< Ndu Manzaniba 18 >
1 Hu gon kpi biyi, Bulus a rju rji ni Athens nda hi ni Corinth.
Bayan haka, Bulus ya bar Atens ya tafi Korint.
2 Niki a ka zontu ni ndji Yahudawa ri wa ba yo ndi Akwila, ndi wu ngrji Pontus, wa la ren mayi a ye rhini Itali mba wama Pricila, nitu Claudius a yo doka du Yahudawa du ba rju ni Rome. Bulus a hi niba,
A can ya sadu da wani mutumin Yahuda mai suna Akwila, ɗan garin Fontus, wanda ya je can ba da daɗewa ba daga Italiya tare da matarsa Firiskila, gama Kalaudiyus ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya tafi yă gan su,
3 nitu wa bata ti bibi ndu son ni gbungblu riri niwu, a son niba nda sia ti ndu'a, bana bi tsro bru ni tent.
da yake shi ma mai ɗinkin tenti ne kamar su, sai ya zauna ya yi aiki tare da su.
4 Niki Bulus a son zi shle bla ni sinagog chachu ni vi Sati (Sabbath), nda ni gbron mren Yahudawa baba Greek ba.
Kowace Asabbaci kuwa yakan yi muhawwara a majami’a, yana ƙoƙari yă rinjayi Yahudawa da Hellenawa.
5 Zizan niwa Sila mba Timoti ba grji ye ni Macedonia, Bulus a ka yo sron ma yo ngbangban ni lan tre'a, nda ni bwu hla ni Yahudawa ba ndi Yesu yi hi Kristi.
Sa’ad da Sila da Timoti suka iso daga Makidoniya, sai Bulus ya ba da kansa ga yin wa’azi kaɗai, yana tabbatar wa Yahudawa cewa Yesu shi ne Kiristi.
6 Niki wa Yahudawa ba ba lu hon wu nda mren u, Bulus a kpon nklon kpama ni bawu nda hla bawu ndi, “Du iyi mbi he ni tu mbi, mi ngla wo mu rju, rji zizan mi hini bi kora'a.”
Amma sa’ad da Yahudawa suka yi hamayya da Bulus suka kuma shiga zaginsa, sai ya karkaɗe tufafinsa a cikin rashin yarda, ya ce musu, “Alhakinku yana a kanku! Ba ni da wani laifi. Daga yanzu zan tafi wajen Al’ummai.”
7 Mle arju don bubuki nda hi ni ko Titiyus Justus, ndi wa a ta hu nkon bre Irji. Ikoma a na he hu nha ni sinagog.
Sai Bulus ya bar majami’ar ya kuma tafi ƙofar da take kusa da gidan Titus Yustus, mai yi wa Allah sujada.
8 Crispus, ninkon Sinagog a, kpanyime ni Bachi, ni bi koma wawu mba, baba gbugbu ndji bi Korintiya wa ba wo nda kpanyime, ba ti batisma ni bawu.
Kirisbus, shugaban majami’a, da dukan iyalinsa suka gaskata Ubangiji; Korintiyawa masu yawa kuwa da suka ji shi suka gaskata, aka kuwa yi musu baftisma.
9 Bachi a hla ni Bulus ni chu nimi ra, “Na ti sissri na, si tre rju nina son gbangbi na.
Wata rana da dad dare, Ubangiji ya yi magana da Bulus a cikin wahayi ya ce, “Kada ka ji tsoro; ka ci gaba da yin magana, kada ka yi shiru.
10 Nitu mi he ni wu, ndrori na wa ti kpe meme ni wu na. mi he ni gbugbuwu ndji ni mi kikle gbu yi.”
Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.”
11 Bulus a son niki ti ise ri ni wha tanne, nda ni tsro lan tre Irji ni mimba.
Saboda haka Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da rabi, yana koya musu maganar Allah.
12 Niki wa Gallio a hon son ni ruron gomna wu Achaya, Yahudawa ba ba lu ni mren sron ri wu kiamba ni Bulus, nda vuu ye shishi bi gaa tre;
Yayinda Galliyo yake muƙaddas Akayya, Yahudawa suka haɗa kai suka tasar wa Bulus, suka kuwa kawo shi cikin kotu.
13 ba tre ndi, “Igu yi kma sron ndji ba duba hu nkon bre Irji nkan ni wa doka hla.”
Suka yi zarge cewa, “Wannan mutum yana rarrashin mutane su yi wa Allah sujada a hanyoyin da suka saɓa wa doka.”
14 Kima me, niwa Bulus a taa bwu tre ma, Gallio a tre ni Yahudawa ba ndi, “Biyi Yahudawa, a nita nitu meme ko gbirjerje la tre, ani he nitu nkon mi wo yi.
A daidai sa’ad da Bulus yana shirin yin magana, sai Galliyo ya ce wa Yahudawan, “Da a ce ku Yahudawa kuna gunaguni game da munafunci, ko kuma wani babban laifi, da sai in iya sauraronku.
15 Nitu wa a he nitu lan tre baba ba nde ni doka mbi, hi ki ni mla kpa mbi ti kimbi. Mina son ri ni gaa tre ikpi biyii na.”
Amma da yake ya shafi gardama ce game da kalmomi da sunaye da kuma dokarku, sai ku ji da ita da kanku. Ni ba zan zama mai shari’a kan irin waɗannan abubuwa ba.”
16 Gallio a duba rju dinkon ni ruron gaatre'a.
Saboda haka ya kore su.
17 Niki ba lu vu sosthenes, ninkon sinagog nda hlo tsi ni shishi ruron wu gaatre'a. E Gallio ana yo sron ni kpe wa ba tia na.
Sai duk suka juya kan Sostenes shugaban majami’a suka yi masa dūka a gaban kotun. Amma Galliyo ko yă kula.
18 Bulus, hu gon son niki wu vi gbugbu bari, a lu don mri vayi ba nda dran hi ni Syria baba Priscilla mba Akwila. Niwa a rhihe kunkon rhini bubu ri ni jirgi ma wu Cenchrea, a duba kron nfutu ma rju mpempen nitu shirji wa a baan.
Bulus kuwa ya ci gaba da zama a Korint na’yan kwanaki. Sa’an nan ya bar’yan’uwa ya shiga jirgin ruwa zuwa Suriya tare da Firiskila da Akwila. Kafin ya tashi, ya aske kansa a Kenkireya saboda alkawarin da ya yi.
19 Niwa ba ye ri ni Ephesus, Bulus a kaaba Priscilla mba Aquila don niki, e wawu kima a ri hi ni mi sinagog nda ka si shleniya baba Yahudawa ba.
Suka isa Afisa, inda Bulus ya bar Firiskila da Akwila. Shi kansa ya shiga majami’a ya kuma yi muhawwara da Yahudawa.
20 Niwa ba mye Bulus du son gbaa nha, a kama.
Sa’ad da suka roƙe shi ya ƙara’yan kwanaki da su, bai yarda ba.
21 Ni lu bre nda ni donba, a tre ndi, “Mila kma ye ngari, Irji nita kpanyime.” A dran nitu jirgi mma rhiki hi ni Ephesus.
Amma da yake barin wurin, ya yi alkawari cewa, “Zan dawo in Allah ya yarda.” Sa’an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa.
22 Niwa Bulus a ye grji ni Caesarea, a hon hi ka chi ekklisiya wu Urushelima nda grji hi ni Antioch.
Sa’ad da ya sauka a Kaisariya, sai ya haura ya gai da ikkilisiya sa’an nan ya gangara zuwa Antiyok.
23 Hu gon fon son niki, Bulus rju kuunkon zren zu ni gbungblu Galatia mba Phrygia, nda ni nhron mri ko ba du ba kri gbangban.
Bayan ya yi’yan kwanaki a Antiyok, Bulus ya tashi daga can ya zaga ko’ina a yankin Galatiya da Firjiya, yana ƙarfafa dukan almajirai.
24 Niki, Yahudawa ri ni nde Apollos, wa ba ngrjiwu ni Alexandria, a ye ni Ehpesus. A he ni lantre ndindi wu tre nda ni mla toh vunvu tre Irji.
Ana cikin haka sai wani mutumin Yahuda mai suna Afollos, ɗan ƙasar Alekzandariya, ya zo Afisa. Shi masani ne, yana da cikakken sani na Nassosi.
25 Apollos ana kpa tsro ndindi ni tsro tre Bachi, nitu wa a ta kri gbangban ni dri, a tre nda tsro ni nkon tsatsra kpi nitu Yesu, e nda to nitu batisma wu Yohana megen.
An horar da shi a hanyar Ubangiji, ya kuma himma ƙwarai a magana, ya kuma yi koyarwa game da Yesu, daidai, ko da yake baftismar Yohanna ce kaɗai ya sani.
26 Apollos a lu kri si tre ni gbengblen sron ni mi sinagog. Niwa Priscilla mba Aquila ba woowu, ba yo ye ni kosan nda mla bla niwu, nkon wu Irji.
Sai ya fara magana gabagadi a majami’a. Sa’ad da Firiskila da Akwila suka ji shi, sai suka gayyace shi gidansu suka ƙara bayyana masa hanyar Allah sosai.
27 Niwa a ta son vu yba hi ni Achaia, mri vayi ba ba nhron nda nha vunvu ni mriko bi Achaia ndi du ba kpaa ni wo ha. Niwa a ka riki, a zo ni nkon gbugbuwu biwa ba kpanyime, nita a kpaba hamma ni duba ti kpe.
Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata.
28 Apollos a kri gbangban ni sen nyu ni Yahudawa ba nda tsro ba rhi ni vunvu Irji ndi Yesu yi hi Kristi.
Gama da ƙwazo ya ƙaryata Yahudawa a muhawwara a fili, yana tabbatar daga Nassosi cewa Yesu shi ne Kiristi.