< Ndu Manzaniba 15 >

1 Indji bari ba grji rji ni Judiya ye ni Antioch nda ye bla tsro ni mri vayi ba ndi, “Bi tina duba han mbru ni yiwu hu njo tre Musa na, bina kpa chuchuwo na.
Wadansu mutane suka zo daga Yahudiya suka koyar da 'yan'uwa, cewa, “Idan ba yi maku kaciya bisa ga al'addar Musa ba, ba za ku sami ceto ba.”
2 Kpeyi a vu tu Bulus mba Barnaba zon ti nkan nda duba kri senyu ni ba. Niki, Bulus mba Barnaba, baba bari ni mi mba, ba chuba ndi duba hon hi ni Urushelima nda yi son ni ba manzani baba bi ninkon ba nitu duba tu tre'a.
Da Bulus da Barnaba suka tunkare su da mahawara, sai 'yan'uwa suka yanke shawara Bulus da Barnaba da wasu su je Urushalima wurin manzanni da dattawa a kan wannan magana.
3 Nitu ki, niwa ekklisiya a ton ba'a, ba zren zu ni Phoenicia mba Samaria, nda si bwu bla sran sron wa bi kora'a ba kpa'a. Ba nji ngyiri kpukpome ye ni mri vayi ba.
Da shike iklisiya ce ta aike su, sai suka bi ta Finikiya da ta Samariya suka sanar da tuban al'ummai. Ya kawo murna mai yawa a wurin 'yan'uwa.
4 Niwa ba ye rini Urushelima, ekklisiya mba manzaniba baba bi ninkon ba ba kpaba ni wo ha, i baka vu kpi wa Irji a ti bawu'a bla ni bawu.
Bayan sun zo Urushalima, sai iklisiya da manzanni da dattawa, suka marabce su, sai suka fada masu abin da Allah ya yi ta wurinsu.
5 Ama ndji bari, ni mi biwa ba kpanyeme'a, wa bahe ni mi grji bi Pharisee, ba lu kri nda tre ndi, “Ani kpe wuti ni duba vu ba han mbru nda yo tre gbangban ni bawu duba hu tre doka Musa.”
Amma wadansu mutane wadanda suka ba da gaskiya daga cikin Farisawa, suka tashi suka ce, “Dole ne a yi masu kaciya a kuma umarce su su kiyaye dokar Musa.”
6 Niki manzaniba baba bi ninkon ba ba zontu ki nitu duba mla kpeyi yato.
Sai manzanin da dattawan suka taru don su duba wannan lamari.
7 Hu gon sen nyu ni kpamba, Bitrus a lu kri nda tre niba ndi, mri vayi, bito ndi, ni nton ndindi wa aka hi ye'a, Irji a chu ni mi mbi, nitu ni nyu mu, Bi kora ba duba wo lantre wu tre ndindi'a, nda kpanyeme.
Bayan mahawara mai tsanani, sai Bitrus ya tashi ya ce masu, “'Yan'uwa, kun san lokacin baya da ya wuce, Allah ya yi zabi a cikinku, cewa ta bakina ne al'ummai za su ji bishara, su kuma ba da gaskiya.
8 Irji, wa ato dri'a a mla bla ni bawu niwa a nuba Ruhu Tsatsra, toh waa ati nitawu;
Allah, wanda ya san zuciya, ya yi masu shaida, ya kuma basu Ruhu Mai Tsarki kamar yadda ya yi mana;
9 ndana chuta ti nkan ni ba na, niwa a vu sron mba se ni toh kri gbangban.
kuma bai bambanta mu da su ba, ya tsabtace zuciyarsu ta wurin bangaskiya.
10 Zizan nitu ki, ahi ngye duyi ni tsra Irji, niwa bi klo ilo wu ya nitu nkanto wu bi hu'a wa ba timbu, ni kita kina mla to ba nji na'a?
To, saboda haka don me kuke gwada Allah, kuna sa wa almajirai nauyi a wuya wanda ubanninmu duk da mu ba mu iya dauka ba?
11 Ama ki kpanyeme ndi ki kpachuwo nitu ya ndindi wu Bachi Yesu, na baba me.”
Amma mun gaskanta za mu samu ceto ta wurin alherin Ubangiji Yesu, kamar yadda suke.”
12 Kpaandji ba wawu ba ki ni gbangbi niwa ba si sren ton ni ndu wu bwu ya mba wu kanyu yo ni w'ho wa Barnaba mba Bulus ba vu si bla nitu wa Irji a ti ndu ni mi Bi kora'a, zuni wo mba.
Dukan taron jama'ar suka yi shiru sa'adda suke sauraron sakon shaidar da mamakin abin da Allah ya yi ta wurin Bulus da Barnaba a cikin al'ummai.
13 Hu gon wa ba tre kle'a, Yakubu a saa nda ni tre ndi, “Mri vayi, yo ton ndi wome.
Bayan sun gama magana, Yakubu ya amsa, ya ce, “'Yan'uwa, ku ji ni.
14 Siman a hla yiwu niwa Irji ni ya ndindi ma ni mumla azo bi kora'a nitu du ban rhi ni ba, ndji wu ndema.
Saminu ya fada yadda Allah ya fara nuna jinkai ga al'ummai domin ya dauke jama'a daga cikinsu domin sunansa.
15 Lantre ba anabawa a kpanyme ni kii, na wa ba nha'a.
Maganar annabawa ta yarda da wannan, kamar yadda yake a rubuce,
16 Hu gon kpi biyi, mi k'ma ye, mba miye mme ngari, ko wu zontu ni Irji wu Dauda, wa a zilhe ye; Mi nzu sazi, ni du wron meme ma du k'ma ye to ana he,
'Bayan wadannan abubuwa zan dawo, zan gina gidan Dauda wanda ya fadi kasa; in sake gina bangonsa, in tsayar da shi,
17 ni du mbru ndji wa ba don'a, duba wato Bachi, baba wawu bi kora wa ba yo ba ni ndemu.'
saboda sauran jama'a su nemi fuskar Ubangiji, har da al'ummai da ake kira da sunana.
18 Ikpe yi yi Bachi a tre ndi, A nhati kpi biyi wa bato rhi ni sen'a? / Nk'ma vunvu wu Greek bi sen wa ba he ni tu tre wandi a nkan / Ikpe yiyi wa Bachi a tre, ni tuma yi, ba toh wawu kpi wa ba ti nisen. (aiōn g165)
Wannan shine abin da Ubangiji ya fadi, shi wanda ya yi wadannan abubuwa da aka sani tun zamanin da. (aiōn g165)
19 Nitu kima, mi ban zi ndi kina ti ba ya na, baba bi kora wa ba k'ma ye ni Irji.
Saboda haka, a gani na kada mu matsa wa al'umman da suka juyo gun Allah;
20 Ama ki nhahi ni bawu ndi a tre wa s tsra, duba chukpa mba ti nkan ni kpa ti meme gunki, wrhuni hu mba mba ni nn'ma wa ba wuu ba ndwuto, mba rhini iyi.
amma zamu rubuta masu da cewa, su guje wa gumaka da zina da faskanci da maye da cin mushe.
21 Nitu Musa, ba d'buhla ni gbu nkankan, rhini k'ba bi sen, a ye ni zizan wa basi bla nimi Synagogue chachu ni vi Sabbath.”
Tun zamanin da akwai mutane a kowanne birni wadanda suke wa'azi da karatun Musa a majami'u kowanne Asabaci.”
22 Niki a bi ya ni manzaniba baba bi ninkon ba, mba ekklisiya wawu, duba chu Juda wa ba yo ndi Barsabbas, mba Sila, wa bana bi ninkon wu bi vayi ba, nda ton ba hi ni Antioch baba Bulus mba BArnaba.
Sai ya yi wa manzanin kyau su da dattawa da dukan iklisiyar su zabi Yahuza da Barnaba da Sila da dattawan iklisiya a tura su Antakiya tare da Bulus da Barnaba.
23 Nha zuni wo mba, “Rhini manzani baba bi ninkon ba, mri vayi mbi, hini mri vayi bi kora nimi Antioch, Syria mba Cilicia ki chi yi!
Sai suka rubuta wasika, “Manzani da dattawa da 'yan'uwa zuwa ga al'ummai 'yan'uwa a Antakiya da Suriya da Kilikiya, gaisuwa mai yawa.
24 Nitu ki wo ndi ndji bari ba rhunita hama ni kpanyime mbu, nda ka si chonyi ni lan tre wa a kpa sron mbi ti meme'a.
Mun ji cewa wasu mutane daga cikinmu wadanda ba mu umarce su ba, sun fita daga cikinmu sun yi maku koyarwar da ta daga maku hankali.
25 A bi ya nitawu, wa ki k'ma sron mbu yo ni bubu riri, ndi chu ndji biyi wa ki tonba ye ni yi baba mri vayi bi mlason mbu, Barnaba mba Bulus,
Ya yi kyau da dukanmu, muka amince mu zabi wadansu mutane mu tura su wurinku tare da Bulus da Barnaba,
26 ndji biwa ba ban tu yo ni nkon qu nitu nde wu Bachi Yesu Kristi.
mutane wadanda suka sadaukar da ransu domin sunan Ubangiji Yesu Almasihu.
27 Nitu ki, ki ton Juda mba Sila, Wa ba vu bla ni yiwu, kpi biyi ngame ni lantre mba.
Mun aika Yahuza da Sila su gaya maku wadannan abubuwa.
28 Nitu a ya bi ni Ruhu Tsatsra mba ni tawu, du kina la ban ndu ya sa nha nitu mbi zan wa a he toki ye:
Saboda haka ya yi kyau Ruhu Mai Tsarki da mu, kada mu sa maku nauyi fiye da wadannan abubuwan:
29 ndi du yi chuwo rjuni kpi wa ba ton ni brji, ni iyi, kpi wa ba wuu ni ndwu to, mba rhini latre wamba ko lilon. Bita chu kpambi wru ni kpi biyi, zren ni bi yiwu. gbuchu.
ku bar yi wa gumaka hadaya, ku bar cin mushe da shan kayan maye da zina da faskanci, in kun kiyaye wadannan abubuwa za ku zauna lafiya. Ku huta lafiya.”
30 Niki, niwa ba kle nda yo ba ninkon, ba zren grji hi ni Antioch, hu gon wa ba vu gbu ndji ba zontu zi bubu riri, ba ka vunvu wa ba nha bawu nuba.
Da aka sallame su, sai suka je Antakiya. Bayan sun tara jama'a sai suka ba su wasikar.
31 Niwa ba bwu bla, ba ta kpe nitu nron tre wa ba kpa'a.
Bayan da suka karanta ta, sai suka yi murna sosai saboda karfafawa.
32 Juda mba Sila, wa bana anabawa ngame, nronba mri vayi ba ni lan tre gbugbuwu nda zoba kri gbangban.
Yahuza da Sila, da shike su annabawa ne, suka karfafa 'yan'uwa da kalmomi masu yawa.
33 Hu gon wa ba fon ki niki, ba tru ba hi ni si sran rhini mri vayi ba hi ni biwa bana ton ba'a.
Bayan sun yi kwananki a wurin, sai aka sallame su zuwa wurin 'yan'uwa wadanda suka aiko su.
34 Vunvu wu bi zan, bi son bana he ni nklan 34 na (Ya Ndu Man.15:40). Ama a toh bi du Sila du k'ma son niki.
Amma ya gamshe Sila ya zauna a wurin.
35 Ama Bulus mba Barnaba ba kii ni Antioch ndani tsro nda ni bla (baba gbugbu bari) lan tre wu Bachi.
Amma Bulus da Barnaba suka tsaya a Antakiya da sauran 'yan'uwa, suna koyar da maganar Ubangiji.
36 Hu gon vi bari, Bulus a hla ni Barnaba, “Ki k'ma hi zizan ni ki hi tsri ni mri vayi bi gbu wa kina ka d'bu hla lantre Bachi, niki toh ka ba heni ha.”
Bayan kwanaki kadan Bulus ya ce ma Barnaba, “Mu koma yanzu mu ziyarci dukan 'yan'uwa da muka yi masu bisharar Ubangiji, mu ga yadda suke.
37 Barnaba a son ban Yohana wa ba yondi Markus, nji nha.
Barnaba yana so su dauki Yahaya wanda kuma ake kira Markus.
38 Ama Bulus a rhimren ndi ana bi du ba ban Markus na, waa ana kaa ba don ni Pamphylia nda na la huba ni ndu'a na.
Amma Bulus ya yi tunanin bai kamata a tafi da Markus ba, tun da ya bar su a Bamfiliya bai ci gaba da su ba.
39 Niki, kikle sen nyu a gaaba nda du ba hu nkon nkankan ni kpamba, i Barnaba a ban Markus hu ni kpama, nda dran rju hi ni Cyprus.
Nan jayayya ta tashi tsakaninsu, har suka rabu da juna sai Barnaba ya tafi tare da Markus suka ketare zuwa Kuburus.
40 Ama Bulus a chu Sila nda rju kunkon hi, hu wa mri vayi ba ba vu ba sru ni nji ndindi wu Bachi.
Amma Bulus ya zabi Sila suka tafi, bayan 'yan'uwa sun yi masu addu'ar alherin Allah ya kiyaye su.
41 Mle a zren zu ni Syria mba Cilicia ndani gbre kri gbangban ni ekklisiya ba.
Bulus ya tafi ya zazzaga Suriya da Kilikiya yana ta karfafa iklisiyoyin.

< Ndu Manzaniba 15 >