata magana game da wani ai, kotuna suna nan a buɗe, akwai kuma muƙaddasai. Suna iya kai ƙara.
39 Bita ni wato kpe nkan, kima ki vu ya ni son yi ni mla ti.
In kuma akwai wani abu har yanzu da kuke so ku kawo, dole a daidaita shi a majalisa.
40 A hi njanji ki he ni ya wu lo bata vuta nitu kma gbu srantu wu vi luwa. Kina he ni kpe wu kaatu nitu kpa gbu tsi wu luwa na, e kina to nkon wu chutu rju na.”
Yadda yake a yanzu, muna a hatsarin amsa zargin ta da hargitsi saboda abin da ya faru yau. Da yake ba za mu iya ba da dalilin da ya sa aka yi wannan hargitsi ba.”
41 Niwa a kle tre toyi, a kaa son a nda du ndji ba shan hi.
Bayan da ya faɗi haka, sai ya sallami taron.